< 1 Yohanna 5 >
1 Kowa ya gaskata cewa Yesu shi ne Kiristi, shi haifaffe na Allah ne, kuma duk mai ƙaunar mahaifi kuwa, yakan ƙaunaci ɗansa ma.
Mindenki, aki hiszi, hogy Jézus a Krisztus, Istentől született, és mindenki, aki szereti az Atyát, a Fiút is szereti, aki tőle született.
2 Ga yadda muka san cewa muna ƙaunar’ya’yan Allah. Muna yin haka ta wurin ƙaunar Allah da kuma aikata umarnansa.
Abból ismerjük meg, hogy szeretjük Isten gyermekeit, hogyha Istent szeretjük, és parancsolatait megtartjuk.
3 Ƙaunar Allah ita ce, a yi biyayya da umarnansa. Umarnansa kuwa ba masu nauyi ba ne;
Mert az az Isten szeretete, hogy megtartjuk parancsolatait. Az ő parancsolatai pedig nem nehezek.
4 domin duk haifaffe na Allah yana cin nasara a kan duniya. Bangaskiyarmu kuwa ita ce ta ba mu wannan nasara a kan duniya.
Mindenki, aki Istentől született legyőzi a világot. A győzelem, amely legyőzte a világot: a mi hitünk.
5 Wa ya cin nasara a kan duniya? Sai wanda ya gaskata cewa Yesu Ɗan Allah ne.
Ki az, aki legyőzi a világot, ha nem az, aki hiszi, hogy Jézus az Isten Fia.
6 Ga wanda ya zo ta wurin ruwa da jini, wato, Yesu Kiristi. Bai zo ta wurin ruwa kaɗai ba, sai dai ta wurin ruwa da kuma jini. Ruhu ne kuwa yake ba da shaida, gama Ruhu shi ne gaskiya.
Ő az a Jézus Krisztus, aki víz és vér által jött el. Nemcsak vízzel, hanem vízzel és vérrel. A Lélek pedig bizonyságot tesz Róla, mert a Lélek az igazság.
7 Akwai shaidu uku, wato,
Hárman vannak, akik bizonyságot tesznek a mennyben: az Atya, az Ige és a Szentlélek és ez a három egy.
8 Ruhu, da ruwa, da kuma jini; waɗannan uku kuwa manufarsu ɗaya ce.
És hárman vannak, akik bizonyságot tesznek a földön: a Lélek, a víz és a vér és ez a három is egy.
9 Tun da yake mukan yarda da shaida mutane, ai, shaidar Allah ta fi ƙarfi. Wannan ita ce shaidar Allah, wato, ya shaidi Ɗansa.
Ha elfogadjuk az emberek bizonyságtételét, Isten bizonyságtétele nagyobb, mert Isten bizonyságtétele az, amellyel Fiáról tesz bizonyságot.
10 Duk wanda ya gaskata da Ɗan Allah, yana da shaidan nan a zuciyarsa. Duk wanda bai gaskata da Allah ba kuwa ya mai da shi maƙaryaci, domin bai gaskata shaidar da Allah ya bayar game da Ɗansa ba.
Aki hisz Isten Fiában, abban megvan ez a bizonyságtétel. Aki nem hisz Istennek, hazuggá teszi őt, mert nem hisz abban a bizonyságtételben, amellyel Isten bizonyságot tett Fiáról.
11 Wannan kuwa ita ce shaidar; cewa Allah ya ba mu rai madawwami, wannan rai kuwa yana cikin Ɗansa. (aiōnios )
Ez a bizonyságtétel pedig az, hogy örök életet adott nekünk Isten. Ez az élet pedig az ő Fiában van. (aiōnios )
12 Duk wanda yake da Ɗan, yana da rai; wanda kuwa ba shi da Ɗan Allah, ba shi da rai.
Akié a Fiú, azé az élet. Akiben nincs meg Isten Fia, az élet sincs meg abban.
13 Ina rubuta waɗannan abubuwa gare ku, ku da kuka gaskata sunan Ɗan Allah domin ku san kuna da rai madawwami. (aiōnios )
Ezeket azért írtam nektek, akik hisztek Isten Fiának nevében, hogy tudjátok meg: örök életetek van. (aiōnios )
14 Wannan shi ne ƙarfin halin da muke da shi sa’ad da muke zuwa a gaban Allah, gama mun san cewa kome muka roƙa bisa ga nufinsa, yakan saurare mu.
Az az iránta való bizodalmunk, hogy ha kérünk valamit az ő akarata szerint, meghallgat minket.
15 In kuwa muka san cewa yana sauraranmu, ko mene ne muka roƙa, mun sani, mun riga mun sami abin da muka roƙa daga gare shi ke nan.
Ha pedig tudjuk, hogy meghallgat bennünket, bármit kérünk, azt is tudjuk, hogy meg is adja azt, amit tőle kérünk.
16 Kowa ya ga ɗan’uwansa yana yin zunubin da bai kai ga mutuwa ba, sai yă yi masa addu’a. Ta dalilin mai addu’an nan kuwa, Allah zai ba da rai ga mai yin zunubin da bai kai ga mutuwa ba. Akwai zunubin da yakan kai ga mutuwa. Ban ce a yi addu’a domin wannan ba.
Ha valaki látja, hogy atyjafia nem halálos bűnt követ el, könyörögjön érte, és életet fog adni annak, aki nem halálos bűnt követ el. Van halálos bűn. Nem az ilyen esetre mondom, hogy könyörögjön.
17 Duk rashin adalci, zunubi ne, amma akwai waɗansu zunuban da ba sa kai ga mutuwa.
Minden gonoszság bűn, de van nem halálos bűn is.
18 Mun san cewa kowane haifaffe na Allah ba ya cin gaba da yin zunubi; kasancewarsa haifaffe na Allah ita takan kāre shi, mugun kuwa ba zai iya cuce shi ba.
Tudjuk, hogy aki Istentől született nem vétkezik, hanem aki Istentől született vigyáz magára, és a gonosz meg sem érinti.
19 Mun san cewa mu’ya’yan Allah ne, duniya duka kuwa tana hannun Mugun.
Tudjuk, hogy Istentől vagyunk, és az egész világ gonoszságban vesztegel.
20 Mun san cewa Ɗan Allah ya zo duniya, ya kuma ba mu ganewa domin mu san shi wanda yake na gaskiya. Mu kuwa muna cikinsa, shi da yake Allah na gaskiya wato, cikin Ɗansa Yesu Kiristi. Shi ne Allah na gaskiya da kuma rai na har abada. (aiōnios )
De tudjuk azt is, hogy az Isten Fia eljött és képességet adott nekünk arra, hogy megismerjük az Igazat, és hogy mi az Igazban, az ő Fiában, a Jézus Krisztusban vagyunk. Ő az igaz Isten és az örök élet. (aiōnios )
21 ’Ya’yana ƙaunatattu, ku yi nesa da gumaka.
Gyermekeim, oltalmazzátok meg magatokat a bálványoktól. Ámen.