< 1 Yohanna 5 >
1 Kowa ya gaskata cewa Yesu shi ne Kiristi, shi haifaffe na Allah ne, kuma duk mai ƙaunar mahaifi kuwa, yakan ƙaunaci ɗansa ma.
Hver den som tror at Jesus er Kristus, han er født av Gud, og hver den som elsker Faderen, han elsker også den som er født av ham.
2 Ga yadda muka san cewa muna ƙaunar’ya’yan Allah. Muna yin haka ta wurin ƙaunar Allah da kuma aikata umarnansa.
På dette kjenner vi at vi elsker Guds barn, når vi elsker Gud og holder hans bud.
3 Ƙaunar Allah ita ce, a yi biyayya da umarnansa. Umarnansa kuwa ba masu nauyi ba ne;
For dette er kjærligheten til Gud at vi holder hans bud; og hans bud er ikke tunge.
4 domin duk haifaffe na Allah yana cin nasara a kan duniya. Bangaskiyarmu kuwa ita ce ta ba mu wannan nasara a kan duniya.
For alt det som er født av Gud, seirer over verden; og dette er den seier som har seiret over verden: vår tro.
5 Wa ya cin nasara a kan duniya? Sai wanda ya gaskata cewa Yesu Ɗan Allah ne.
Hvem er den som seirer over verden, uten den som tror at Jesus er Guds Sønn?
6 Ga wanda ya zo ta wurin ruwa da jini, wato, Yesu Kiristi. Bai zo ta wurin ruwa kaɗai ba, sai dai ta wurin ruwa da kuma jini. Ruhu ne kuwa yake ba da shaida, gama Ruhu shi ne gaskiya.
Han er den som kom med vann og blod, Jesus Kristus; ikke bare med vannet, men med vannet og med blodet, og Ånden er den som vidner, fordi Ånden er sannheten.
7 Akwai shaidu uku, wato,
For de er tre som vidner:
8 Ruhu, da ruwa, da kuma jini; waɗannan uku kuwa manufarsu ɗaya ce.
Ånden og vannet og blodet, og disse tre går ut på ett.
9 Tun da yake mukan yarda da shaida mutane, ai, shaidar Allah ta fi ƙarfi. Wannan ita ce shaidar Allah, wato, ya shaidi Ɗansa.
Tar vi imot menneskenes vidnesbyrd, da er Guds vidnesbyrd større; for dette er Guds vidnesbyrd at han har vidnet om sin Sønn.
10 Duk wanda ya gaskata da Ɗan Allah, yana da shaidan nan a zuciyarsa. Duk wanda bai gaskata da Allah ba kuwa ya mai da shi maƙaryaci, domin bai gaskata shaidar da Allah ya bayar game da Ɗansa ba.
Den som tror på Guds Sønn, har vidnesbyrdet i sig selv; den som ikke tror Gud, har gjort ham til en løgner; for han har ikke trodd på det vidnesbyrd som Gud har vidnet om sin Sønn.
11 Wannan kuwa ita ce shaidar; cewa Allah ya ba mu rai madawwami, wannan rai kuwa yana cikin Ɗansa. (aiōnios )
Og dette er vidnesbyrdet at Gud har gitt oss evig liv, og dette liv er i hans Sønn. (aiōnios )
12 Duk wanda yake da Ɗan, yana da rai; wanda kuwa ba shi da Ɗan Allah, ba shi da rai.
Den som har Sønnen, han har livet; den som ikke har Guds Sønn, han har ikke livet.
13 Ina rubuta waɗannan abubuwa gare ku, ku da kuka gaskata sunan Ɗan Allah domin ku san kuna da rai madawwami. (aiōnios )
Dette har jeg skrevet til eder forat I skal vite at I har evig liv, I som tror på Guds Sønns navn. (aiōnios )
14 Wannan shi ne ƙarfin halin da muke da shi sa’ad da muke zuwa a gaban Allah, gama mun san cewa kome muka roƙa bisa ga nufinsa, yakan saurare mu.
Og dette er den frimodige tillit som vi har til ham, at dersom vi beder om noget efter hans vilje, da hører han oss;
15 In kuwa muka san cewa yana sauraranmu, ko mene ne muka roƙa, mun sani, mun riga mun sami abin da muka roƙa daga gare shi ke nan.
og dersom vi vet at han hører oss, hvad vi så beder om, da vet vi at vi har de ting vi har bedt ham om.
16 Kowa ya ga ɗan’uwansa yana yin zunubin da bai kai ga mutuwa ba, sai yă yi masa addu’a. Ta dalilin mai addu’an nan kuwa, Allah zai ba da rai ga mai yin zunubin da bai kai ga mutuwa ba. Akwai zunubin da yakan kai ga mutuwa. Ban ce a yi addu’a domin wannan ba.
Dersom nogen ser sin bror gjøre en synd som ikke er til døden, da skal han bede, og han skal gi ham liv - jeg mener dem som ikke synder til døden. Der er synd til døden; det er ikke om den jeg sier at han skal bede.
17 Duk rashin adalci, zunubi ne, amma akwai waɗansu zunuban da ba sa kai ga mutuwa.
Enhver urettferdighet er synd, og der er synd som ikke er til døden.
18 Mun san cewa kowane haifaffe na Allah ba ya cin gaba da yin zunubi; kasancewarsa haifaffe na Allah ita takan kāre shi, mugun kuwa ba zai iya cuce shi ba.
Vi vet at hver den som er født av Gud, synder ikke; men den som er født av Gud, tar sig i vare, og den onde rører ham ikke.
19 Mun san cewa mu’ya’yan Allah ne, duniya duka kuwa tana hannun Mugun.
Vi vet at vi er av Gud, og hele verden ligger i det onde;
20 Mun san cewa Ɗan Allah ya zo duniya, ya kuma ba mu ganewa domin mu san shi wanda yake na gaskiya. Mu kuwa muna cikinsa, shi da yake Allah na gaskiya wato, cikin Ɗansa Yesu Kiristi. Shi ne Allah na gaskiya da kuma rai na har abada. (aiōnios )
men vi vet at Guds Sønn er kommet, og han har gitt oss skjønn til å kjenne den Sanne, og vi er i den Sanne, i hans Sønn Jesus Kristus. Denne er den sanne Gud og det evige liv. (aiōnios )
21 ’Ya’yana ƙaunatattu, ku yi nesa da gumaka.
Mine barn! Vokt eder for avgudene!