< 1 Sarakuna 11 >
1 Sarki Solomon ya ƙaunaci baƙin mata. Ban da’yar Fir’auna, ya auri Mowabawa, Ammonawa, mutanen Edom, Sidoniyawa da Hittiyawa.
Or, le roi Salomon aima plusieurs femmes étrangères, outre la fille de Pharaon: des Moabites, des Ammonites, des Iduméennes, des Sidoniennes et des Héthiennes,
2 Sun fito daga al’ummai da Ubangiji ya ce wa Isra’ilawa, “Kada ku yi aurayya da su, domin tabbatacce za su juye zukatanku zuwa ga waɗansu alloli.” Duk da haka Solomon ya manne musu, ya nace, yana ƙaunarsu.
D'entre les nations dont l'Éternel avait dit aux enfants d'Israël: Vous n'irez point chez elles, et elles ne viendront point chez vous; certaine-ment elles détourneraient votre cœur pour suivre leurs dieux. Salomon s'attacha à ces nations par l'amour.
3 Ya auri mata ɗari bakwai, haifaffun gidan sarauta, da kuma ƙwarƙwarai ɗari uku. Matan nan nasa suka karkatar da shi.
Il eut donc pour femmes sept cents princesses, et trois cents concubines; et ses femmes détournèrent son cœur.
4 Yayinda Solomon yake tsufa, matansa suka juye zuciyarsa ga bin waɗansu alloli, zuciyarsa kuwa ba tă bi Ubangiji Allahnsa ɗungum kamar yadda zuciyar Dawuda mahaifinsa ta kasance ba.
Et il arriva, au temps de la vieillesse de Salomon, que ses femmes détournèrent son cœur après d'autres dieux; et son cœur ne fut pas intègre avec l'Éternel son Dieu, comme le cœur de David, son père.
5 Ya bi Ashtarot, alliyar Sidoniyawa, da Molek, allahn da aka hana na Ammonawa.
Et Salomon suivit Astarté, divinité des Sidoniens, et Milcom, l'abomination des Ammonites.
6 Saboda haka Solomon ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji. Bai bi Ubangiji gaba ɗaya kamar yadda Dawuda mahaifinsa ya yi ba.
Ainsi Salomon fit ce qui est mal aux yeux de l'Éternel, et il ne suivit pas pleinement l'Éternel, comme David, son père.
7 A kan tudu, gabas da Urushalima, Solomon ya gina masujada a can domin Kemosh, allahn da aka hana na Mowab, da Molek, allahn da aka hana na Ammonawa.
Et Salomon bâtit un haut lieu à Kémos, l'idole abominable de Moab, sur la montagne qui est vis-à-vis de Jérusalem; et à Molec, l'abomination des enfants d'Ammon.
8 Ya yi haka domin dukan baƙin matansa, waɗanda suka ƙone turare suka kuma miƙa hadayu ga allolinsu.
Il en fit de même pour toutes ses femmes étrangères, qui offraient de l'encens et des sacrifices à leurs dieux.
9 Ubangiji ya yi fushi da Solomon domin zuciyarsa ya juye daga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya bayyana masa sau biyu.
Et l'Éternel fut indigné contre Salomon, parce qu'il avait détourné son cœur de l'Éternel, le Dieu d'Israël, qui lui était apparu deux fois,
10 Ko da yake ya hana Solomon bin waɗansu alloli, Solomon bai kiyaye umarnin Ubangiji ba.
Et lui avait même donné ce commandement exprès, de ne point suivre d'autres dieux; mais il n'observa point ce que l'Éternel lui avait commandé.
11 Saboda haka Ubangiji ya ce wa Solomon, “Da yake halinka ke nan, ba ka kuma kiyaye alkawarina, da ƙa’idodina da na umarce ka ba, tabbatacce zan yage masarautar daga gare ka, in ba da ita ga ɗaya daga cikin bayinka.
Et l'Éternel dit à Salomon: Puisque tu as agi ainsi, et que tu n'as pas gardé mon alliance et mes ordonnances que je t'avais données, je t'arracherai certainement le royaume et je le donnerai à ton serviteur.
