< 1 Yohanna 4 >

1 Abokaina ƙaunatattu, ba kowane ruhu za ku gaskata ba, sai dai ku gwada ruhohi don ku ga ko daga Allah ne, domin annabawan ƙarya da yawa sun fito duniya.
Morom laga bhai khan, sob atma ke biswas nokoribi. Kintu, kuntu atma Isor pora ase etu bhal pora sai lobi, kelemane bisi misa bhabobadi khan prithibi te ulaikene ase.
2 Ga yadda za ku gane Ruhun Allah, duk ruhun da ya yarda cewa Yesu Kiristi ya zo cikin jiki, to, daga Allah yake.
Etu pora tumikhan Isor laga Atma to janibo- kun manu Jisu Khrista to sharir hoi kene Isor pora ahise koi kene shikar kore,
3 Amma duk ruhun da bai yarda da Yesu ba, ba daga Allah ba ne, ruhun magabcin Kiristi ne, wanda kuka ji yana zuwa, har ma ya riga ya shigo duniya.
aru kun atma pora Jisu to Isor pora ahise koi kene shikar nakore. Etu Khrista bhirodh kora laga atma ase, jun ahibole ase koi kene tumikhan hunise, aru etiya tai prithibi te ahi jaise.
4 Ku,’ya’yana ƙaunatattu, ku daga Allah ne, kun kuma yi nasara a kan magabtan Kiristi, domin wanda yake a cikinku ya fi wanda yake a duniya girma.
Tumikhan Isor pora ase, morom laga bacha khan, aru taikhan ke jiti loise, kelemane etu ekjon kun tumi logote ase Tai etu duniya te thaka ekjon pora bhi sobse dangor ase.
5 Su daga duniya ne saboda haka suke magana yadda duniya take ganin abubuwa, duniya kuwa tana sauraronsu.
Taikhan duniya laga ase; etu nimite taikhan ki koi etu duniya laga he ase, aru duniya laga manu khan taikhan laga kotha he hune.
6 Mu daga Allah ne, kuma duk wanda ya san Allah yakan saurare mu. Amma duk wanda ba daga Allah ba, ba ya sauraronmu. Ta haka ne muke gane Ruhun gaskiya, da kuma ruhun ƙarya.
Amikhan Isor pora ase. Kun manu Isor ke jane amikhan laga kotha hune. Aru kun manu Isor pora nohoi amikhan laga kotha nahune. Etu pora amikhan jane hosa laga atma aru misa laga atma.
7 Abokaina ƙaunatattu, mu ƙaunaci juna, domin ƙauna tana zuwa daga Allah ne. Duk mai ƙauna, haifaffe ne na Allah, ya kuma san Allah.
Morom laga bhai khan, amikhan ekjon-ekjon ke morom koribo, kelemane morom to Isor pora he ahe, aru kun manu morom kore tai Isor pora jonom loise, kelemane Isor to morom ase.
8 Duk wanda ba ya ƙauna, bai san Allah ba, domin Allah ƙauna ne.
Kun manu morom kori bole najane tai Isor ke najane, kelemane Isor to morom ase.
9 Ga yadda Allah ya nuna ƙaunarsa a cikinmu, Allah ya aiki makaɗaici Ɗansa zuwa duniya domin mu rayu ta wurinsa.
Kelemane Isor laga etu morom amikhan ke dikhai diya nimite, Isor pora Tai laga ekjon morom thaka Putro ke duniya te pathai dise aru etu pora moi khan sob Tai logote jinda hoi jabo.
10 Wannan ita ce ƙauna, wato, ba mu ne muka ƙaunaci Allah ba, sai dai shi ne ya ƙaunace mu, ya kuma aiko Ɗansa yă zama hadaya ta kafara saboda zunubanmu.
Etu laga morom to, amikhan pora Isor ke morom kora karone nohoi, kintu Tai pora amikhan ke morom korise, aru Tai amikhan ke Tai laga Putro pathaise amikhan ke paap pora bacha bole nimite.
