< 1 Sarakuna 1 >

1 Sa’ad da Sarki Dawuda ya tsufa ya kuma ƙara shekaru, ba ya iya jin ɗumi ko an rufe shi da abin rufuwa.
And kyng Dauid wax eld, and hadde ful many daies of age; and whanne he was hilid with clothis, he was not maad hoot.
2 Saboda haka bayinsa suka ce masa, “Bari mu nemi wata budurwa wadda za tă yi wa ranka yă daɗe, sarki hidima, tă kuma kula da shi. Za tă dinga kwanta kusa da ranka yă daɗe, yă ji ɗumi.”
Therfor hise seruauntis seiden to hym, Seke we to oure lord the kyng a yong wexynge virgyn; and stonde sche bifor the kyng, and nursche sche hym, and slepe in his bosum, and make hoot oure lord the kyng.
3 Suka nemi kyakkyawar yarinya cikin fāɗin Isra’ila, sai suka sami Abishag, mutuniyar Shunam, suka kawo ta wa sarki.
Therfor thei souyten a yong wexyng virgyn, fair in alle the coostis of Israel; and thei founden Abisag of Sunam, and thei brouyten hir to the kyng.
4 Yarinyar kuwa kyakkyawa ce ƙwarai; ta kuwa lura da sarki, ta kuma yi masa hidima, amma sarki bai yi jima’i da ita ba.
Forsothe the damysel was ful fair, and sche slepte with the kyng, and mynystride to hym; forsothe the king knew not hir fleischli.
5 Adoniya, wanda mahaifiyarsa ce Haggit, ya fito ya ce, “Zan zama sarki.” Saboda haka ya nemi kekunan yaƙi, ya kuma shirya dawakai, tare da mutane hamsin da za su sha gabansa.
Sotheli Adonye, sone of Agith, was reisid, and seide, Y schal regne. And he made to hym a chare, and knyytis, and fifti men, that runnen bifor hym.
6 (A duk rayuwarsa mahaifinsa bai taɓa tsawata masa yă ce, “Me ya sa kake yin haka ba?” Shi kuwa mai kyan gani ne ƙwarai, shi ne aka haifa bayan Absalom.)
Nether his fadir repreuyde hym ony tyme, and seide, Whi `didist thou this? Forsothe also he was ful fair, the secounde child aftir Absolon; and his word was with Joab,
7 Adoniya ya haɗa baƙi da Yowab ɗan Zeruhiya da kuma Abiyatar firist, suka kuma ba shi goyon baya.
sone of Saruye, and with `Abiathar, preest, that helpiden the partis of Adonye.
8 Amma Zadok firist, Benahiya ɗan Yehohiyada, annabi Natan, Shimeyi, Reyi da kuma matsara na musamman na Dawuda ba su bi Adoniya ba.
Sotheli Sadoch, the preest, and Banaie, sone of Joiada, and Nathan, the prophete, and Semey, and Cerethi, and Ferethi, and al the strengthe of the oost of Dauid, weren not with Adonye.
9 Wata rana Adoniya ya tafi Dutsen Zohelet kusa da En Rogel, inda ya yi hadayar tumaki, da shanun noma, da shanun da ake kiwo a gida. Ya kuma gayyaci’yan’uwansa, wato, sauran’ya’yan Sarki Dawuda, tare da dukan dattawan sarki da suka fito daga Yahuda,
Therfor whanne rammes weren offrid, and caluys, and alle fatte thingis, bisidis the stoon Zoelech, that was nyy the welle of Rogel, Adonye clepide alle hise britheren, sones of the kyng, and alle the men of Juda, seruauntis of the kyng.
10 amma bai gayyaci annabi Natan, ko Benahiya, ko wani daga matsara na musamman, ko kuwa ɗan’uwansa Solomon ba.
Sotheli `he clepide not Nathan, the profete, and Banaie, and alle stronge men, and Salomon, his brothir.
11 Sai Natan ya ce wa Batsheba, mahaifiyar Solomon, “Ki san cewa Adoniya, ɗan Haggit, ya zama sarki ba tare da sanin ranka yă daɗe, sarkinmu Dawuda ba?
Therfor Nathan seide to Bersabee, modir of Salomon, Whether thou herdist, that Adonye, sone of Agith, regnede, and oure lord Dauid knoweth not this?
12 Yanzu bari in ba ki shawara yadda za ki cece ranki da kuma ran ɗanki Solomon.
Now therfor come thou, take thou counsel of me, and saue thi lijf, and of Salomon thi sone.
13 Ki shiga wurin Sarki Dawuda ki ce masa, ‘Ranka yă daɗe sarki, ba ka rantse mini ni baiwarka cewa, “Tabbatacce Solomon ɗanka ne zai zama sarki bayana, yă kuma zauna a kujerar sarautar ba”? To, me ya sa Adoniya ya zama sarki?’
