< 1 Sarakuna 1 >

1 Sa’ad da Sarki Dawuda ya tsufa ya kuma ƙara shekaru, ba ya iya jin ɗumi ko an rufe shi da abin rufuwa.
When King David was very old [IDM, DOU], even though his servants put many blankets on top of him, he was unable to become warm.
2 Saboda haka bayinsa suka ce masa, “Bari mu nemi wata budurwa wadda za tă yi wa ranka yă daɗe, sarki hidima, tă kuma kula da shi. Za tă dinga kwanta kusa da ranka yă daɗe, yă ji ɗumi.”
So they said to him, “Your Majesty, allow us to search for a young virgin who can stay with you and take care of you. She can sleep close to you and enable you to become warm.”
3 Suka nemi kyakkyawar yarinya cikin fāɗin Isra’ila, sai suka sami Abishag, mutuniyar Shunam, suka kawo ta wa sarki.
[The king gave them permission, ] so they searched throughout Israel for a beautiful young woman. They found a woman named Abishag, from Shunem [town], and brought her to the king.
4 Yarinyar kuwa kyakkyawa ce ƙwarai; ta kuwa lura da sarki, ta kuma yi masa hidima, amma sarki bai yi jima’i da ita ba.
She was [truly] very beautiful. She took care of [DOU] the king, but the king did not have sexual relations with her.
5 Adoniya, wanda mahaifiyarsa ce Haggit, ya fito ya ce, “Zan zama sarki.” Saboda haka ya nemi kekunan yaƙi, ya kuma shirya dawakai, tare da mutane hamsin da za su sha gabansa.
[After Absalom died], David’s oldest surviving son was Adonijah, whose mother was Haggith. He was a very handsome/good-looking man. But David had never rebuked him about anything he did. [After Absalom died, Adonijah thought that he would become king]. So he started to boast, saying “I will become king [now].” Then he provided for himself some chariots, and men to drive them, and horses [to pull them], and 50 men to run [as his bodyguards] in front of those chariots [wherever he went].
6 (A duk rayuwarsa mahaifinsa bai taɓa tsawata masa yă ce, “Me ya sa kake yin haka ba?” Shi kuwa mai kyan gani ne ƙwarai, shi ne aka haifa bayan Absalom.)
7 Adoniya ya haɗa baƙi da Yowab ɗan Zeruhiya da kuma Abiyatar firist, suka kuma ba shi goyon baya.
One day he conferred with Joab, [David’s army commander], and Abiathar the priest, and they promised/agreed to help/support Adonijah.
8 Amma Zadok firist, Benahiya ɗan Yehohiyada, annabi Natan, Shimeyi, Reyi da kuma matsara na musamman na Dawuda ba su bi Adoniya ba.
But Zadok, who was also a priest, Benaiah [who had supervised David’s bodyguards], Nathan the prophet, Shimei and Rei, and David’s most capable soldiers refused to help/support Adonijah.
9 Wata rana Adoniya ya tafi Dutsen Zohelet kusa da En Rogel, inda ya yi hadayar tumaki, da shanun noma, da shanun da ake kiwo a gida. Ya kuma gayyaci’yan’uwansa, wato, sauran’ya’yan Sarki Dawuda, tare da dukan dattawan sarki da suka fito daga Yahuda,
One day Adonijah went to Snake Rock near En-Rogel [Spring, which is near Jerusalem], to sacrifice some sheep and oxen and fattened cattle. He invited most of his brothers, King David’s other sons, to come. He also invited all of the king’s officials from Judah to come to the celebration.
10 amma bai gayyaci annabi Natan, ko Benahiya, ko wani daga matsara na musamman, ko kuwa ɗan’uwansa Solomon ba.
But he did not invite Nathan or Benaiah or the king’s most capable soldiers or his [younger/half]-brother Solomon.
11 Sai Natan ya ce wa Batsheba, mahaifiyar Solomon, “Ki san cewa Adoniya, ɗan Haggit, ya zama sarki ba tare da sanin ranka yă daɗe, sarkinmu Dawuda ba?
Nathan [found out what they were doing, so he went to] Solomon’s mother Bathsheba [and] asked her, “Have you not heard that Haggith’s son Adonijah is declared himself to be the king? And King David does not know about it!
12 Yanzu bari in ba ki shawara yadda za ki cece ranki da kuma ran ɗanki Solomon.
So if you want to save yourself and your son Solomon from being killed, allow me to tell you what you should do.
13 Ki shiga wurin Sarki Dawuda ki ce masa, ‘Ranka yă daɗe sarki, ba ka rantse mini ni baiwarka cewa, “Tabbatacce Solomon ɗanka ne zai zama sarki bayana, yă kuma zauna a kujerar sarautar ba”? To, me ya sa Adoniya ya zama sarki?’
