< 1 Sarakuna 11 >

1 Sarki Solomon ya ƙaunaci baƙin mata. Ban da’yar Fir’auna, ya auri Mowabawa, Ammonawa, mutanen Edom, Sidoniyawa da Hittiyawa.
Now King Solomon loved many foreign women including the daughter of Pharaoh—women of the Moabites, Ammonites, Edomites, Sidonians, and Hittites.
2 Sun fito daga al’ummai da Ubangiji ya ce wa Isra’ilawa, “Kada ku yi aurayya da su, domin tabbatacce za su juye zukatanku zuwa ga waɗansu alloli.” Duk da haka Solomon ya manne musu, ya nace, yana ƙaunarsu.
They were from the nations about which Yahweh said to the people of Israel, “You will not go among them to marry, neither will they come among you, for they will certainly turn your heart to their gods.” In spite of this command, Solomon was affectionate toward these women in love.
3 Ya auri mata ɗari bakwai, haifaffun gidan sarauta, da kuma ƙwarƙwarai ɗari uku. Matan nan nasa suka karkatar da shi.
Solomon had seven hundred royal wives and three hundred concubines. His wives turned his heart away.
4 Yayinda Solomon yake tsufa, matansa suka juye zuciyarsa ga bin waɗansu alloli, zuciyarsa kuwa ba tă bi Ubangiji Allahnsa ɗungum kamar yadda zuciyar Dawuda mahaifinsa ta kasance ba.
For when Solomon grew old, his wives turned away his heart after other gods; his heart was not fully surrendered to Yahweh his God, as was the heart of David his father.
5 Ya bi Ashtarot, alliyar Sidoniyawa, da Molek, allahn da aka hana na Ammonawa.
For Solomon followed Ashtoreth, the goddess of the Sidonians, and he followed Molech, the disgusting idol of the Ammonites.
6 Saboda haka Solomon ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji. Bai bi Ubangiji gaba ɗaya kamar yadda Dawuda mahaifinsa ya yi ba.
Solomon did what was evil in the sight of Yahweh; he did not fully follow Yahweh as David his father had done.
7 A kan tudu, gabas da Urushalima, Solomon ya gina masujada a can domin Kemosh, allahn da aka hana na Mowab, da Molek, allahn da aka hana na Ammonawa.
Then Solomon built a high place for Chemosh, the disgusting idol of Moab, on a hill east of Jerusalem, and also for Molech, the disgusting idol of the people of Ammon.
8 Ya yi haka domin dukan baƙin matansa, waɗanda suka ƙone turare suka kuma miƙa hadayu ga allolinsu.
He also built high places for all his foreign wives, who burned incense and sacrificed to their gods at them.
9 Ubangiji ya yi fushi da Solomon domin zuciyarsa ya juye daga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya bayyana masa sau biyu.
Yahweh was angry with Solomon, because his heart had turned away from him, the God of Israel, even though he had appeared to him twice
10 Ko da yake ya hana Solomon bin waɗansu alloli, Solomon bai kiyaye umarnin Ubangiji ba.
and commanded him about this very thing, that he should not go after other gods. But Solomon did not obey what Yahweh commanded.
11 Saboda haka Ubangiji ya ce wa Solomon, “Da yake halinka ke nan, ba ka kuma kiyaye alkawarina, da ƙa’idodina da na umarce ka ba, tabbatacce zan yage masarautar daga gare ka, in ba da ita ga ɗaya daga cikin bayinka.
Therefore Yahweh said to Solomon, “Because you have done this and have not kept the covenant and my statutes that I have commanded you, I will surely tear the kingdom from you and give it to your servant.
12 Amma saboda Dawuda mahaifinka, ba zan yi haka a zamaninka ba. Zan yage ta daga hannun ɗanka.
However, for David your father's sake, I will not do it in your lifetime, but I will tear it out of the hand of your son.
13 Amma ba zan yage dukan masarautar daga gare shi ba, zan ba shi kabila ɗaya saboda Dawuda bawana, da kuma saboda Urushalima, wadda na zaɓa.”
Yet I will not tear away all the kingdom; I will give one tribe to your son for David my servant's sake, and for the sake of Jerusalem, which I have chosen.”
14 Sai Ubangiji ya tayar wa Solomon wani abokin gāba, mai suna Hadad, mutumin Edom daga gidan sarautar Edom.
Then Yahweh raised up an adversary to Solomon, Hadad the Edomite. He was from the royal family of Edom.
15 A shekarun baya Dawuda ya ci Edom da yaƙi. Yowab, shugaban sojojinsa ya tafi can domin yă binne Isra’ilawa waɗanda suka mutu a yaƙi. Sa’ad da suke a can, sojojin Isra’ila suka kashe kowane ɗa namiji a Edom.
When David was in Edom, Joab the captain of the army had gone up to bury the dead, every man who had been killed in Edom.
