< 1 Yohanna 5 >
1 Kowa ya gaskata cewa Yesu shi ne Kiristi, shi haifaffe na Allah ne, kuma duk mai ƙaunar mahaifi kuwa, yakan ƙaunaci ɗansa ma.
Whosoever believeth that, Jesus, is the Christ, of God, hath been born: and, whosoever loveth him that begat, loveth him that hath been begotten of him.
2 Ga yadda muka san cewa muna ƙaunar’ya’yan Allah. Muna yin haka ta wurin ƙaunar Allah da kuma aikata umarnansa.
Hereby, perceive we, that we love the children of God, as soon as, God, we love, and, his commandments, we are doing.
3 Ƙaunar Allah ita ce, a yi biyayya da umarnansa. Umarnansa kuwa ba masu nauyi ba ne;
For, this is the love of God—that, his commandments, we be keeping, and, his commandments, are not burdensome;
4 domin duk haifaffe na Allah yana cin nasara a kan duniya. Bangaskiyarmu kuwa ita ce ta ba mu wannan nasara a kan duniya.
Because, whatsoever hath been born of God, overcometh the world; and, this, is the victory that hath overcome the world—our faith.
5 Wa ya cin nasara a kan duniya? Sai wanda ya gaskata cewa Yesu Ɗan Allah ne.
[And] who is he that overcometh the world, save he that believeth that, Jesus, is the Son of God?
6 Ga wanda ya zo ta wurin ruwa da jini, wato, Yesu Kiristi. Bai zo ta wurin ruwa kaɗai ba, sai dai ta wurin ruwa da kuma jini. Ruhu ne kuwa yake ba da shaida, gama Ruhu shi ne gaskiya.
This, is he that came through means of water and blood, Jesus Christ: not, by the water, only, but, by the water and by the blood, —and, the Spirit, it is, that is bearing witness, because, the Spirit, is the truth.
7 Akwai shaidu uku, wato,
Because, three, are they who are bearing witness—
8 Ruhu, da ruwa, da kuma jini; waɗannan uku kuwa manufarsu ɗaya ce.
The Spirit, and the Water, and the Blood; and, the three, are, [witnesses], unto one thing.
9 Tun da yake mukan yarda da shaida mutane, ai, shaidar Allah ta fi ƙarfi. Wannan ita ce shaidar Allah, wato, ya shaidi Ɗansa.
If, the witness of men, we receive, the witness of God, is, greater. Because, this, is the witness of God—in that he hath borne witness concerning his Son, —
10 Duk wanda ya gaskata da Ɗan Allah, yana da shaidan nan a zuciyarsa. Duk wanda bai gaskata da Allah ba kuwa ya mai da shi maƙaryaci, domin bai gaskata shaidar da Allah ya bayar game da Ɗansa ba.
He that believeth on the Son of God, hath the witness, within himself: He that doth not believe God, false, hath made him, —because he hath not believed on the witness which, God, hath witnessed, concerning his Son—
11 Wannan kuwa ita ce shaidar; cewa Allah ya ba mu rai madawwami, wannan rai kuwa yana cikin Ɗansa. (aiōnios )
And, this, is the witness: —that, life age-abiding, hath God given unto us, and, this life, is, in his Son: (aiōnios )
12 Duk wanda yake da Ɗan, yana da rai; wanda kuwa ba shi da Ɗan Allah, ba shi da rai.
He that hath the Son, hath, the life, —he that hath not the Son of God, hath not, the life.
13 Ina rubuta waɗannan abubuwa gare ku, ku da kuka gaskata sunan Ɗan Allah domin ku san kuna da rai madawwami. (aiōnios )
These things, have I written unto you—in order that ye may know that ye have, Life Age-abiding—unto you who believe on the name of the Son of God. (aiōnios )
14 Wannan shi ne ƙarfin halin da muke da shi sa’ad da muke zuwa a gaban Allah, gama mun san cewa kome muka roƙa bisa ga nufinsa, yakan saurare mu.
And, this, is the boldness which we have towards him: that, if, anything, we ask, according to his will, He doth hearken unto us.
15 In kuwa muka san cewa yana sauraranmu, ko mene ne muka roƙa, mun sani, mun riga mun sami abin da muka roƙa daga gare shi ke nan.
And, if we know that he doth hearken unto us, whatsoever we ask, we know that we have the things asked, which we have asked of him,
16 Kowa ya ga ɗan’uwansa yana yin zunubin da bai kai ga mutuwa ba, sai yă yi masa addu’a. Ta dalilin mai addu’an nan kuwa, Allah zai ba da rai ga mai yin zunubin da bai kai ga mutuwa ba. Akwai zunubin da yakan kai ga mutuwa. Ban ce a yi addu’a domin wannan ba.
If one should see his brother committing a sin, not unto death, he shall ask, and He will grant unto him life, —for them who are sinning, not unto death. There, is, a sin, unto death: not concerning that, am I saying, that he should make request.
17 Duk rashin adalci, zunubi ne, amma akwai waɗansu zunuban da ba sa kai ga mutuwa.
All unrighteousness, is, sin, and there, is, a sin, not unto death.
18 Mun san cewa kowane haifaffe na Allah ba ya cin gaba da yin zunubi; kasancewarsa haifaffe na Allah ita takan kāre shi, mugun kuwa ba zai iya cuce shi ba.
We know that, whosoever hath been born of God, is not committing sin, —Nay, he that hath been born of God, He keepeth him, and, the wicked one, doth not touch him.
19 Mun san cewa mu’ya’yan Allah ne, duniya duka kuwa tana hannun Mugun.
We know that, of God, are we; and, the whole world, in the wicked one, is lying.
20 Mun san cewa Ɗan Allah ya zo duniya, ya kuma ba mu ganewa domin mu san shi wanda yake na gaskiya. Mu kuwa muna cikinsa, shi da yake Allah na gaskiya wato, cikin Ɗansa Yesu Kiristi. Shi ne Allah na gaskiya da kuma rai na har abada. (aiōnios )
We know, moreover, that, the Son of God, hath come, and hath given us insight, so that we are getting to understand, him that is Real, —and we are in him that is Real, in his Son Jesus Christ. This, is the Real God, and life age-abiding. (aiōnios )
21 ’Ya’yana ƙaunatattu, ku yi nesa da gumaka.
Dear children! Guard yourselves from idols.