< 1 Sarakuna 11 >

1 Sarki Solomon ya ƙaunaci baƙin mata. Ban da’yar Fir’auna, ya auri Mowabawa, Ammonawa, mutanen Edom, Sidoniyawa da Hittiyawa.
King Solomon married many foreign women. First he married the daughter of the king of Egypt. He also married women from the Heth people-group and from the Moab, Ammon, and Edom people-groups, and from Sidon [city].
2 Sun fito daga al’ummai da Ubangiji ya ce wa Isra’ilawa, “Kada ku yi aurayya da su, domin tabbatacce za su juye zukatanku zuwa ga waɗansu alloli.” Duk da haka Solomon ya manne musu, ya nace, yana ƙaunarsu.
He married them even though Yahweh had commanded the Israeli people, “Do not marry people from those areas, because if you do that, they will surely persuade you [IDM] to worship the gods that they worship!”
3 Ya auri mata ɗari bakwai, haifaffun gidan sarauta, da kuma ƙwarƙwarai ɗari uku. Matan nan nasa suka karkatar da shi.
Solomon married 700 women who were kings’ daughters. He also had 300 wives who were his slaves/servants. And his wives caused him to turn away [from worshiping God].
4 Yayinda Solomon yake tsufa, matansa suka juye zuciyarsa ga bin waɗansu alloli, zuciyarsa kuwa ba tă bi Ubangiji Allahnsa ɗungum kamar yadda zuciyar Dawuda mahaifinsa ta kasance ba.
By the time that Solomon became old, they had persuaded him to worship the gods from their countries. He was not completely dedicated/committed to Yahweh his God like his father [SYN] David had been.
5 Ya bi Ashtarot, alliyar Sidoniyawa, da Molek, allahn da aka hana na Ammonawa.
Solomon worshiped Astarte, the goddess that the people of Sidon [worshiped], and he worshiped Molech, the disgusting god that the Ammon people-group [worshiped].
6 Saboda haka Solomon ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji. Bai bi Ubangiji gaba ɗaya kamar yadda Dawuda mahaifinsa ya yi ba.
That’s how Solomon did things that Yahweh said were evil. He did not conduct his life like his father David had done; he did not conduct his life as Yahweh wanted him to.
7 A kan tudu, gabas da Urushalima, Solomon ya gina masujada a can domin Kemosh, allahn da aka hana na Mowab, da Molek, allahn da aka hana na Ammonawa.
On the hill to the east of Jerusalem he built a place to worship Chemosh, the disgusting god that the Moab people-group [worshiped], and a place to worship Molech, the disgusting god that the Ammon people-group [worshiped].
8 Ya yi haka domin dukan baƙin matansa, waɗanda suka ƙone turare suka kuma miƙa hadayu ga allolinsu.
He also built places where all his foreign wives could burn incense and offer sacrifices to the gods from their own countries.
9 Ubangiji ya yi fushi da Solomon domin zuciyarsa ya juye daga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya bayyana masa sau biyu.
Even though Yahweh, the God whom the Israelis [worshiped], had appeared to Solomon two times, and had commanded him to not worship foreign gods, Solomon refused to obey Yahweh. So Yahweh was angry with Solomon,
10 Ko da yake ya hana Solomon bin waɗansu alloli, Solomon bai kiyaye umarnin Ubangiji ba.
11 Saboda haka Ubangiji ya ce wa Solomon, “Da yake halinka ke nan, ba ka kuma kiyaye alkawarina, da ƙa’idodina da na umarce ka ba, tabbatacce zan yage masarautar daga gare ka, in ba da ita ga ɗaya daga cikin bayinka.
and said to him, “You have chosen to break the agreement that I made with you and to disobey what I commanded you. So I am surely not going to allow you to rule all of your kingdom. I am going to allow one of your officials to rule it.