16 Yowab da dukan Isra’ilawa suka zauna a can, wata shida, sai da suka hallaka dukan mutane a Edom.
Joab and all Israel remained there six months until he had killed every male in Edom.
17 Amma Hadad yana ɗan yaro a lokaci, wanda ya gudu zuwa Masar tare da shugabannin mutanen Edom waɗanda suka yi wa mahaifinsa hidima.
But Hadad was taken with other Edomites by his father's servants into Egypt, since Hadad was still a little child.
18 Suka taso daga Midiyan suka tafi Faran. Sa’an nan suka ɗauki mutane daga Faran suka tafi Masar, zuwa wurin Fir’auna wanda ya ba wa Hadad gida da ƙasa, ya kuma tanada masa da abinci.
They left Midian and came to Paran, from where they took men with them to Egypt, to Pharaoh king of Egypt, who gave him a house and land and food.
19 Fir’auna ya ji daɗin Hadad har ya ba shi’yar’uwar matarsa, Sarauniya Tafenes, aure.
Hadad found great favor in the sight of Pharaoh, so that Pharaoh gave him a wife, his own wife's sister, the sister of Tahpenes the queen.
20 ’Yar’uwar Tafenes ta haifi masa ɗa wanda ya kira Genubat, wanda Tafenes ta yi renonsa a fadan sarki. A can, Genubat ya yi zama da’ya’yan Fir’auna.
The sister of Tahpenes gave birth to Hadad's son. They named him Genubath. Tahpenes raised him in Pharaoh's palace. So Genubath lived in Pharaoh's palace among the children of Pharaoh.
21 Yayinda yake a Masar, Hadad ya ji Dawuda ya huta tare da kakanninsa, ya kuma ji cewa Yowab shugaban mayaƙa ya mutu. Sai Hadad ya ce wa Fir’auna, “Bari in tafi, don in koma ƙasata.”
While he was in Egypt, Hadad heard that David had lain down with his ancestors and that Joab the captain of the host was dead, Hadad said to Pharaoh, “Let me depart, so I may go to my own country.”
22 Fir’auna ya tambaye shi, ya ce, “Me ka rasa a nan da kake so ka koma garinka?” Ya ce, “Ba kome, amma ka dai bar ni in tafi!”
Then Pharaoh said to him, “But what have you lacked with me, that you now seek to go to your own country?” Hadad answered, “Nothing. Please let me go.”
23 Allah kuwa ya tayar wa Solomon wani abokin gāba, mai suna Rezon, ɗan Eliyada, wanda ya gudu daga maigidansa, Hadadezer sarkin Zoba.
God also raised up another adversary to Solomon, Rezon son of Eliada, who had fled from his master Hadadezer king of Zobah.
24 Rezon ya tattara mutane kewaye da shi, ya zama kuma shugaban’yan tawaye sa’ad da Dawuda ya hallaka mayaƙan Zoba;’yan tawayen suka tafi Damaskus, inda suka zauna, suka kuma yi mulki.
Rezon gathered men to himself and became captain over a small force, when David defeated the men of Zobah. Rezon's men went to Damascus and lived there, and Rezon controlled Damascus.
25 Rezon ya zama babban abokin gāban Isra’ila cikin dukan kwanakin mulkin Solomon. Ya ƙara rikici a kan rikicin Hadad. Rezon ya ƙi mulkin Isra’ila da dukan ransa. Saboda haka Rezon ya yi mulki a Aram ya kuma ƙi jinin Isra’ila.
He was an enemy of Israel all the days of Solomon, along with the trouble that Hadad caused. Rezon abhorred Israel and reigned over Aram.
26 Haka ma Yerobowam, ɗan Nebat, shi ma ya yi wa sarki tawaye. Shi ɗaya ne daga shugabannin Solomon, shi mutumin Efraim ne daga Zereda, mahaifiyarsa kuwa gwauruwa ce, mai suna Zeruwa.
Then Jeroboam son of Nebat, an Ephraimite of Zeredah, an official of Solomon, whose mother's name was Zeruah, a widow, also lifted up his hand against the king.
27 Ga yadda ya tayar wa sarki Solomon. Sarki Solomon ya gina madogaran gini, ya ciccika wurare a katangar birnin Dawuda mahaifinsa da ƙasa.
He lifted up his hand against the king because Solomon had built up the place located at Millo and repaired the opening in the city wall of David his father.
28 To, Yerobowam mutum ne mai fasaha. Sa’ad da Solomon ya ga yadda matashin yake aiki da himma, sai ya sa shi yă lura da dukan aikin gandu na gidan Yusuf.
Jeroboam was a mighty man of valor. Solomon saw that the young man was industrious, so he gave him command over all the labor of the house of Joseph.
29 Da Yerobowam ya fita Urushalima, sai annabi Ahiya, mutumin Shilo ya tarar da shi a hanya. Lokacin kuwa Ahiya yana saye da sabuwar riga, ba kowa a filin sai su biyu kaɗai.
