< 1 Sarakuna 11 >

1 Sarki Solomon ya ƙaunaci baƙin mata. Ban da’yar Fir’auna, ya auri Mowabawa, Ammonawa, mutanen Edom, Sidoniyawa da Hittiyawa.
And King Solomon has loved many strange women, and the daughter of Pharaoh, females of Moab, Ammon, Edom, Sidon, [and] of the Hittites,
2 Sun fito daga al’ummai da Ubangiji ya ce wa Isra’ilawa, “Kada ku yi aurayya da su, domin tabbatacce za su juye zukatanku zuwa ga waɗansu alloli.” Duk da haka Solomon ya manne musu, ya nace, yana ƙaunarsu.
of the nations of which YHWH said to the sons of Israel, “You do not go in to them, and they do not go in to you; surely they turn aside your heart after their gods”; Solomon has cleaved to them for love.
3 Ya auri mata ɗari bakwai, haifaffun gidan sarauta, da kuma ƙwarƙwarai ɗari uku. Matan nan nasa suka karkatar da shi.
And he has seven hundred wives, princesses, and three hundred concubines; and his wives turn aside his heart.
4 Yayinda Solomon yake tsufa, matansa suka juye zuciyarsa ga bin waɗansu alloli, zuciyarsa kuwa ba tă bi Ubangiji Allahnsa ɗungum kamar yadda zuciyar Dawuda mahaifinsa ta kasance ba.
And it comes to pass, at the time of Solomon’s old age, his wives have turned aside his heart after other gods, and his heart has not been perfect with his God YHWH, like the heart of his father David.
5 Ya bi Ashtarot, alliyar Sidoniyawa, da Molek, allahn da aka hana na Ammonawa.
And Solomon goes after Ashtoreth goddess of the Zidonians, and after Milcom the abomination of the Ammonites;
6 Saboda haka Solomon ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji. Bai bi Ubangiji gaba ɗaya kamar yadda Dawuda mahaifinsa ya yi ba.
and Solomon does evil in the eyes of YHWH, and has not been fully after YHWH, like his father David.
7 A kan tudu, gabas da Urushalima, Solomon ya gina masujada a can domin Kemosh, allahn da aka hana na Mowab, da Molek, allahn da aka hana na Ammonawa.
Then Solomon builds a high place for Chemosh the abomination of Moab, in the hill that [is] on the front of Jerusalem, and for Molech the abomination of the sons of Ammon;
8 Ya yi haka domin dukan baƙin matansa, waɗanda suka ƙone turare suka kuma miƙa hadayu ga allolinsu.
and so he has done for all his strange women, who are perfuming and sacrificing to their gods.
9 Ubangiji ya yi fushi da Solomon domin zuciyarsa ya juye daga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya bayyana masa sau biyu.
And YHWH shows Himself angry with Solomon, for his heart has turned aside from YHWH, God of Israel, who had appeared to him twice,
10 Ko da yake ya hana Solomon bin waɗansu alloli, Solomon bai kiyaye umarnin Ubangiji ba.
and given a charge to him concerning this thing, not to go after other gods; and he has not kept that which YHWH commanded,
11 Saboda haka Ubangiji ya ce wa Solomon, “Da yake halinka ke nan, ba ka kuma kiyaye alkawarina, da ƙa’idodina da na umarce ka ba, tabbatacce zan yage masarautar daga gare ka, in ba da ita ga ɗaya daga cikin bayinka.
and YHWH says to Solomon, “Because that this has been with you, and you have not kept My covenant and My statutes that I charged on you, I surely tear the kingdom from you, and have given it to your servant.
12 Amma saboda Dawuda mahaifinka, ba zan yi haka a zamaninka ba. Zan yage ta daga hannun ɗanka.
Only, I do not do it in your days, for the sake of your father David; I tear it out of the hand of your son;
13 Amma ba zan yage dukan masarautar daga gare shi ba, zan ba shi kabila ɗaya saboda Dawuda bawana, da kuma saboda Urushalima, wadda na zaɓa.”
only, I do not tear away all of the kingdom; I give one tribe to your son, for the sake of My servant David, and for the sake of Jerusalem that I have chosen.”
14 Sai Ubangiji ya tayar wa Solomon wani abokin gāba, mai suna Hadad, mutumin Edom daga gidan sarautar Edom.
And YHWH raises up an adversary against Solomon, Hadad the Edomite; he [is] of the seed of the king in Edom;
15 A shekarun baya Dawuda ya ci Edom da yaƙi. Yowab, shugaban sojojinsa ya tafi can domin yă binne Isra’ilawa waɗanda suka mutu a yaƙi. Sa’ad da suke a can, sojojin Isra’ila suka kashe kowane ɗa namiji a Edom.
