< 1 Sarakuna 11 >

1 Sarki Solomon ya ƙaunaci baƙin mata. Ban da’yar Fir’auna, ya auri Mowabawa, Ammonawa, mutanen Edom, Sidoniyawa da Hittiyawa.
Kralj je Salomon - uz kćer faraonovu - volio mnoge žene tuđinke: Moapke, Amonke, Edomke, Sidonke i Hetitkinje,
2 Sun fito daga al’ummai da Ubangiji ya ce wa Isra’ilawa, “Kada ku yi aurayya da su, domin tabbatacce za su juye zukatanku zuwa ga waɗansu alloli.” Duk da haka Solomon ya manne musu, ya nace, yana ƙaunarsu.
od svih naroda za koje je Jahve rekao Izraelcima: “Nećete odlaziti k njima i oni neće dolaziti k vama; oni će zacijelo okrenuti vaša srca svojim bogovima.” Njima se priklonio Salomon svojom ljubavlju.
3 Ya auri mata ɗari bakwai, haifaffun gidan sarauta, da kuma ƙwarƙwarai ɗari uku. Matan nan nasa suka karkatar da shi.
Imao je sedam stotina kneževskih žena i tri stotine inoča. Njegove su žene zavodile njegovo srce.
4 Yayinda Solomon yake tsufa, matansa suka juye zuciyarsa ga bin waɗansu alloli, zuciyarsa kuwa ba tă bi Ubangiji Allahnsa ɗungum kamar yadda zuciyar Dawuda mahaifinsa ta kasance ba.
I kada je Salomon ostario, njegove su mu žene okrenule srce prema drugim bogovima, i srce njegovo nije više potpuno pripadalo Jahvi kao što je pripadalo srce njegova oca Davida.
5 Ya bi Ashtarot, alliyar Sidoniyawa, da Molek, allahn da aka hana na Ammonawa.
Salomon je išao za Aštartom, boginjom Sidonaca, i Milkomom, sramotom Amonaca.
6 Saboda haka Solomon ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji. Bai bi Ubangiji gaba ɗaya kamar yadda Dawuda mahaifinsa ya yi ba.
Činio je ono što ne bijaše pravo u očima Jahvinim i nije se sasvim pokoravao Jahvi kao što se pokoravao njegov otac David.
7 A kan tudu, gabas da Urushalima, Solomon ya gina masujada a can domin Kemosh, allahn da aka hana na Mowab, da Molek, allahn da aka hana na Ammonawa.
Tako sagradi Salomon uzvišicu Kemošu, sramoti Moaba, na gori istočno od Jeruzalema, i Milkomu, sramoti Amonaca.
8 Ya yi haka domin dukan baƙin matansa, waɗanda suka ƙone turare suka kuma miƙa hadayu ga allolinsu.
To učini za sve svoje žene tuđinke, koje su prinosile kad i žrtve svojim bogovima.
9 Ubangiji ya yi fushi da Solomon domin zuciyarsa ya juye daga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya bayyana masa sau biyu.
Jahve se razgnjevi na Salomona jer je okrenuo srce svoje od Jahve, Boga Izraelova, koji mu se bio dvaput javio
10 Ko da yake ya hana Solomon bin waɗansu alloli, Solomon bai kiyaye umarnin Ubangiji ba.
i koji mu je baš tada zabranio štovati druge bogove, ali on nije održao te zapovijedi.
11 Saboda haka Ubangiji ya ce wa Solomon, “Da yake halinka ke nan, ba ka kuma kiyaye alkawarina, da ƙa’idodina da na umarce ka ba, tabbatacce zan yage masarautar daga gare ka, in ba da ita ga ɗaya daga cikin bayinka.
Tada Jahve reče Salomonu: “Kada je tako s tobom te ne držiš moga Saveza i naredaba koje sam ti dao, ja ću sigurno oduzeti od tebe kraljevstvo i dat ću ga jednom od tvojih slugu.