At that time, when Jeroboam went out of Jerusalem, the prophet Ahijah the Shilonite found him on the road. Now Ahijah had dressed in a new garment and the two men were alone in the field.
30 Sai Ahiya ya kama sabuwar rigar da yake saye da ita ya yage ta gida goma sha biyu.
Then Ahijah grabbed hold of the new garment that was on him and tore it into twelve pieces.
31 Sa’an nan ya ce wa Yerobowam, “Ɗauki gida goma wa kanka, gama abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce ke nan, ‘Duba, zan yage masarauta daga hannun Solomon in ba ka kabilu goma.
He said to Jeroboam, “Take ten pieces, for Yahweh, the God of Israel, says, 'Look, I will tear the kingdom out of the hand of Solomon and I will give ten tribes to you
32 Amma saboda bawana Dawuda da kuma birnin Urushalima, wadda na zaɓa daga dukan kabilan Isra’ila, zai sami kabila guda.
(but Solomon will have one tribe, for my servant David's sake and for Jerusalem's sake—the city that I have chosen out of all the tribes of Israel),
33 Zan yi wannan domin sun yashe ni, suka kuma yi wa Ashtarot, alliyar Sidoniyawa, da Kemosh, allahn Mowabawa, da kuma Molek, allahn Ammonawa sujada, ba su yi tafiya a hanyoyina ba, ba su kuwa yi abin da yake daidai a idanuna ba, ba su kiyaye farillaina da dokokina kamar yadda Dawuda, mahaifin Solomon ya yi ba.
because they have forsaken me and have worshiped Ashtoreth the goddess of the Sidonians, Chemosh the god of Moab, and Molech the god of the people of Ammon. They have not walked in my ways, to do what is right in my eyes, and to keep my statutes and my decrees, as did David his father.
34 “‘Amma ba zan ɗauki dukan masarautar daga hannun Solomon ba; na naɗa shi sarki, dukan kwanaki ransa saboda Dawuda bawana, wanda na zaɓa, wanda kuma ya kiyaye umarnai da farillaina.
However, I will not take the whole kingdom out of Solomon's hand. Instead, I have made him ruler all the days of his life, for David my servant's sake whom I chose, the one who kept my commandments and my statutes.
35 Zan ɗauke masarautar daga hannuwan ɗansa ne, in ba ka kabilu goma.
But I will take the kingdom out of his son's hand and I will give it to you, ten tribes.
36 Zan ba da ɗaya ga ɗansa don kullum Dawuda bawana yă kasance da fitila a gabana a Urushalima, birnin da na zaɓa in sa Sunana.
I will give one tribe to Solomon's son, so that David my servant may always have a lamp before me in Jerusalem, the city in which I have chosen to put my name.
37 Amma fa, ga kai, zan ɗauke ka, za ka kuwa yi mulki bisa dukan abin da zuciyarka take so; za ka zama sarki a bisa Isra’ila.
I will take you, and you will rule to fulfill all that you desire, and you will be king over Israel.
38 In ka aikata dukan abin da na umarce ka, ka yi tafiya a hanyoyina, ka kuma yi abin da yake daidai a idanuna ta wurin kiyaye farillaina da umarnaina, kamar yadda Dawuda bawana ya yi, zan kasance tare da kai. Zan gina maka masarauta mai dawwama kamar wadda na gina wa Dawuda, zan kuma ba da Isra’ila gare ka.
If you listen to all that I command you, and if you walk in my ways and do what is right in my eyes, to keep my statutes and my commandments, as David my servant did, then I will be with you and will build you a sure house, as I built for David, and will give Israel to you.
39 Zan ƙasƙantar da zuriyar Dawuda saboda wannan, amma ba har abada ba.’”
I will punish the descendants of David, but not forever.'”
40 Solomon ya yi ƙoƙari yă kashe Yerobowam, amma Yerobowam ya tsere zuwa Masar, zuwa wurin sarki Shishak, ya zauna a can sai bayan mutuwar Solomon.
So Solomon tried to kill Jeroboam. But Jeroboam got up and fled into Egypt, to Shishak king of Egypt, and he remained in Egypt until the death of Solomon.
41 Game da sauran ayyukan mulkin Solomon, da dukan abubuwan da ya yi, da hikimar da ya nuna, an rubuta su a littafin tarihin Solomon.
As for the other matters concerning Solomon, all that he did and his wisdom, are they not written in the book of the events of Solomon?
42 Solomon ya yi mulki a Urushalima, a bisa dukan Isra’ila, shekaru arba’in.
Solomon reigned in Jerusalem over all Israel for forty years.
43 Sa’an nan ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a birnin Dawuda mahaifinsa. Sai Rehobowam ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
He slept with his ancestors and he was buried in the city of David his father. Rehoboam his son became king in his place.

< 1 Sarakuna 11 >