Go thou, and entre to kyng Dauid, and seie thou to hym, Whether not thou, my lord the kyng, hast swore to me, thin handmaide, and seidist, that Salomon thi sone schal regne aftir me, and he schal sitte in my trone?
14 Yayinda kike can kina magana da sarki, zan shiga in kuma tabbatar da abin da kika faɗa.”
Whi therfor regneth Adonye? And yit while thou schalt speke there with the kyng, Y schal come aftir thee, and `Y schal fille thi wordis.
15 Saboda haka Batsheba ta je don tă ga sarki. A yanzu dai sarki ya tsufa, yana nan kuma a cikin ɗakinsa, inda Abishag mutuniya Shunam take masa hidima.
Therfor Bersabee entride to the kyng in the closet; forsothe the kyng was ful eeld, and Abisag of Sunam `mynystride to hym.
16 Batsheba ta rusuna ta kuma durƙusa a gaban sarki. Sai sarki ya tambaye ta ya ce, “Me kike so?”
Bersabee bowide hir silf, and worschipide the kyng; to whom the kyng seide, What wolt thou to thee?
17 Ta ce masa, “Ranka yă daɗe, kai kanka ka rantse mini ni baiwarka da sunan Ubangiji Allahnka cewa, ‘Solomon ɗanka zai zama sarki bayana, zai kuma zauna a kujerar sarautata.’
And sche answeride, and seide, My lord the kyng, thou hast swore to thin handmaide bi thi Lord God, Salomon thy sone schal regne aftir me, and he schal sitte in my trone;
18 Amma yanzu Adoniya ya zama sarki, kai kuwa ranka yă daɗe sarki, ba ka san wani abu game da shi ba.
and lo! Adonye hath regnede now, `while thou, my lord the kyng, knowist not;
19 Ya miƙa hadayun shanu, da shanun da ake kiwo a gida, da tumaki masu yawa, ya kuma gayyaci dukan’ya’yan sarki maza, da Abiyatar firist, da Yowab shugaban mayaƙa, amma bai gayyaci Solomon bawanka ba.
he hath slayn oxis, and alle fatte thingis, and ful many rammes; and he clepide alle the sones of the king, also `Abiathar preest, and Joab, the prince of chyualri; but he clepide not Salomon, thi seruaunt.
20 Ranka yă daɗe sarki, idanun dukan Isra’ila suna a kanka, domin su san wa zai zauna a kujerar ranka yă daɗe sarkina, a bayanka.
Netheles, my lord the kyng, the iyen of al Israel biholden in to thee, that thou schewe to hem, who owith to sitte in thi trone, my lord the kyng, aftir thee;
21 In ba haka, bayan an binne ranka yă daɗe sarki, tare da kakanninsa, za a wulaƙance ni da Solomon ɗana, kamar masu laifi.”
and it schal be, whanne my lord the kyng hath slepte with hise fadris, Y and my sone Salomon schulen be synneris.
22 Yayinda take cikin magana tare da sarki, sai annabi Natan ya iso.
`While sche spak yit with the king, Nathan, the prophete, cam.
23 Sai aka faɗa wa sarki, “Ga annabi Natan.” Da Natan ya je gaban sarki, sai ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
And thei telden to the kyng, and seiden, Nathan, the prophete, is present. And whanne he hadde entrid in the siyt of the kyng, and hadde worschipide hym lowli to erthe,
24 Natan ya ce, “Ranka yă daɗe, sarki, ko ka furta cewa Adoniya ne zai zama sarki a bayanka, yă kuma zauna a kujerar sarautarka?
Nathan seide, My lord the kyng, seidist thou, Adonye regne aftir me, and sitte he on my trone?
25 Yau ya gangara, ya kuma miƙa hadayun shanu, da shanun da ake kiwo a gida, da tumaki masu yawa. Ya gayyaci dukan’ya’yan sarki maza, da shugaban mayaƙa, da kuma Abiyatar firist. A yanzu haka suna ci, suna sha, tare da shi, suna cewa, ‘Ran Sarki Adoniya yă daɗe!’
For he cam doun to dai, and offride oxis, and fatte thingis, and ful many wetheris; and he clepide alle the sones of the kyng, also Abiathar, preest; and whanne thei eten, and drunken bifor hym, and seiden, Kyng Adonye lyue;
26 Amma bai gayyace ni bawanka, da Zadok firist, da Benahiya ɗan Yehohiyada, da kuma bawanka Solomon ba.
he clepide not me, thi seruaunt, and Sadoch, preest, and Banaie, sone of Joiada, and Salomon, thi sone.
27 Ranka yă daɗe, sarki, ko ka tabbatar da haka, amma ba ka ko faɗa wa fadawanka, cewa ga wanda zai gāje Ranka yă daɗe, sarki ba?”