12 Amma saboda Dawuda mahaifinka, ba zan yi haka a zamaninka ba. Zan yage ta daga hannun ɗanka.
Ali neću to učiniti za tvoga života, zbog oca tvojega Davida; uzet ću ga iz ruke tvoga sina.
13 Amma ba zan yage dukan masarautar daga gare shi ba, zan ba shi kabila ɗaya saboda Dawuda bawana, da kuma saboda Urushalima, wadda na zaɓa.”
Ipak neću od njega uzeti svega kraljevstva: ostavit ću jedno pleme tvome sinu, zbog sluge mojega Davida, zbog Jeruzalema koji izabrah.”
14 Sai Ubangiji ya tayar wa Solomon wani abokin gāba, mai suna Hadad, mutumin Edom daga gidan sarautar Edom.
Tada diže Jahve protivnika Salomonu: Edomca Hadada, iz kraljevske kuće Edomaca.
15 A shekarun baya Dawuda ya ci Edom da yaƙi. Yowab, shugaban sojojinsa ya tafi can domin yă binne Isra’ilawa waɗanda suka mutu a yaƙi. Sa’ad da suke a can, sojojin Isra’ila suka kashe kowane ɗa namiji a Edom.
Jer kada je David tukao Edomce i kad je Joab, vojskovođa, otišao da pokopa ubijene i dao pogubiti sve muškarce u Edomu -
16 Yowab da dukan Isra’ilawa suka zauna a can, wata shida, sai da suka hallaka dukan mutane a Edom.
Joab i sav Izrael ostadoše ondje šest mjeseci dok nisu istrijebili sve muškarce u Edomu -
17 Amma Hadad yana ɗan yaro a lokaci, wanda ya gudu zuwa Masar tare da shugabannin mutanen Edom waɗanda suka yi wa mahaifinsa hidima.
Hadad je utekao u Egipat s Edomcima koji bijahu u službi njegova oca. Hadad je bio tada mladi dječak.
18 Suka taso daga Midiyan suka tafi Faran. Sa’an nan suka ɗauki mutane daga Faran suka tafi Masar, zuwa wurin Fir’auna wanda ya ba wa Hadad gida da ƙasa, ya kuma tanada masa da abinci.
Otišli su iz Midjana i stigli u Paran. Poveli su sa sobom ljude iz Parana i otišli u Egipat pred faraona, kralja Egipta, koji mu dade kuću, odredi mu hranu i dodijeli zemlje.
19 Fir’auna ya ji daɗin Hadad har ya ba shi’yar’uwar matarsa, Sarauniya Tafenes, aure.
Hadad je stekao veliku milost u faraona, koji mu dade sestru svoje žene, sestru velike kneginje Tafnese.
20 ’Yar’uwar Tafenes ta haifi masa ɗa wanda ya kira Genubat, wanda Tafenes ta yi renonsa a fadan sarki. A can, Genubat ya yi zama da’ya’yan Fir’auna.
Sestra Tafnesina rodi mu sina Genubata, koga Tafnesa odgoji u kraljevskoj palači, i Genubat je ostao u palači među faraonovom djecom.
21 Yayinda yake a Masar, Hadad ya ji Dawuda ya huta tare da kakanninsa, ya kuma ji cewa Yowab shugaban mayaƙa ya mutu. Sai Hadad ya ce wa Fir’auna, “Bari in tafi, don in koma ƙasata.”
Kada je Hadad doznao u Egiptu da je David počinuo kod svojih otaca i da je vojskovođa Joab umro, reče faraonu: “Dopusti mi da odem u svoju zemlju!”
22 Fir’auna ya tambaye shi, ya ce, “Me ka rasa a nan da kake so ka koma garinka?” Ya ce, “Ba kome, amma ka dai bar ni in tafi!”
Faraon mu reče: “Što ti nedostaje u mene te želiš poći u svoju zemlju?” A on mu odgovori: “Ništa, ali me pusti da odem!” [25b] To je bilo zlo što ga je učinio Hadad: mrzio je Izraela i vladao je Edomom.