12 Amma saboda Dawuda mahaifinka, ba zan yi haka a zamaninka ba. Zan yage ta daga hannun ɗanka.
Seulement, pour l'amour de David, ton père, je ne le ferai point pendant ta vie; c'est des mains de ton fils que je l'arracherai.
13 Amma ba zan yage dukan masarautar daga gare shi ba, zan ba shi kabila ɗaya saboda Dawuda bawana, da kuma saboda Urushalima, wadda na zaɓa.”
Toutefois je n'arracherai pas tout le royaume; j'en donnerai une tribu à ton fils pour l'amour de David, mon serviteur, et pour l'amour de Jérusalem que j'ai choisie.
14 Sai Ubangiji ya tayar wa Solomon wani abokin gāba, mai suna Hadad, mutumin Edom daga gidan sarautar Edom.
L'Éternel suscita donc un ennemi à Salomon: Hadad, Iduméen, qui était de la race royale d'Édom.
15 A shekarun baya Dawuda ya ci Edom da yaƙi. Yowab, shugaban sojojinsa ya tafi can domin yă binne Isra’ilawa waɗanda suka mutu a yaƙi. Sa’ad da suke a can, sojojin Isra’ila suka kashe kowane ɗa namiji a Edom.
Dans le temps que David était en Édom, lorsque Joab, chef de l'armée, monta pour ensevelir ceux qui avaient été tués, il tua tous les mâles d'Édom.
16 Yowab da dukan Isra’ilawa suka zauna a can, wata shida, sai da suka hallaka dukan mutane a Edom.
Car Joab demeura là six mois avec tout Israël, jusqu'à ce qu'il eût exterminé tous les mâles d'Édom.
17 Amma Hadad yana ɗan yaro a lokaci, wanda ya gudu zuwa Masar tare da shugabannin mutanen Edom waɗanda suka yi wa mahaifinsa hidima.
Alors Hadad s'enfuit avec quelques Iduméens des serviteurs de son père, pour se retirer en Égypte. Or, Hadad était fort jeune.
18 Suka taso daga Midiyan suka tafi Faran. Sa’an nan suka ɗauki mutane daga Faran suka tafi Masar, zuwa wurin Fir’auna wanda ya ba wa Hadad gida da ƙasa, ya kuma tanada masa da abinci.
Et quand ils furent partis de Madian, ils vinrent à Paran; et ils prirent avec eux des gens de Paran et se retirèrent en Égypte vers Pharaon, roi d'Égypte, qui lui donna une maison, lui assigna de quoi se nourrir, et lui donna aussi une terre.
19 Fir’auna ya ji daɗin Hadad har ya ba shi’yar’uwar matarsa, Sarauniya Tafenes, aure.
Et Hadad fut fort dans les bonnes grâces de Pharaon; de sorte qu'il lui fit épouser la sœur de sa femme, la sœur de la reine Thachpénès.
20 ’Yar’uwar Tafenes ta haifi masa ɗa wanda ya kira Genubat, wanda Tafenes ta yi renonsa a fadan sarki. A can, Genubat ya yi zama da’ya’yan Fir’auna.
Et la sœur de Thachpénès lui enfanta son fils Guénubath, que Thachpénès sevra dans la maison de Pharaon. Ainsi Guénubath était dans la maison de Pharaon, parmi les fils de Pharaon.
21 Yayinda yake a Masar, Hadad ya ji Dawuda ya huta tare da kakanninsa, ya kuma ji cewa Yowab shugaban mayaƙa ya mutu. Sai Hadad ya ce wa Fir’auna, “Bari in tafi, don in koma ƙasata.”
Or, quand Hadad eut appris en Égypte que David s'était endormi avec ses pères, et que Joab, le chef de l'armée, était mort, il dit à Pharaon: Laisse-moi partir, et je m'en irai en mon pays.
22 Fir’auna ya tambaye shi, ya ce, “Me ka rasa a nan da kake so ka koma garinka?” Ya ce, “Ba kome, amma ka dai bar ni in tafi!”
Et Pharaon lui dit: Que te manque-t-il donc auprès de moi, pour que tu demandes ainsi de t'en aller en ton pays? Et il lui répondit: Rien; mais laisse-moi, laisse-moi partir!
