< 1 Yohanna 5 >
1 Kowa ya gaskata cewa Yesu shi ne Kiristi, shi haifaffe na Allah ne, kuma duk mai ƙaunar mahaifi kuwa, yakan ƙaunaci ɗansa ma.
Everyone who believes that Jesus is the Christ has been born of God, and everyone who loves him who has begotten also loves the one begotten of him.
2 Ga yadda muka san cewa muna ƙaunar’ya’yan Allah. Muna yin haka ta wurin ƙaunar Allah da kuma aikata umarnansa.
By this we know that we love the children of God, when we love God and keep his commandments.
3 Ƙaunar Allah ita ce, a yi biyayya da umarnansa. Umarnansa kuwa ba masu nauyi ba ne;
For this is the love of God, that we keep his commandments. And his commandments are not burdensome.
4 domin duk haifaffe na Allah yana cin nasara a kan duniya. Bangaskiyarmu kuwa ita ce ta ba mu wannan nasara a kan duniya.
For everyone who has been born of God overcomes the world. This is the victory that has overcome the world—our faith.
5 Wa ya cin nasara a kan duniya? Sai wanda ya gaskata cewa Yesu Ɗan Allah ne.
Who is it that overcomes the world but he who believes that Jesus is the Son of God?
6 Ga wanda ya zo ta wurin ruwa da jini, wato, Yesu Kiristi. Bai zo ta wurin ruwa kaɗai ba, sai dai ta wurin ruwa da kuma jini. Ruhu ne kuwa yake ba da shaida, gama Ruhu shi ne gaskiya.
This is he who came by water and blood—Jesus Christ. He did not come by water only, but by water and blood. It is the Spirit who testifies, because the Spirit is the truth.
7 Akwai shaidu uku, wato,
For there are three that testify:
8 Ruhu, da ruwa, da kuma jini; waɗannan uku kuwa manufarsu ɗaya ce.
the Spirit, the water, and the blood; and these three are in agreement.
9 Tun da yake mukan yarda da shaida mutane, ai, shaidar Allah ta fi ƙarfi. Wannan ita ce shaidar Allah, wato, ya shaidi Ɗansa.
If we receive the testimony of men, we should know that the testimony of God is greater, because it is the testimony that God has given about his Son.
10 Duk wanda ya gaskata da Ɗan Allah, yana da shaidan nan a zuciyarsa. Duk wanda bai gaskata da Allah ba kuwa ya mai da shi maƙaryaci, domin bai gaskata shaidar da Allah ya bayar game da Ɗansa ba.
Whoever believes in the Son of God has the testimony in himself. Whoever does not believe God has made him a liar, because he has not believed the testimony that God has given about his Son.
11 Wannan kuwa ita ce shaidar; cewa Allah ya ba mu rai madawwami, wannan rai kuwa yana cikin Ɗansa. (aiōnios )
And this is the testimony, that God has given us eternal life, and this life is in his Son. (aiōnios )
12 Duk wanda yake da Ɗan, yana da rai; wanda kuwa ba shi da Ɗan Allah, ba shi da rai.
Whoever has the Son has life; whoever does not have the Son of God does not have life.
13 Ina rubuta waɗannan abubuwa gare ku, ku da kuka gaskata sunan Ɗan Allah domin ku san kuna da rai madawwami. (aiōnios )
I have written these things to you who believe in the name of the Son of God so that you may know that you have eternal life, and so that you may continue believing in the name of the Son of God. (aiōnios )
14 Wannan shi ne ƙarfin halin da muke da shi sa’ad da muke zuwa a gaban Allah, gama mun san cewa kome muka roƙa bisa ga nufinsa, yakan saurare mu.
This is the confidence that we have toward him, that if we ask anything according to his will, he hears us.
15 In kuwa muka san cewa yana sauraranmu, ko mene ne muka roƙa, mun sani, mun riga mun sami abin da muka roƙa daga gare shi ke nan.
And if we know that he hears us in whatever we ask, we know that we have what we have asked of him.
16 Kowa ya ga ɗan’uwansa yana yin zunubin da bai kai ga mutuwa ba, sai yă yi masa addu’a. Ta dalilin mai addu’an nan kuwa, Allah zai ba da rai ga mai yin zunubin da bai kai ga mutuwa ba. Akwai zunubin da yakan kai ga mutuwa. Ban ce a yi addu’a domin wannan ba.
If anyone sees his brother committing a sin that does not lead to death, he should pray for him, and God will give him life. I refer to those who commit sins that do not lead to death. There is sin that leads to death; I do not say that he should pray about that.
17 Duk rashin adalci, zunubi ne, amma akwai waɗansu zunuban da ba sa kai ga mutuwa.
All unrighteousness is sin, but there is sin that does not lead to death.
18 Mun san cewa kowane haifaffe na Allah ba ya cin gaba da yin zunubi; kasancewarsa haifaffe na Allah ita takan kāre shi, mugun kuwa ba zai iya cuce shi ba.
We know that no one who has been born of God continues in sin, but he who is born of God guards himself, and the evil one does not touch him.
19 Mun san cewa mu’ya’yan Allah ne, duniya duka kuwa tana hannun Mugun.
We know that we are from God, and that the whole world lies in the power of the evil one.
20 Mun san cewa Ɗan Allah ya zo duniya, ya kuma ba mu ganewa domin mu san shi wanda yake na gaskiya. Mu kuwa muna cikinsa, shi da yake Allah na gaskiya wato, cikin Ɗansa Yesu Kiristi. Shi ne Allah na gaskiya da kuma rai na har abada. (aiōnios )
And we know that the Son of God has come and given us understanding so that we may know him who is true. And we are in him who is true, in his Son Jesus Christ. He is the true God and eternal life. (aiōnios )
21 ’Ya’yana ƙaunatattu, ku yi nesa da gumaka.
Little children, guard yourselves from idols. Amen.