12 Amma saboda Dawuda mahaifinka, ba zan yi haka a zamaninka ba. Zan yage ta daga hannun ɗanka.
But, because of [what I promised] your father David, I will allow you to rule all your kingdom while you are still [living]. [After you die], I will not allow your son to rule the whole kingdom [MTY].
13 Amma ba zan yage dukan masarautar daga gare shi ba, zan ba shi kabila ɗaya saboda Dawuda bawana, da kuma saboda Urushalima, wadda na zaɓa.”
But I will not take all the kingdom away from him. Instead, I will allow him to rule one tribe [besides the tribe of Judah], because of what I promised to David, who served me [well], and because [I want David’s descendants to rule in] Jerusalem, [where my temple is located].”
14 Sai Ubangiji ya tayar wa Solomon wani abokin gāba, mai suna Hadad, mutumin Edom daga gidan sarautar Edom.
Yahweh caused Hadad, from the family of the kings in the Edom people-group, to rebel against Solomon.
15 A shekarun baya Dawuda ya ci Edom da yaƙi. Yowab, shugaban sojojinsa ya tafi can domin yă binne Isra’ilawa waɗanda suka mutu a yaƙi. Sa’ad da suke a can, sojojin Isra’ila suka kashe kowane ɗa namiji a Edom.
What happened was that previously, when David’s [army] had conquered the Edom people-group, his army commander Joab had gone there to [help] bury the [Israeli soldiers] who had been killed [in the battle]. Joab and his army remained in the Edom area for six months, and during that time they killed all the males of that area.
16 Yowab da dukan Isra’ilawa suka zauna a can, wata shida, sai da suka hallaka dukan mutane a Edom.
17 Amma Hadad yana ɗan yaro a lokaci, wanda ya gudu zuwa Masar tare da shugabannin mutanen Edom waɗanda suka yi wa mahaifinsa hidima.
Hadad was a young child [at that time], and he had escaped to Egypt, along with some of his father’s servants from the Edom area.
18 Suka taso daga Midiyan suka tafi Faran. Sa’an nan suka ɗauki mutane daga Faran suka tafi Masar, zuwa wurin Fir’auna wanda ya ba wa Hadad gida da ƙasa, ya kuma tanada masa da abinci.
They [went to the] Midian [region], and then they went to [the desert area at] Paran. Some other men joined them there. Then they all traveled to Egypt and went to see the king of Egypt. The king gave Hadad some land and ordered his servants to give him some food regularly.
19 Fir’auna ya ji daɗin Hadad har ya ba shi’yar’uwar matarsa, Sarauniya Tafenes, aure.
The king liked Hadad. As a result he gave him the sister of his own wife, Queen Tahpenes, to be Hadad’s wife.
20 ’Yar’uwar Tafenes ta haifi masa ɗa wanda ya kira Genubat, wanda Tafenes ta yi renonsa a fadan sarki. A can, Genubat ya yi zama da’ya’yan Fir’auna.
Later Hadad’s wife gave birth to a son named Genubath. The sister of Tahpenes (raised him/brought him up) in the palace, where he lived with the king’s sons.
21 Yayinda yake a Masar, Hadad ya ji Dawuda ya huta tare da kakanninsa, ya kuma ji cewa Yowab shugaban mayaƙa ya mutu. Sai Hadad ya ce wa Fir’auna, “Bari in tafi, don in koma ƙasata.”
While Hadad was in Egypt, he heard that David had died [EUP], and that Joab, the commander of David’s army, was also dead. So he said to the king of Egypt, “Please allow me to return to my own country.”
22 Fir’auna ya tambaye shi, ya ce, “Me ka rasa a nan da kake so ka koma garinka?” Ya ce, “Ba kome, amma ka dai bar ni in tafi!”
But the king said to him, “Why do you want to go back to your country? Is there something that you lack that you want me to give to you?” Hadad replied, “No, but please just allow me to go.” [So the king allowed him to leave, and he returned to his own country and became the king of Edom].
23 Allah kuwa ya tayar wa Solomon wani abokin gāba, mai suna Rezon, ɗan Eliyada, wanda ya gudu daga maigidansa, Hadadezer sarkin Zoba.