Go immediately to King David. Say to him, ‘Your Majesty, you solemnly promised me [RHQ] that my son Solomon would become the king after you [die], and that he would sit on your throne [and rule]. So why is it that Adonijah [has said that he] is now the king?’
14 Yayinda kike can kina magana da sarki, zan shiga in kuma tabbatar da abin da kika faɗa.”
Then, while you are still talking to the king, I will come in and tell him that what you are saying to him [about Adonijah] is true.”
15 Saboda haka Batsheba ta je don tă ga sarki. A yanzu dai sarki ya tsufa, yana nan kuma a cikin ɗakinsa, inda Abishag mutuniya Shunam take masa hidima.
So Bathsheba went to see the king in his bedroom. He was very old, and Abishag was taking care of him.
16 Batsheba ta rusuna ta kuma durƙusa a gaban sarki. Sai sarki ya tambaye ta ya ce, “Me kike so?”
Bathsheba bowed very low in front of the king, and the king asked her, “What do you want?”
17 Ta ce masa, “Ranka yă daɗe, kai kanka ka rantse mini ni baiwarka da sunan Ubangiji Allahnka cewa, ‘Solomon ɗanka zai zama sarki bayana, zai kuma zauna a kujerar sarautata.’
She replied, “Your Majesty, you solemnly promised me, knowing that Yahweh our God [was listening] [IDM], that my son Solomon would become king after you [die], and that he would sit on your throne [and rule].
18 Amma yanzu Adoniya ya zama sarki, kai kuwa ranka yă daɗe sarki, ba ka san wani abu game da shi ba.
But now, believe it or not, Adonijah has become king, and you do not know anything about it.
19 Ya miƙa hadayun shanu, da shanun da ake kiwo a gida, da tumaki masu yawa, ya kuma gayyaci dukan’ya’yan sarki maza, da Abiyatar firist, da Yowab shugaban mayaƙa, amma bai gayyaci Solomon bawanka ba.
He has sacrificed a lot of oxen and fattened cattle and sheep, and he has invited all of your other sons to the celebration. He has also invited Abiathar the priest and Joab the commander of your army, but he did not invite your son Solomon.
20 Ranka yă daɗe sarki, idanun dukan Isra’ila suna a kanka, domin su san wa zai zauna a kujerar ranka yă daɗe sarkina, a bayanka.
Your Majesty, all the people [SYN] of Israel are expecting you to tell them who is the one who will become king after you are no longer the king.
21 In ba haka, bayan an binne ranka yă daɗe sarki, tare da kakanninsa, za a wulaƙance ni da Solomon ɗana, kamar masu laifi.”
If you do not do that, what will happen is that after you die [EUP] people will consider that my son Solomon and I are rebelling, [and they will execute us because we did not help Adonijah to become king].”
22 Yayinda take cikin magana tare da sarki, sai annabi Natan ya iso.
While she was still talking to the king, Nathan came [to the palace].
23 Sai aka faɗa wa sarki, “Ga annabi Natan.” Da Natan ya je gaban sarki, sai ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
The king’s servants/advisors told David, “Nathan the prophet has come.” So [Bathsheba left, and] Nathan went into where the king was and knelt down, with his face on the ground.
24 Natan ya ce, “Ranka yă daɗe, sarki, ko ka furta cewa Adoniya ne zai zama sarki a bayanka, yă kuma zauna a kujerar sarautarka?
Then Nathan said, “Your Majesty, have you declared that Adonijah will become king after you are no longer the king?
25 Yau ya gangara, ya kuma miƙa hadayun shanu, da shanun da ake kiwo a gida, da tumaki masu yawa. Ya gayyaci dukan’ya’yan sarki maza, da shugaban mayaƙa, da kuma Abiyatar firist. A yanzu haka suna ci, suna sha, tare da shi, suna cewa, ‘Ran Sarki Adoniya yă daɗe!’
[I say that] because today he has gone down [to En-Rogel Spring] and has sacrificed a lot of oxen, fattened cattle, and sheep. And he has invited all of your other sons, Joab the army commander, and Abiathar the priest. They are all eating and drinking with him and saying ‘We hope/desire that King Adonijah will live a long time!’
26 Amma bai gayyace ni bawanka, da Zadok firist, da Benahiya ɗan Yehohiyada, da kuma bawanka Solomon ba.
But he did not invite me or Zadok the priest or Benaiah or Solomon.
27 Ranka yă daɗe, sarki, ko ka tabbatar da haka, amma ba ka ko faɗa wa fadawanka, cewa ga wanda zai gāje Ranka yă daɗe, sarki ba?”