23 Allah kuwa ya tayar wa Solomon wani abokin gāba, mai suna Rezon, ɗan Eliyada, wanda ya gudu daga maigidansa, Hadadezer sarkin Zoba.
Bog je protiv Salomona podigao protivnika mu Rezona, sina Elijadova, koji je pobjegao od svoga gospodara Hadadezera, kralja sopskoga;
24 Rezon ya tattara mutane kewaye da shi, ya zama kuma shugaban’yan tawaye sa’ad da Dawuda ya hallaka mayaƙan Zoba;’yan tawayen suka tafi Damaskus, inda suka zauna, suka kuma yi mulki.
Rezon je skupio ljude oko sebe i postao im četovođa kada ih David ubijaše. Rezon zauze Damask, ondje se nastani i zavlada Damaskom.
25 Rezon ya zama babban abokin gāban Isra’ila cikin dukan kwanakin mulkin Solomon. Ya ƙara rikici a kan rikicin Hadad. Rezon ya ƙi mulkin Isra’ila da dukan ransa. Saboda haka Rezon ya yi mulki a Aram ya kuma ƙi jinin Isra’ila.
[25a] On je bio protivnik Izraelov za života Salomonova.
26 Haka ma Yerobowam, ɗan Nebat, shi ma ya yi wa sarki tawaye. Shi ɗaya ne daga shugabannin Solomon, shi mutumin Efraim ne daga Zereda, mahaifiyarsa kuwa gwauruwa ce, mai suna Zeruwa.
Jeroboam bijaše sin Efraćanina Nebata, iz Sareda, a majka mu bijaše udovica imenom Serva. On je bio u službi Salomonovoj i podigao je ruku protiv kralja.
27 Ga yadda ya tayar wa sarki Solomon. Sarki Solomon ya gina madogaran gini, ya ciccika wurare a katangar birnin Dawuda mahaifinsa da ƙasa.
Evo razloga njegove pobune. Salomon je gradio Milo da zatrpa kosinu u gradu Davida, oca svoga.
28 To, Yerobowam mutum ne mai fasaha. Sa’ad da Solomon ya ga yadda matashin yake aiki da himma, sai ya sa shi yă lura da dukan aikin gandu na gidan Yusuf.
Taj Jeroboam bijaše valjan čovjek; Salomon opazi kako se mladi čovjek prihvaća posla i postavi ga nad svom rabotom kuće Josipove.
29 Da Yerobowam ya fita Urushalima, sai annabi Ahiya, mutumin Shilo ya tarar da shi a hanya. Lokacin kuwa Ahiya yana saye da sabuwar riga, ba kowa a filin sai su biyu kaɗai.
Tada se dogodi te Jeroboam ode iz Jeruzalema, i na putu ga susrete prorok Ahija iz Šila, ogrnut novim plaštem; bijahu sami njih dvojica u polju.
30 Sai Ahiya ya kama sabuwar rigar da yake saye da ita ya yage ta gida goma sha biyu.
Ahija uze novi plašt koji je imao na sebi i razdrije ga na dvanaest komada.
31 Sa’an nan ya ce wa Yerobowam, “Ɗauki gida goma wa kanka, gama abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce ke nan, ‘Duba, zan yage masarauta daga hannun Solomon in ba ka kabilu goma.
I reče Jeroboamu: “Uzmi sebi deset komada, jer ovako govori Jahve, Bog Izraelov: 'Evo ću istrgnuti kraljevstvo iz ruke Salomonove i dat ću tebi deset plemena.
32 Amma saboda bawana Dawuda da kuma birnin Urushalima, wadda na zaɓa daga dukan kabilan Isra’ila, zai sami kabila guda.
On će imati jedno pleme, zbog sluge mojega Davida i Jeruzalema, grada koji sam izabrao između svih plemena Izraelovih.
33 Zan yi wannan domin sun yashe ni, suka kuma yi wa Ashtarot, alliyar Sidoniyawa, da Kemosh, allahn Mowabawa, da kuma Molek, allahn Ammonawa sujada, ba su yi tafiya a hanyoyina ba, ba su kuwa yi abin da yake daidai a idanuna ba, ba su kiyaye farillaina da dokokina kamar yadda Dawuda, mahaifin Solomon ya yi ba.