God also caused another man named Rezon, the son of Eliada, to rebel against Solomon. Rezon had run away from his master, King Hadadezer of [the] Zobah [area north of Damascus].
24 Rezon ya tattara mutane kewaye da shi, ya zama kuma shugaban’yan tawaye sa’ad da Dawuda ya hallaka mayaƙan Zoba;’yan tawayen suka tafi Damaskus, inda suka zauna, suka kuma yi mulki.
Rezon then became the leader of a group of outlaws. That happened after David’s [army had defeated Hadadezer and] had [also] killed all [his soldiers]. Rezon and his men went to Damascus and started to live there, and [the people there] appointed him to be their king.
25 Rezon ya zama babban abokin gāban Isra’ila cikin dukan kwanakin mulkin Solomon. Ya ƙara rikici a kan rikicin Hadad. Rezon ya ƙi mulkin Isra’ila da dukan ransa. Saboda haka Rezon ya yi mulki a Aram ya kuma ƙi jinin Isra’ila.
All during the time that Solomon was alive, while Rezon was ruling [not only Damascus but all of] Syria, he was an enemy of Israel and caused trouble for Israel like Hadad did.
26 Haka ma Yerobowam, ɗan Nebat, shi ma ya yi wa sarki tawaye. Shi ɗaya ne daga shugabannin Solomon, shi mutumin Efraim ne daga Zereda, mahaifiyarsa kuwa gwauruwa ce, mai suna Zeruwa.
Another man who rebelled against [IDM] Solomon was one of his officials named Jeroboam, the son of Nebat. He was from Zeredah [town] in [the region where the tribe of] Ephraim [lives]. His mother was a widow named Zeruah.
27 Ga yadda ya tayar wa sarki Solomon. Sarki Solomon ya gina madogaran gini, ya ciccika wurare a katangar birnin Dawuda mahaifinsa da ƙasa.
This is what happened. Solomon’s workers were filling in the land/ground on the east side of Jerusalem and repairing the walls [around the city].
28 To, Yerobowam mutum ne mai fasaha. Sa’ad da Solomon ya ga yadda matashin yake aiki da himma, sai ya sa shi yă lura da dukan aikin gandu na gidan Yusuf.
Jeroboam was a very capable young man. So, when Solomon saw that he worked very hard, he appointed him to supervise all the men who were forced to work in the areas where the tribes of Manasseh and Ephraim live.
29 Da Yerobowam ya fita Urushalima, sai annabi Ahiya, mutumin Shilo ya tarar da shi a hanya. Lokacin kuwa Ahiya yana saye da sabuwar riga, ba kowa a filin sai su biyu kaɗai.
One day when Jeroboam was walking alone along the road outside of Jerusalem, the prophet Ahijah from Shiloh [city] met him. Ahijah was wearing a new robe,
30 Sai Ahiya ya kama sabuwar rigar da yake saye da ita ya yage ta gida goma sha biyu.
which he took off and tore into twelve pieces.
31 Sa’an nan ya ce wa Yerobowam, “Ɗauki gida goma wa kanka, gama abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce ke nan, ‘Duba, zan yage masarauta daga hannun Solomon in ba ka kabilu goma.
He said to Jeroboam, “Take ten of these pieces for yourself, because Yahweh, the God whom we Israelis [worship], says to you, ‘I am going to tear the kingdom from Solomon, and I am going to enable you to become the ruler of ten of the tribes [of Israel].
32 Amma saboda bawana Dawuda da kuma birnin Urushalima, wadda na zaɓa daga dukan kabilan Isra’ila, zai sami kabila guda.
Solomon’s [descendants] will still rule one tribe (OR, two tribes), because of [what I promised] David, a man who served me [very well], and because of Jerusalem, the city that I have chosen from all the cities in Israel [to be the city where my people will worship me].