Did you, as the king, say that they should do this without telling your other officials who you want to become king [MTY] after you are no longer the king?”
28 Sai Dawuda ya ce, “Kira Batsheba tă shiga.” Sai ta zo gaban sarki ta kuma tsaya a gabansa.
Then [after Nathan left the room, ] King David said [to one of his servants], “Tell Bathsheba to come in here again.” So [he went and told her, and] she came in and stood in front of the king.
29 Sai sarki ya yi rantsuwa, “Muddin Ubangiji yana a raye, wanda ya cece ni daga kowace damuwa,
Then the king said, “Yahweh has rescued me from all my troubles. I promised you, with Yahweh the God whom we Israelis [worship] listening, that your son Solomon would be king after I am no longer the king. Today, as surely as Yahweh lives, [I solemnly declare that] I will do what I promised.”
30 tabbatacce a yau zan aikata abin da na yi miki rantsuwa da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila; Solomon ɗanki zai zama sarki bayana, kuma shi zai zauna a kan kujerar sarautata a maimakona.”
31 Sai Batsheba ta rusuna da fuskarta har ƙasa, ta kuma durƙusa a gaban sarki ta ce, “Bari ran Sarkina Dawuda yă daɗe, har abada!”
Bathsheba knelt down with her face on the ground and said, “Your Majesty, I hope/desire that you will live for many more years [HYP]!”
32 Sarki Dawuda ya ce, “Ku kira mini Zadok firist, annabi Natan, da Benahiya ɗan Yehohiyada.” Da suka zo gaban sarki,
Then King David said, “Summon Zadok the priest, Nathan the prophet, and Benaiah.” [So someone went and summoned them.] When they came in,
33 sai ya ce musu, “Ku ɗauki bayin sarki tare da ku, ku kuma sa ɗana Solomon a kan dokina, ku gangara da shi zuwa Gihon.
he said to them, “Put my son Solomon on my mule. Take him with my officials down to Gihon [Spring].
34 A can ku sa Zadok firist, da annabi Natan su shafe shi sarki a bisa Isra’ila. Ku busa ƙaho, ku kuma yi ihu, kuna cewa, ‘Ran Sarki Solomon yă daɗe!’
There, you two, Zadok and Nathan, should anoint him, [with olive oil to appoint him to be] the king of Israel. Then you must blow trumpets, and [all the people there must] shout, ‘We hope/desire that King Solomon will live for many years!’
35 Sa’an nan ku haura tare da shi, zai kuwa zo yă zauna a kujera sarautata, yă yi mulki a maimakona. Na naɗa shi mai mulki a bisa Isra’ila da Yahuda.”
Then follow him back here, and he will come and sit on my throne. He will then become king instead of me. I have appointed him to be the ruler of [all the people of] Israel and of Judah.”
36 Benahiya ɗan Yehohiyada ya amsa wa sarki, ya ce, “Amin! Bari Ubangiji Allah na ranka yă daɗe sarkina, yă tabbatar da haka.
Benaiah replied, “We will do that! We hope/wish that Yahweh, who is your God [and our God], will cause it to happen!
37 Kamar yadda Ubangiji ya kasance da ranka yă daɗe, sarki, haka ma bari yă kasance da Solomon, yă kuma mai da kujerar sarautarsa tă fi kujerar sarautar ranka yă daɗe, Sarki Dawuda, girma!”
King David, Yahweh has helped you; we hope/wish that he will also help Solomon and enable him to become a greater king than you have been.”
38 Sai Zadok firist, annabi Natan, Benahiya ɗan Yehohiyada, Keretawa, da Feletiyawa suka gangara, suka sa Solomon a kan dokin Sarki Dawuda, suka raka shi zuwa Gihon.
So Zadok, Nathan, Benaiah, and the two groups of men who were the king’s bodyguards went and put Solomon on King David’s mule and escorted him down to Gihon [Spring].
39 Zadok firist ya ɗauki ƙahon mai daga tenti mai tsarki, ya shafe Solomon. Sa’an nan suka busa ƙaho, sai dukan mutane suka yi ihu, suna cewa “Ran Sarki Solomon yă daɗe!”
There Zadok took the container of [olive] oil from the Sacred Tent and (anointed/poured some oil on) Solomon. Then the trumpets were blown, and all the people shouted, “We hope/wish that King Solomon will live for many years!”
40 Dukan mutane kuwa suka haura suka bi shi, suna busan sarewa, suna farin ciki sosai, har ƙasa ta girgiza saboda sowa.
Then all the people followed him back up [to the city], shouting joyfully and playing flutes. They shouted very loudly, with the result that the ground shook.