and it comes to pass, in David’s being with Edom, in the going up of Joab head of the host to bury the slain, that he strikes every male in Edom—
16 Yowab da dukan Isra’ilawa suka zauna a can, wata shida, sai da suka hallaka dukan mutane a Edom.
for six months Joab abided there, and all Israel, until the cutting off of every male in Edom—
17 Amma Hadad yana ɗan yaro a lokaci, wanda ya gudu zuwa Masar tare da shugabannin mutanen Edom waɗanda suka yi wa mahaifinsa hidima.
and Hadad flees, he and certain Edomites, of the servants of his father, with him, to go to Egypt, and Hadad [is] a little youth,
18 Suka taso daga Midiyan suka tafi Faran. Sa’an nan suka ɗauki mutane daga Faran suka tafi Masar, zuwa wurin Fir’auna wanda ya ba wa Hadad gida da ƙasa, ya kuma tanada masa da abinci.
and they rise out of Midian, and come into Paran, and take men with them out of Paran, and come into Egypt, to Pharaoh king of Egypt, and he gives a house to him, and has commanded bread for him, and has given land to him.
19 Fir’auna ya ji daɗin Hadad har ya ba shi’yar’uwar matarsa, Sarauniya Tafenes, aure.
And Hadad finds grace in the eyes of Pharaoh exceedingly, and he gives to him a wife, the sister of his own wife, sister of Tahpenes the mistress;
20 ’Yar’uwar Tafenes ta haifi masa ɗa wanda ya kira Genubat, wanda Tafenes ta yi renonsa a fadan sarki. A can, Genubat ya yi zama da’ya’yan Fir’auna.
and the sister of Tahpenes bears to him his son Genubath, and Tahpenes weans him within the house of Pharaoh, and Genubath is in the house of Pharaoh in the midst of the sons of Pharaoh.
21 Yayinda yake a Masar, Hadad ya ji Dawuda ya huta tare da kakanninsa, ya kuma ji cewa Yowab shugaban mayaƙa ya mutu. Sai Hadad ya ce wa Fir’auna, “Bari in tafi, don in koma ƙasata.”
And Hadad has heard in Egypt that David has lain with his fathers, and that Joab head of the host is dead, and Hadad says to Pharaoh, “Send me away, and I go to my land.”
22 Fir’auna ya tambaye shi, ya ce, “Me ka rasa a nan da kake so ka koma garinka?” Ya ce, “Ba kome, amma ka dai bar ni in tafi!”
And Pharaoh says to him, “But what are you lacking with me, that behold, you are seeking to go to your own land?” And he says, “Nothing, but you certainly send me away.”
23 Allah kuwa ya tayar wa Solomon wani abokin gāba, mai suna Rezon, ɗan Eliyada, wanda ya gudu daga maigidansa, Hadadezer sarkin Zoba.
And God raises an adversary against him, Rezon son of Eliadah, who has fled from Hadadezer king of Zobah, his lord,
24 Rezon ya tattara mutane kewaye da shi, ya zama kuma shugaban’yan tawaye sa’ad da Dawuda ya hallaka mayaƙan Zoba;’yan tawayen suka tafi Damaskus, inda suka zauna, suka kuma yi mulki.
and gathers men to himself, and is head of a troop in David’s slaying them, and they go to Damascus, and dwell in it, and reign in Damascus;
25 Rezon ya zama babban abokin gāban Isra’ila cikin dukan kwanakin mulkin Solomon. Ya ƙara rikici a kan rikicin Hadad. Rezon ya ƙi mulkin Isra’ila da dukan ransa. Saboda haka Rezon ya yi mulki a Aram ya kuma ƙi jinin Isra’ila.
and he is an adversary against Israel all the days of Solomon (besides the evil that Hadad [did]), and he cuts off in Israel, and reigns over Aram.
26 Haka ma Yerobowam, ɗan Nebat, shi ma ya yi wa sarki tawaye. Shi ɗaya ne daga shugabannin Solomon, shi mutumin Efraim ne daga Zereda, mahaifiyarsa kuwa gwauruwa ce, mai suna Zeruwa.
And Jeroboam son of Nebat, an Ephraimite of Zereda—the name of whose mother [is] Zeruah, a widow woman—servant to Solomon, he also lifts up a hand against the king;
27 Ga yadda ya tayar wa sarki Solomon. Sarki Solomon ya gina madogaran gini, ya ciccika wurare a katangar birnin Dawuda mahaifinsa da ƙasa.
and this [is] the thing [for] which he lifted up a hand against the king: Solomon built Millo—he shut up the breach of the city of his father David,
28 To, Yerobowam mutum ne mai fasaha. Sa’ad da Solomon ya ga yadda matashin yake aiki da himma, sai ya sa shi yă lura da dukan aikin gandu na gidan Yusuf.
and the man Jeroboam [is] mighty in valor, and Solomon sees that the young man is doing business, and appoints him over all the burden of the house of Joseph.
29 Da Yerobowam ya fita Urushalima, sai annabi Ahiya, mutumin Shilo ya tarar da shi a hanya. Lokacin kuwa Ahiya yana saye da sabuwar riga, ba kowa a filin sai su biyu kaɗai.