To je zato što me ostavio i poklonio se Aštarti, boginji Sidonaca, Kemošu, bogu moapskom, i Milkomu, bogu Amonaca, i ne hodi više mojim putovima; ne čini što je pravo u mojim očima, niti izvršava moje zakone i naredbe kao što je činio njegov otac David.
34 “‘Amma ba zan ɗauki dukan masarautar daga hannun Solomon ba; na naɗa shi sarki, dukan kwanaki ransa saboda Dawuda bawana, wanda na zaɓa, wanda kuma ya kiyaye umarnai da farillaina.
Ali mu neću iz ruke uzeti sve kraljevstvo, jer sam ga postavio knezom za sveg njegova života, zbog sluge svoga Davida, koga sam izabrao i koji je držao moje zapovijedi i moje zakone.
35 Zan ɗauke masarautar daga hannuwan ɗansa ne, in ba ka kabilu goma.
Ali ću uzeti kraljevstvo iz ruke njegova sina i tebi ću ga dati, to jest deset plemena.
36 Zan ba da ɗaya ga ɗansa don kullum Dawuda bawana yă kasance da fitila a gabana a Urushalima, birnin da na zaɓa in sa Sunana.
A njegovu ću sinu ostaviti jedno pleme da moj sluga David ima uvijek svjetiljku preda mnom u Jeruzalemu, gradu koji sam izabrao sebi da u njemu stoluje Ime moje.
37 Amma fa, ga kai, zan ɗauke ka, za ka kuwa yi mulki bisa dukan abin da zuciyarka take so; za ka zama sarki a bisa Isra’ila.
Tebe ću uzeti da kraljuješ nad svim što budeš želio i da budeš kralj nad Izraelom.
38 In ka aikata dukan abin da na umarce ka, ka yi tafiya a hanyoyina, ka kuma yi abin da yake daidai a idanuna ta wurin kiyaye farillaina da umarnaina, kamar yadda Dawuda bawana ya yi, zan kasance tare da kai. Zan gina maka masarauta mai dawwama kamar wadda na gina wa Dawuda, zan kuma ba da Isra’ila gare ka.
Ako budeš poslušao sve što ti zapovjedim i stupao budeš putovima mojim te činio što je pravedno u očima mojim držeći moje zakone i zapovijedi moje, kako je to činio moj sluga David, tada ću ja biti s tobom i sagradit ću ti trajan dom, kao što sam sagradio Davidu, i dat ću ti Izraela.
39 Zan ƙasƙantar da zuriyar Dawuda saboda wannan, amma ba har abada ba.’”
Ponizit ću potomke Davidove; ali ne zauvijek.'”
40 Solomon ya yi ƙoƙari yă kashe Yerobowam, amma Yerobowam ya tsere zuwa Masar, zuwa wurin sarki Shishak, ya zauna a can sai bayan mutuwar Solomon.
Salomon je zato tražio da ubije Jeroboama, ali on pobježe u Egipat k Šišaku i ostade u Egiptu do smrti Salomonove.
41 Game da sauran ayyukan mulkin Solomon, da dukan abubuwan da ya yi, da hikimar da ya nuna, an rubuta su a littafin tarihin Solomon.
Ostala povijest Salomonova, sve što je učinio i njegova mudrost, zar nije zapisana u knjizi Povijesti Salomonove?
42 Solomon ya yi mulki a Urushalima, a bisa dukan Isra’ila, shekaru arba’in.
A kraljevaše Salomon u Jeruzalemu nad svim Izraelom četrdeset godina.
43 Sa’an nan ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a birnin Dawuda mahaifinsa. Sai Rehobowam ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Onda počinu Salomon kod otaca svojih i bi sahranjen u Davidovu gradu, a njegov sin Roboam zakralji se namjesto njega.

< 1 Sarakuna 11 >