< 1 Yohanna 5 >
1 Kowa ya gaskata cewa Yesu shi ne Kiristi, shi haifaffe na Allah ne, kuma duk mai ƙaunar mahaifi kuwa, yakan ƙaunaci ɗansa ma.
Whoever believes that Jesus is the Christ is born of God: and every one that loves him that fathered loves him also that is begotten of him.
2 Ga yadda muka san cewa muna ƙaunar’ya’yan Allah. Muna yin haka ta wurin ƙaunar Allah da kuma aikata umarnansa.
By this we know that we love the children of God, when we love God, and keep his commandments.
3 Ƙaunar Allah ita ce, a yi biyayya da umarnansa. Umarnansa kuwa ba masu nauyi ba ne;
For this is the love of God, that we keep his commandments: and his commandments are not grievous.
4 domin duk haifaffe na Allah yana cin nasara a kan duniya. Bangaskiyarmu kuwa ita ce ta ba mu wannan nasara a kan duniya.
For whatever is born of God overcomes the world: and this is the victory that overcomes the world, even our faith.
5 Wa ya cin nasara a kan duniya? Sai wanda ya gaskata cewa Yesu Ɗan Allah ne.
Who is he that overcomes the world, but he that believes that Jesus is the Son of God?
6 Ga wanda ya zo ta wurin ruwa da jini, wato, Yesu Kiristi. Bai zo ta wurin ruwa kaɗai ba, sai dai ta wurin ruwa da kuma jini. Ruhu ne kuwa yake ba da shaida, gama Ruhu shi ne gaskiya.
This is he that came by water and blood, even Jesus Christ; not by water only, but by water and blood. And it is the Spirit that bears witness, because the Spirit is truth.
7 Akwai shaidu uku, wato,
For there are three that bear record in heaven, the Father, the Word, and the Holy Ghost: and these three are one.
8 Ruhu, da ruwa, da kuma jini; waɗannan uku kuwa manufarsu ɗaya ce.
And there are three that bear witness in earth, the Spirit, and the water, and the blood: and these three agree in one.
9 Tun da yake mukan yarda da shaida mutane, ai, shaidar Allah ta fi ƙarfi. Wannan ita ce shaidar Allah, wato, ya shaidi Ɗansa.
If we receive the witness of men, the witness of God is greater: for this is the witness of God which he has testified of his Son.
10 Duk wanda ya gaskata da Ɗan Allah, yana da shaidan nan a zuciyarsa. Duk wanda bai gaskata da Allah ba kuwa ya mai da shi maƙaryaci, domin bai gaskata shaidar da Allah ya bayar game da Ɗansa ba.
He that believes on the Son of God has the witness in himself: he that believes not God has made him a liar; because he believes not the record that God gave of his Son.
11 Wannan kuwa ita ce shaidar; cewa Allah ya ba mu rai madawwami, wannan rai kuwa yana cikin Ɗansa. (aiōnios )
And this is the record, that God has given to us eternal life, and this life is in his Son. (aiōnios )
12 Duk wanda yake da Ɗan, yana da rai; wanda kuwa ba shi da Ɗan Allah, ba shi da rai.
He that has the Son has life; and he that has not the Son of God has not life.
13 Ina rubuta waɗannan abubuwa gare ku, ku da kuka gaskata sunan Ɗan Allah domin ku san kuna da rai madawwami. (aiōnios )
These things have I written to you that believe on the name of the Son of God; that you may know that you have eternal life, and that you may believe on the name of the Son of God. (aiōnios )
14 Wannan shi ne ƙarfin halin da muke da shi sa’ad da muke zuwa a gaban Allah, gama mun san cewa kome muka roƙa bisa ga nufinsa, yakan saurare mu.
And this is the confidence that we have in him, that, if we ask any thing according to his will, he hears us:
15 In kuwa muka san cewa yana sauraranmu, ko mene ne muka roƙa, mun sani, mun riga mun sami abin da muka roƙa daga gare shi ke nan.
And if we know that he hear us, whatever we ask, we know that we have the petitions that we desired of him.
16 Kowa ya ga ɗan’uwansa yana yin zunubin da bai kai ga mutuwa ba, sai yă yi masa addu’a. Ta dalilin mai addu’an nan kuwa, Allah zai ba da rai ga mai yin zunubin da bai kai ga mutuwa ba. Akwai zunubin da yakan kai ga mutuwa. Ban ce a yi addu’a domin wannan ba.
If any man see his brother sin a sin which is not to death, he shall ask, and he shall give him life for them that sin not to death. There is a sin to death: I do not say that he shall pray for it.
17 Duk rashin adalci, zunubi ne, amma akwai waɗansu zunuban da ba sa kai ga mutuwa.
All unrighteousness is sin: and there is a sin not to death.
18 Mun san cewa kowane haifaffe na Allah ba ya cin gaba da yin zunubi; kasancewarsa haifaffe na Allah ita takan kāre shi, mugun kuwa ba zai iya cuce shi ba.
We know that whoever is born of God sins not; but he that is begotten of God keeps himself, and that wicked one touches him not.
19 Mun san cewa mu’ya’yan Allah ne, duniya duka kuwa tana hannun Mugun.
And we know that we are of God, and the whole world lies in wickedness.
20 Mun san cewa Ɗan Allah ya zo duniya, ya kuma ba mu ganewa domin mu san shi wanda yake na gaskiya. Mu kuwa muna cikinsa, shi da yake Allah na gaskiya wato, cikin Ɗansa Yesu Kiristi. Shi ne Allah na gaskiya da kuma rai na har abada. (aiōnios )
And we know that the Son of God is come, and has given us an understanding, that we may know him that is true, and we are in him that is true, even in his Son Jesus Christ. This is the true God, and eternal life. (aiōnios )
21 ’Ya’yana ƙaunatattu, ku yi nesa da gumaka.
Little children, keep yourselves from idols. Amen.