23 Allah kuwa ya tayar wa Solomon wani abokin gāba, mai suna Rezon, ɗan Eliyada, wanda ya gudu daga maigidansa, Hadadezer sarkin Zoba.
Dieu suscita encore un ennemi à Salomon: Rézon, fils d'Eljada, qui s'était enfui d'avec son seigneur Hadadézer, roi de Tsoba,
24 Rezon ya tattara mutane kewaye da shi, ya zama kuma shugaban’yan tawaye sa’ad da Dawuda ya hallaka mayaƙan Zoba;’yan tawayen suka tafi Damaskus, inda suka zauna, suka kuma yi mulki.
Et qui assembla des gens contre lui et était chef de bande, lorsque David tua les Syriens. Et ils s'en allèrent à Damas, y habitèrent et y régnèrent.
25 Rezon ya zama babban abokin gāban Isra’ila cikin dukan kwanakin mulkin Solomon. Ya ƙara rikici a kan rikicin Hadad. Rezon ya ƙi mulkin Isra’ila da dukan ransa. Saboda haka Rezon ya yi mulki a Aram ya kuma ƙi jinin Isra’ila.
Rézon fut donc ennemi d'Israël tout le temps de Salomon, outre le mal que fit Hadad; il eut Israël en aversion, et il régna sur la Syrie.
26 Haka ma Yerobowam, ɗan Nebat, shi ma ya yi wa sarki tawaye. Shi ɗaya ne daga shugabannin Solomon, shi mutumin Efraim ne daga Zereda, mahaifiyarsa kuwa gwauruwa ce, mai suna Zeruwa.
Jéroboam, fils de Nébat, Éphratien de Tséréda, serviteur de Salomon, dont la mère, femme veuve, s'appelait Tséruha, se révolta aussi contre le roi.
27 Ga yadda ya tayar wa sarki Solomon. Sarki Solomon ya gina madogaran gini, ya ciccika wurare a katangar birnin Dawuda mahaifinsa da ƙasa.
Et voici l'occasion pour laquelle il se révolta contre le roi: Salomon bâtissait Millo et fermait la brèche de la cité de David, son père.
28 To, Yerobowam mutum ne mai fasaha. Sa’ad da Solomon ya ga yadda matashin yake aiki da himma, sai ya sa shi yă lura da dukan aikin gandu na gidan Yusuf.
Or, Jéroboam était fort et vaillant; et Salomon, voyant ce jeune homme qui travaillait, l'établit sur toute la corvée de la maison de Joseph.
29 Da Yerobowam ya fita Urushalima, sai annabi Ahiya, mutumin Shilo ya tarar da shi a hanya. Lokacin kuwa Ahiya yana saye da sabuwar riga, ba kowa a filin sai su biyu kaɗai.
Or, il arriva dans ce temps-là que Jéroboam sortit de Jérusalem. Et le prophète Achija, le Silonite, vêtu d'un manteau neuf, le rencontra dans le chemin; et ils étaient eux deux tout seuls dans les champs.
30 Sai Ahiya ya kama sabuwar rigar da yake saye da ita ya yage ta gida goma sha biyu.
Alors Achija prit le manteau neuf qu'il avait sur lui, et le déchira en douze morceaux;
31 Sa’an nan ya ce wa Yerobowam, “Ɗauki gida goma wa kanka, gama abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce ke nan, ‘Duba, zan yage masarauta daga hannun Solomon in ba ka kabilu goma.
Et il dit à Jéroboam: Prends pour toi dix morceaux; car ainsi a dit l'Éternel, le Dieu d'Israël: Voici, je vais déchirer le royaume d'entre les mains de Salomon, et je te donnerai dix tribus;
32 Amma saboda bawana Dawuda da kuma birnin Urushalima, wadda na zaɓa daga dukan kabilan Isra’ila, zai sami kabila guda.
Mais il aura une tribu, pour l'amour de David, mon serviteur, et de Jérusalem, la ville que j'ai choisie d'entre toutes les tribus d'Israël;
33 Zan yi wannan domin sun yashe ni, suka kuma yi wa Ashtarot, alliyar Sidoniyawa, da Kemosh, allahn Mowabawa, da kuma Molek, allahn Ammonawa sujada, ba su yi tafiya a hanyoyina ba, ba su kuwa yi abin da yake daidai a idanuna ba, ba su kiyaye farillaina da dokokina kamar yadda Dawuda, mahaifin Solomon ya yi ba.