Whether this word yede out fro my lord the kyng, and thou schewidist not to me, thi seruaunt, who schulde sitte on the trone of my lord the king after hym?
28 Sai Dawuda ya ce, “Kira Batsheba tă shiga.” Sai ta zo gaban sarki ta kuma tsaya a gabansa.
And kyng Dauid answeride, and seide, Clepe ye Bersabee to me. And whanne sche hadde entrid bifor the kyng, and hadde stonde bifor hym, the kyng swoor,
29 Sai sarki ya yi rantsuwa, “Muddin Ubangiji yana a raye, wanda ya cece ni daga kowace damuwa,
and seide, The Lord lyueth, that delyueryde my lijf fro al angwisch;
30 tabbatacce a yau zan aikata abin da na yi miki rantsuwa da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila; Solomon ɗanki zai zama sarki bayana, kuma shi zai zauna a kan kujerar sarautata a maimakona.”
for as Y swore to thee bi the Lord God of Israel, and seide, Salomon, thi sone, schal regne after me, and he schal sitte on my trone for me, so Y schal do to dai.
31 Sai Batsheba ta rusuna da fuskarta har ƙasa, ta kuma durƙusa a gaban sarki ta ce, “Bari ran Sarkina Dawuda yă daɗe, har abada!”
And Bersabee, with the cheer cast doun in to erthe, worschipide the kyng, and seide, My lord the kyng Dauid lyue with outen ende.
32 Sarki Dawuda ya ce, “Ku kira mini Zadok firist, annabi Natan, da Benahiya ɗan Yehohiyada.” Da suka zo gaban sarki,
And kyng Dauid seide, Clepe ye Sadoch, the preest, to me, and Nathan, the prophete, and Banaie, sone of Joiada. And whanne thei hadden entrid bifor the kyng,
33 sai ya ce musu, “Ku ɗauki bayin sarki tare da ku, ku kuma sa ɗana Solomon a kan dokina, ku gangara da shi zuwa Gihon.
the kyng seide to hem, Take with you the seruauntis of youre lord, and putte ye my sone Salomon on my mule, and lede ye hym in to Gyon.
34 A can ku sa Zadok firist, da annabi Natan su shafe shi sarki a bisa Isra’ila. Ku busa ƙaho, ku kuma yi ihu, kuna cewa, ‘Ran Sarki Solomon yă daɗe!’
And Sadoch, the preest, and Nathan, the profete, anoynte hym in to kyng on Israel and Juda; and ye schulen synge with a clarioun, and ye schulen seie, Lyue kyng Salomon!
35 Sa’an nan ku haura tare da shi, zai kuwa zo yă zauna a kujera sarautata, yă yi mulki a maimakona. Na naɗa shi mai mulki a bisa Isra’ila da Yahuda.”
Ye schulen stie aftir hym, and ye schulen come to Jerusalem; and he schal sitte on my trone, and he schal regne for me; and Y schal comaunde to hym, that he be duyk on Israel and on Juda.
36 Benahiya ɗan Yehohiyada ya amsa wa sarki, ya ce, “Amin! Bari Ubangiji Allah na ranka yă daɗe sarkina, yă tabbatar da haka.
And Banaie, sone of Joiada, answeride to the kyng, and seide, Amen, `that is, so be it, ether verili, ether feithfuli; so speke the Lord God of my lord the kyng.
37 Kamar yadda Ubangiji ya kasance da ranka yă daɗe, sarki, haka ma bari yă kasance da Solomon, yă kuma mai da kujerar sarautarsa tă fi kujerar sarautar ranka yă daɗe, Sarki Dawuda, girma!”
As the Lord was with my lord the kyng, so be he with Salomon, and make he the trone of Salomon heiyere than the trone of my lord the kyng Dauid.
38 Sai Zadok firist, annabi Natan, Benahiya ɗan Yehohiyada, Keretawa, da Feletiyawa suka gangara, suka sa Solomon a kan dokin Sarki Dawuda, suka raka shi zuwa Gihon.
Therfor Sadoch, the preest, yede doun, and Nathan, the prophete, and Banaie, sone of Joiada, and Cerethi, and Ferethi; and thei puttiden Salomon on the mule of Dauid, the kyng, and thei brouyten hym in to Gion.
39 Zadok firist ya ɗauki ƙahon mai daga tenti mai tsarki, ya shafe Solomon. Sa’an nan suka busa ƙaho, sai dukan mutane suka yi ihu, suna cewa “Ran Sarki Solomon yă daɗe!”
And Sadoch, the preest, took an horn of oile of the tabernacle, and anoyntide Salomon; and thei sungen with a clarioun; and al the puple seide, Lyue kyng Salomon!