11 Abokaina ƙaunatattu, da yake Allah ya ƙaunace mu haka, ya kamata mu ma mu ƙaunaci juna.
Morom laga bhai khan, jodi Isor pora amikhan ke iman morom korise, titia hoile amikhan bhi ekjon-ekjon ke morom kori bole lage.
12 Ba wanda ya taɓa ganin Allah; amma in muna ƙaunar juna, Allah yana raye a cikinmu, ƙaunarsa kuwa ta zama cikakkiya a cikinmu ke nan.
Kun manu bhi Isor ke kitia bhi dikha nai. Jodi amikhan ekjon-ekjon ke morom kore, Isor amikhan logote thake, aru Tai laga morom to amikhan logot bhal bonai diye.
13 Mun san cewa muna rayuwa a cikinsa shi kuma a cikinmu, domin ya ba mu Ruhunsa.
Etu pora Isor amikhan logote ase koi kene jane, kelemane Tai laga Atma amikhan ke dise.
14 Mun gani, mun kuma shaida cewa Uba ya aiko Ɗansa domin yă zama Mai Ceton duniya.
Aru, amikhan dikhise aru etu laga gawahi ase Baba pora Tai laga Putro ke etu duniya laga Tran-korta hobole pathaise.
15 Duk wanda ya yarda cewa Yesu Ɗan Allah ne, Allah yana raye a cikinsa, shi kuma a cikin Allah.
Kun manu nijor laga mukh pora shikar kore Jisu he Isor laga Putro ase koi kene, Isor tai logote ase aru tai bhi Isor logote ase.
16 Ta haka muka sani, muke kuma dogara ga ƙaunar da Allah yake mana. Allah ƙauna ne. Duk wanda yake rayuwa cikin ƙauna, yana rayuwa a cikin Allah ne, Allah kuma a cikinsa.
Aru, Isor pora amikhan ke morom kora to janise aru biswas korise. Isor to morom ase, aru kun manu etu morom te thake tai Isor logote ase, aru Isor bhi tai logote ase.
17 Ta haka, ƙauna ta zama cikakkiya a cikinmu domin mu kasance masu ƙarfin hali a ranar shari’a, domin a wannan duniya muna kama da shi.
Etu nimite, morom to amikhan laga majote bhal bonai dise, etu pora amikhan bisar kora laga dinte bharosa kori kene thakibo, kelemane Khrista thaka nisena, amikhan bhi etu duniya te thaki ase.
18 Babu tsoro cikin ƙauna. Cikakkiyar ƙauna dai takan kawar da tsoro, domin hukunci ne yake kawo tsoro. Mai jin tsoro ba cikakke ba ne a cikin ƙauna.
Morom te eku bhoi nai. Kintu, hosa morom pora sob bhoi phelai diye, kelemane bhoi to sajai pabole nimite ase. Kintu kun manu bhoi kore, morom to tai logote nai.
19 Muna ƙauna, domin ya ƙaunace mu da farko.
Amikhan morom kore kelemane Isor pora poila amikhan ke morom korise.
20 Duk wanda ya ce, “Ina ƙaunar Allah,” amma yana ƙin ɗan’uwansa, maƙaryaci ne. Gama duk wanda ba ya ƙaunar ɗan’uwansa da yake gani, ba zai iya ƙaunar Allah wanda ba ya gani ba.
Jodi kunba manu koi, “Moi Isor ke morom kore,” kintu nijor laga bhai ke ghin kore, tai misa koi ase. Kun manu tai laga nijor bhai ke morom nakore, kun tai dikhise, Isor ke kitia bhi morom kori bole na paribo, kunke tai dikha nai.
21 Ya kuma ba mu wannan umarni cewa duk wanda yake ƙaunar Allah, dole yă ƙaunaci ɗan’uwansa.
Aru, etu he sikhai diya kotha ase kun to amikhan Khrista nimite rakhise, kun manu Isor ke morom kore tai nijor laga bhai ke bhi morom kori bole lage.

< 1 Yohanna 4 >