Parce qu'ils m'ont abandonné et se sont prosternés devant Astarté, divinité des Sidoniens, devant Kémos, dieu de Moab, et devant Milcom, dieu des enfants d'Ammon, et n'ont point marché dans mes voies, pour faire ce qui est droit à mes yeux, pour garder mes statuts et mes ordonnances, comme l'a fait David, père de Salomon.
34 “‘Amma ba zan ɗauki dukan masarautar daga hannun Solomon ba; na naɗa shi sarki, dukan kwanaki ransa saboda Dawuda bawana, wanda na zaɓa, wanda kuma ya kiyaye umarnai da farillaina.
Toutefois je n'ôterai rien de ce royaume d'entre ses mains; car, tout le temps qu'il vivra, je le maintiendrai prince, pour l'amour de David, mon serviteur, que j'ai choisi et qui a gardé mes commandements et mes statuts.
35 Zan ɗauke masarautar daga hannuwan ɗansa ne, in ba ka kabilu goma.
Mais j'ôterai le royaume d'entre les mains de son fils,
36 Zan ba da ɗaya ga ɗansa don kullum Dawuda bawana yă kasance da fitila a gabana a Urushalima, birnin da na zaɓa in sa Sunana.
Et je t'en donnerai dix tribus; et je donnerai une tribu à son fils, afin que David, mon serviteur, ait toujours une lampe devant moi à Jérusalem, la ville que j'ai choisie pour y mettre mon nom.
37 Amma fa, ga kai, zan ɗauke ka, za ka kuwa yi mulki bisa dukan abin da zuciyarka take so; za ka zama sarki a bisa Isra’ila.
Je te prendrai donc, tu régneras sur tout ce que souhaitera ton âme, et tu seras roi sur Israël.
38 In ka aikata dukan abin da na umarce ka, ka yi tafiya a hanyoyina, ka kuma yi abin da yake daidai a idanuna ta wurin kiyaye farillaina da umarnaina, kamar yadda Dawuda bawana ya yi, zan kasance tare da kai. Zan gina maka masarauta mai dawwama kamar wadda na gina wa Dawuda, zan kuma ba da Isra’ila gare ka.
Et si tu m'obéis dans tout ce que je te commanderai, si tu marches dans mes voies et que tu fasses tout ce qui est droit à mes yeux, gardant mes statuts et mes commandements, comme a fait David, mon serviteur, je serai avec toi; je te bâtirai une maison stable, comme j'en ai bâti une à David, et je te donnerai Israël.
39 Zan ƙasƙantar da zuriyar Dawuda saboda wannan, amma ba har abada ba.’”
Ainsi j'affligerai la postérité de David à cause de cela; mais non pour toujours.
40 Solomon ya yi ƙoƙari yă kashe Yerobowam, amma Yerobowam ya tsere zuwa Masar, zuwa wurin sarki Shishak, ya zauna a can sai bayan mutuwar Solomon.
Or Salomon chercha à faire mourir Jéroboam; mais Jéroboam se leva et s'enfuit en Égypte vers Shishak, roi d'Égypte; et il demeura en Égypte jusqu'à la mort de Salomon.
41 Game da sauran ayyukan mulkin Solomon, da dukan abubuwan da ya yi, da hikimar da ya nuna, an rubuta su a littafin tarihin Solomon.
Quant au reste des actions de Salomon, et tout ce qu'il fit, et sa sagesse, cela n'est-il pas écrit au livre des Actes de Salomon?
42 Solomon ya yi mulki a Urushalima, a bisa dukan Isra’ila, shekaru arba’in.
Or, le temps que Salomon régna à Jérusalem sur tout Israël fut de quarante ans.
43 Sa’an nan ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a birnin Dawuda mahaifinsa. Sai Rehobowam ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Puis Salomon s'endormit avec ses pères, et il fut enseveli dans la cité de David, son père. Et Roboam, son fils, régna à sa place.