41 Adoniya tare da dukan baƙin da suke tare da shi kuwa suka ji wannan sa’ad da suke gama bikinsu. Da jin busan ƙaho, sai Yowab ya yi tambaya, ya ce, “Me ya jawo surutu haka a birni?”
When Adonijah and all (his guests/the people whom he had invited) were finishing eating at their celebration, they heard the noise. When Joab heard the sound of the trumpets, he asked, “What is causing all that noise in the city?”
42 Tun yana cikin magana, sai Yonatan ɗan Abiyatar ya iso. Adoniya ya ce, “Shigo! Ai, mutumin kirki irinka, lalle ka kawo labari mai daɗi ne.”
While he was still speaking, Jonathan, the son of Abiathar the priest, arrived. Adonijah said, “Come in! You are a man whom we can trust, so you must be bringing us good news!”
43 Yonatan ya ce wa Adoniya, “A ina! Ranka yă daɗe, Sarkinmu Dawuda ya naɗa Solomon sarki.
Jonathan replied, “No, [I do not have good news]! His Majesty, King David, has caused Solomon to be the king!
44 Sarki ya aika shi tare da Zadok firist, annabi Natan, Benahiya ɗan Yehohiyada, Keretawa, da Feletiyawa, suka sa shi a kan dokin sarki,
He sent Zadok, Nathan, Benaiah, and his own group of bodyguards to go with Solomon. They put Solomon on King David’s mule.
45 Zadok firist kuwa da annabi Natan sun shafe shi sarki a Gihon. Daga can suka haura suna kirari, birni kuwa ta ɓarke da sowa. Surutun da kake ji ke nan.
They [went down to] Gihon [Spring], and there Zadok and Nathan anointed him to become the king. Now they have returned from there to the city, shouting joyfully. That is why there is that great/loud noise that you are hearing.
46 Ban da haka ma, Solomon ne sarki yanzu.
So Solomon is now our king [MTY].
47 Yanzu haka, fadawa sun zo suna wa ranka yă daɗe, Sarki Dawuda, sam barka, suna cewa, ‘Bari Allahnka yă sa sunan Solomon yă zama sananne fiye da naka, bari kuma sarautarsa tă fi taka girma!’ Sarki kuwa ya rusuna, ya yi sujada a kan gadonsa
Furthermore, the palace officials came to His Majesty, King David, to tell him that they approved of what he had done. They said, ‘We wish/hope that our God will enable Solomon [MTY] to become more famous than you have been and enable him to be a better king than you have been.’ When they said that, the king, lying on his bed, bowed his head to worship [Yahweh].
48 ya ce, ‘Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya bar idanuna suka ga magāji a kan kujerar sarautata a yau.’”
Then he said, ‘I praise Yahweh, the God whom we Israelis [worship], because he has allowed one of my sons to become the king today, and has permitted me to see it happen.’”
49 A nan fa, dukan baƙin Adoniya suka taso da rawar jiki suka watse.
Then all of Adonijah’s guests (trembled/were afraid), so they all immediately got up and left and scattered.
50 Amma Adoniya, don tsoron Solomon, ya je ya kama ƙahon bagade ya riƙe.
Adonijah was afraid of what Solomon [would do], so he went [to the Sacred Tent] and grabbed the projections at the corners of the altar, [because he knew that no one would kill him there].
51 Sa’ad da aka faɗa wa Solomon cewa, “Adoniya yana tsoron Sarki Solomon, kuma ya manne wa ƙahonin bagade. Yana cewa, ‘Bari Sarki Solomon yă rantse mini a yau cewa ba zai kashe bawansa da takobi ba.’”
But someone told Solomon, “Hey/Listen, Adonijah is afraid of you, so he [has gone to the Sacred Tent and] is holding on to the corners of the altar. He is saying, ‘[Before I leave, ] I want King Solomon to solemnly promise that he will not command that I be executed.’”
52 Solomon ya amsa ya ce, “In ya nuna kansa mai biyayya, ba gashin kansa da zai fāɗi ƙasa; amma in aka same mugunta a cikinsa, zai mutu.”
Solomon replied, “If he proves that he is loyal to me, I will not harm him at all [IDM]. But if he does anything that is wrong, he will be executed.”
53 Sai Sarki Solomon ya aiki mutane, suka kuma sauko da shi daga bagade. Adoniya kuwa ya zo, ya rusuna wa Sarki Solomon, sai Solomon ya ce, “Tafi gidanka.”
So King Solomon sent [some men to Adonijah], and they brought him back from the altar. He came to Solomon and bowed down in front of him. Then Solomon said to him, “Go home.”

< 1 Sarakuna 1 >