33 Zan yi wannan domin sun yashe ni, suka kuma yi wa Ashtarot, alliyar Sidoniyawa, da Kemosh, allahn Mowabawa, da kuma Molek, allahn Ammonawa sujada, ba su yi tafiya a hanyoyina ba, ba su kuwa yi abin da yake daidai a idanuna ba, ba su kiyaye farillaina da dokokina kamar yadda Dawuda, mahaifin Solomon ya yi ba.
I am going to do this because Solomon has rejected me and has been worshiping Astarte, the goddess that the people of Sidon worship, Chemosh, the god that the Moab people-group worship, and Milcom, the god that the Ammon people-group worship. He has not conducted his life as I wanted him to. He has not obeyed my statutes and laws, like his father David did.
34 “‘Amma ba zan ɗauki dukan masarautar daga hannun Solomon ba; na naɗa shi sarki, dukan kwanaki ransa saboda Dawuda bawana, wanda na zaɓa, wanda kuma ya kiyaye umarnai da farillaina.
‘But I will not take the entire kingdom away from him. I will enable him to rule [Judah] all during the years that he is alive. I will do that because of [what I promised to do for] David, whom I chose [to be the king], and who served me [well], and who always obeyed my commandments and laws.
35 Zan ɗauke masarautar daga hannuwan ɗansa ne, in ba ka kabilu goma.
But I will take the [other] ten tribes of his kingdom and give them to you [to rule].
36 Zan ba da ɗaya ga ɗansa don kullum Dawuda bawana yă kasance da fitila a gabana a Urushalima, birnin da na zaɓa in sa Sunana.
I will allow Solomon’s son to rule one tribe, in order that descendants [MET] of David will always rule in Jerusalem, the city that I have chosen to be the place where [my people worship] me [MTY].
37 Amma fa, ga kai, zan ɗauke ka, za ka kuwa yi mulki bisa dukan abin da zuciyarka take so; za ka zama sarki a bisa Isra’ila.
I will enable you to become the king of Israel, and you will rule over all the territory that you want to.
38 In ka aikata dukan abin da na umarce ka, ka yi tafiya a hanyoyina, ka kuma yi abin da yake daidai a idanuna ta wurin kiyaye farillaina da umarnaina, kamar yadda Dawuda bawana ya yi, zan kasance tare da kai. Zan gina maka masarauta mai dawwama kamar wadda na gina wa Dawuda, zan kuma ba da Isra’ila gare ka.
If you obey all that I command you to do, and conduct your life as I want you to, and if you do what I say is right by obeying my laws and commandments like David did, I will help you. I will make sure that your descendants will rule after you [die], like I [promised to] do for David.
39 Zan ƙasƙantar da zuriyar Dawuda saboda wannan, amma ba har abada ba.’”
Because of [Solomon’s sins], I will punish David’s descendants, but I will not continue to punish them forever.’”
40 Solomon ya yi ƙoƙari yă kashe Yerobowam, amma Yerobowam ya tsere zuwa Masar, zuwa wurin sarki Shishak, ya zauna a can sai bayan mutuwar Solomon.
Solomon [found out what Ahijah told Jeroboam], so he tried to kill Jeroboam. But Jeroboam escaped and went to Egypt. He went to Shishak, the king of Egypt, and stayed with him until after Solomon died.
41 Game da sauran ayyukan mulkin Solomon, da dukan abubuwan da ya yi, da hikimar da ya nuna, an rubuta su a littafin tarihin Solomon.
[A record of] all the other things that Solomon did, and all the wise things that he [said and wrote], was written in the Book Telling what Solomon Did.
42 Solomon ya yi mulki a Urushalima, a bisa dukan Isra’ila, shekaru arba’in.
He was the king in Jerusalem who ruled over all of Israel for 40 years.
43 Sa’an nan ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a birnin Dawuda mahaifinsa. Sai Rehobowam ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Then Solomon died [EUP], and was buried in the [part of Jerusalem called] ‘The City of David’. And his son Rehoboam became the king.

< 1 Sarakuna 11 >