40 Dukan mutane kuwa suka haura suka bi shi, suna busan sarewa, suna farin ciki sosai, har ƙasa ta girgiza saboda sowa.
And al the multitude stiede after hym, and the puple of men syngynge with pipis, and `of men beynge glad with greet ioye, `stiede aftir hym; and the erthe sownede of the cry of hem.
41 Adoniya tare da dukan baƙin da suke tare da shi kuwa suka ji wannan sa’ad da suke gama bikinsu. Da jin busan ƙaho, sai Yowab ya yi tambaya, ya ce, “Me ya jawo surutu haka a birni?”
Forsothe Adonye herde, and alle that weren clepid of hym to feeste; and thanne the feeste was endid. But also Joab seide, whanne the vois of trumpe was herd, What wole it to it silf the cry of the citee makynge noise?
42 Tun yana cikin magana, sai Yonatan ɗan Abiyatar ya iso. Adoniya ya ce, “Shigo! Ai, mutumin kirki irinka, lalle ka kawo labari mai daɗi ne.”
Yit the while he spak, Jonathan, sone of Abiathar, the preest, cam; to whom Adonye seide, Entre thou, for thou art a strong man, and tellynge goode thingis.
43 Yonatan ya ce wa Adoniya, “A ina! Ranka yă daɗe, Sarkinmu Dawuda ya naɗa Solomon sarki.
And Jonathan answeride to Adonye, Nay; for oure lord the kyng Dauid hath ordeyned Salomon kyng;
44 Sarki ya aika shi tare da Zadok firist, annabi Natan, Benahiya ɗan Yehohiyada, Keretawa, da Feletiyawa, suka sa shi a kan dokin sarki,
and Dauid sente with Salomon Sadoch, the preest, and Nathan, the prophete, and Banaie, sone of Joiada, and Cerethi, and Ferethi; and thei puttiden Salomon on the mule of the kyng.
45 Zadok firist kuwa da annabi Natan sun shafe shi sarki a Gihon. Daga can suka haura suna kirari, birni kuwa ta ɓarke da sowa. Surutun da kake ji ke nan.
And Sadoch, the preest, and Nathan, the prophete, anoyntiden hym kyng in Gion; and thei camen doun fro thennus beynge glad, and the citee sownede; this is the vois which ye herden.
46 Ban da haka ma, Solomon ne sarki yanzu.
But also Salomon sittith on the trone of rewme;
47 Yanzu haka, fadawa sun zo suna wa ranka yă daɗe, Sarki Dawuda, sam barka, suna cewa, ‘Bari Allahnka yă sa sunan Solomon yă zama sananne fiye da naka, bari kuma sarautarsa tă fi taka girma!’ Sarki kuwa ya rusuna, ya yi sujada a kan gadonsa
and the seruauntis of the kyng entriden, and blessiden oure lord the kyng Dauid, and seiden, God make large the name of Salomon aboue thi name, and magnyfye his trone aboue thi trone. And kyng Dauid worschipide in his bed;
48 ya ce, ‘Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya bar idanuna suka ga magāji a kan kujerar sarautata a yau.’”
and ferthermore he spak these thingis, Blessid be the Lord God of Israel, that yaf to dai a sittere in my trone, while myn iyen seen.
49 A nan fa, dukan baƙin Adoniya suka taso da rawar jiki suka watse.
Therfor alle, that weren clepid of Adonye to feeste, weren aferd, and risiden, and ech man yede in to his weie.
50 Amma Adoniya, don tsoron Solomon, ya je ya kama ƙahon bagade ya riƙe.
Sotheli Adonye dredde Salomon, and roos, and yede in to the tabernacle of the Lord, and helde the horn of the auter.
51 Sa’ad da aka faɗa wa Solomon cewa, “Adoniya yana tsoron Sarki Solomon, kuma ya manne wa ƙahonin bagade. Yana cewa, ‘Bari Sarki Solomon yă rantse mini a yau cewa ba zai kashe bawansa da takobi ba.’”
And thei telden to Salomon, and seiden, Lo! Adonye dredith the kyng Salomon, and holdith the horn of the auter, and seith, Kyng Salomon swere to me to dai, that he schal not sle his seruaunt bi swerd.
52 Solomon ya amsa ya ce, “In ya nuna kansa mai biyayya, ba gashin kansa da zai fāɗi ƙasa; amma in aka same mugunta a cikinsa, zai mutu.”
And Salomon seide, If he is a good man, sotheli not oon heer of hym schal falle in to erthe; but if yuel be foundun in hym, he schal die.
53 Sai Sarki Solomon ya aiki mutane, suka kuma sauko da shi daga bagade. Adoniya kuwa ya zo, ya rusuna wa Sarki Solomon, sai Solomon ya ce, “Tafi gidanka.”
Therfor kyng Salomon sente, and ledde `hym out fro the auter; and he entride, and worschipide kyng Salomon; and Salomon seide to hym, Go in to thin hows.

< 1 Sarakuna 1 >