And it comes to pass, at that time, that Jeroboam has gone out from Jerusalem, and Ahijah the Shilonite, the prophet, finds him in the way, and he is covering himself with a new garment; and both of them [are] by themselves in a field,
30 Sai Ahiya ya kama sabuwar rigar da yake saye da ita ya yage ta gida goma sha biyu.
and Ahijah lays hold on the new garment that [is] on him, and tears it [into] twelve pieces,
31 Sa’an nan ya ce wa Yerobowam, “Ɗauki gida goma wa kanka, gama abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce ke nan, ‘Duba, zan yage masarauta daga hannun Solomon in ba ka kabilu goma.
and says to Jeroboam, “Take ten pieces for yourself, for thus said YHWH, God of Israel: Behold, I am tearing the kingdom out of the hand of Solomon, and have given the ten tribes to you,
32 Amma saboda bawana Dawuda da kuma birnin Urushalima, wadda na zaɓa daga dukan kabilan Isra’ila, zai sami kabila guda.
but he has the one tribe for My servant David’s sake, and for Jerusalem’s sake, the city which I have fixed on, out of all the tribes of Israel,
33 Zan yi wannan domin sun yashe ni, suka kuma yi wa Ashtarot, alliyar Sidoniyawa, da Kemosh, allahn Mowabawa, da kuma Molek, allahn Ammonawa sujada, ba su yi tafiya a hanyoyina ba, ba su kuwa yi abin da yake daidai a idanuna ba, ba su kiyaye farillaina da dokokina kamar yadda Dawuda, mahaifin Solomon ya yi ba.
because they have forsaken Me, and bow themselves to Ashtoreth, goddess of the Zidonians, to Chemosh god of Moab, and to Milcom god of the sons of Ammon, and have not walked in My ways, to do that which [is] right in My eyes, and My statutes and My judgments, like his father David.
34 “‘Amma ba zan ɗauki dukan masarautar daga hannun Solomon ba; na naɗa shi sarki, dukan kwanaki ransa saboda Dawuda bawana, wanda na zaɓa, wanda kuma ya kiyaye umarnai da farillaina.
And I do not take the whole of the kingdom out of his hand, for I make him prince all [the] days of his life, for the sake of My servant David whom I chose, who kept My commands and My statutes;
35 Zan ɗauke masarautar daga hannuwan ɗansa ne, in ba ka kabilu goma.
and I have taken the kingdom out of the hand of his son, and given it to you—the ten tribes;
36 Zan ba da ɗaya ga ɗansa don kullum Dawuda bawana yă kasance da fitila a gabana a Urushalima, birnin da na zaɓa in sa Sunana.
and to his son I give one tribe, for there being a lamp before Me for My servant David in Jerusalem [for] all the days, the city that I have chosen for Myself to put My Name there.
37 Amma fa, ga kai, zan ɗauke ka, za ka kuwa yi mulki bisa dukan abin da zuciyarka take so; za ka zama sarki a bisa Isra’ila.
And I take you, and you have reigned over all that your soul desires, and you have been king over Israel;
38 In ka aikata dukan abin da na umarce ka, ka yi tafiya a hanyoyina, ka kuma yi abin da yake daidai a idanuna ta wurin kiyaye farillaina da umarnaina, kamar yadda Dawuda bawana ya yi, zan kasance tare da kai. Zan gina maka masarauta mai dawwama kamar wadda na gina wa Dawuda, zan kuma ba da Isra’ila gare ka.
and it has been, if you hear all that I command you, and have walked in My ways, and done that which is right in My eyes, to keep My statutes and My commands, as My servant David did, that I have been with you, and have built a steadfast house for you, as I built for David, and have given Israel to you,
39 Zan ƙasƙantar da zuriyar Dawuda saboda wannan, amma ba har abada ba.’”
and I humble the seed of David for this; only, not [for] all the days.”
40 Solomon ya yi ƙoƙari yă kashe Yerobowam, amma Yerobowam ya tsere zuwa Masar, zuwa wurin sarki Shishak, ya zauna a can sai bayan mutuwar Solomon.
And Solomon seeks to put Jeroboam to death, and Jeroboam rises and flees to Egypt, to Shishak king of Egypt, and he is in Egypt until the death of Solomon.
41 Game da sauran ayyukan mulkin Solomon, da dukan abubuwan da ya yi, da hikimar da ya nuna, an rubuta su a littafin tarihin Solomon.
And the rest of the matters of Solomon, and all that he did, and his wisdom, are they not written on the scroll of the matters of Solomon?
42 Solomon ya yi mulki a Urushalima, a bisa dukan Isra’ila, shekaru arba’in.
And the days that Solomon has reigned in Jerusalem over all Israel [are] forty years,
43 Sa’an nan ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a birnin Dawuda mahaifinsa. Sai Rehobowam ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
and Solomon lies with his fathers, and is buried in the city of his father David, and his son Rehoboam reigns in his stead.

< 1 Sarakuna 11 >