< 1 Yohanna 3 >
1 Dubi irin ƙaunar da Uba ya ƙaunace mu da ita mana, har ana ce da mu’ya’yan Allah! Haka kuwa muke! Dalilin da ya sa duniya ba tă san mu ba shi ne, don ba tă san shi ba.
Behold then what manner of love the Father hath bestowed upon us, that we should be called the children of God: though for this reason the world knoweth us not, because it knew not Him.
2 Abokaina ƙaunatattu, yanzu, mu’ya’yan Allah ne, kuma abin da za mu zama nan gaba ba a riga an bayyana ba. Sai dai mun san cewa sa’ad da Kiristi ya bayyana, za mu zama kamar sa, domin za mu gan shi kamar yadda yake.
Beloved, we are now the children of God, but it doth not yet appear what we shall be: we know however, that, when He shall appear, we shall be like Him; for we shall see Him as He is.
3 Duk mai wannan bege a cikinsa yakan tsarkake kansa, kamar yadda shi Kiristi yake da tsabta.
And every one, that hath this hope in Him, purifieth himself, even as He is pure.
4 Duk mai yin zunubi yana karya doka ne; tabbatacce, zunubi, karya doka ne.
Every one that committeth sin, transgresseth the law; for sin is the violation of the law.
5 Sai dai kun san cewa Kiristi ya bayyana ne domin yă ɗauke zunubanmu. A cikinsa kuwa babu zunubi.
And ye know that He was manifested, to take away our sins: and in Him there is no sin.
6 Ba mai rayuwa a cikinsa da yake cin gaba da yin zunubi. Kowa da yake aikata zunubi, bai taɓa ganinsa ba, bai ma san shi ba.
Whosoever abideth in Him sinneth not: whosoever sinneth hath not seen Him, nor known Him.
7 ’Ya’yana ƙaunatattu, kada ku yarda wani yă ruɗe ku. Duk mai yin abin da yake daidai mai adalci ne, yadda Kiristi yake mai adalci.
Little children, let no one deceive you: he that practiseth righteousness is righteous, even as He is righteous:
8 Duk mai aikata abin da yake zunubi shi na Iblis ne, domin Iblis mai aikata zunubi ne tun farko. Dalilin da ya sa Ɗan Allah ya bayyana kuwa shi ne don yă rushe aikin Iblis.
he, that makes a practise of sin, is of the devil; for the devil sinneth from the beginning. And for this the Son of God was manifested, that He might destroy the works of the devil.
9 Babu haifaffe na Allah da zai ci gaba da yin zunubi, domin iri na Allah yana a cikinsa; ba zai iya ci gaba da yin zunubi ba, domin haifaffe ne na Allah.
Whosoever is born of God doth not practise sin, because his seed remaineth in him: and he cannot sin, because he is born of God.
10 Ta haka muka san waɗanda suke’ya’yan Allah da kuma waɗanda suke’ya’yan Iblis. Duk wanda ba ya yin abin da yake daidai, ba ɗan Allah ba ne; haka ma wanda ba ya ƙaunar ɗan’uwansa.
In this the children of God are manifest, and the children of the devil: whosoever doth not practise righteousness, and he who loveth not his brother, is not of God:
11 Wannan shi ne saƙon da kuka ji tun farko. Ya kamata mu ƙaunaci juna.
for this is the injunction which ye heard from the beginning, that we should love one another: not as Cain who was of the evil one, and slew his brother;
12 Kada ku zama kamar Kayinu, wanda ya zama na mugun nan, ya kuma kashe ɗan’uwansa. Me ya sa ya kashe shi? Domin ayyukansa mugaye ne, na ɗan’uwansa kuma na adalci ne.
and why did he slay him? because his own works were evil, and his brother's righteous.
13 Kada ku yi mamaki’yan’uwana, in duniya ta ƙi ku.
Wonder not then, my brethren, if the world hate you:
14 Mun san cewa mun riga mun ratsa daga mutuwa zuwa rai, domin muna ƙaunar’yan’uwanmu. Duk wanda ba ya ƙauna matacce ne har yanzu.
since we know that we have passed from death to life, because we love the brethren: he, that loveth not his brother, remaineth in death.
15 Duk mai ƙin ɗan’uwansa mai kisankai ne, kun kuma san cewa ba mai kisankan da yake da rai madawwami a cikinsa. (aiōnios )
Whosoever hateth his brother is a murderer: and ye know that no murderer hath eternal life abiding in him. (aiōnios )
16 Yadda muka san ƙauna ke nan, wato, Yesu Kiristi ya ba da ransa dominmu. Ya kamata mu ma mu ba da rayukanmu domin’yan’uwanmu.
In this we know his love, that He laid down his life for us: and we should be ready to lay down our lives for the brethren.
17 In wani yana da arziki, ya kuma ga ɗan’uwansa cikin rashi, bai kuwa taimake shi ba, anya, ƙaunar Allah tana a cikinsa kuwa?
But if any one, who hath the good things of the world, seeth his brother in want, and shutteth up his bowels from him, how dwelleth the love of God in him?
18 ’Ya’yana ƙaunatattu, kada mu yi ƙauna da fatar baki kawai, sai dai mu nuna ta ta wurin aikatawa da kuma gaskiya.
My little children, let us not love in word, or in tongue only, but in deed and in truth.
19 Ta haka muka san cewa mu na gaskiya ne, kuma za mu iya tsaya a gaban Allah ba tare da rawar jiki ba.
And hereby we know that we are of the truth, and shall assure our hearts before Him.
20 Idan zuciyarmu ta nuna mana muna da laifi, mun san cewa Allah ya fi zuciyarmu, ya kuma san dukan kome.
For, if our heart condemn us, God is still greater than our heart, and knoweth all things.
21 Abokaina ƙaunatattu, in zukatanmu ba su ba mu laifi ba, muna da ƙarfin halin tsayawa a gaban Allah ke nan.
Beloved, if our heart condemn us not, then have we confidence towards God:
22 Muna kuma samun dukan abin da muka roƙa daga gare shi, domin muna biyayya da umarnansa, muna kuma yin abin da ya gamshe shi.
and whatsoever we ask, we receive from Him, because we keep his commandments, and do the things that are pleasing in his sight.
23 Umarninsa kuwa shi ne, mu gaskata da sunan Ɗansa, Yesu Kiristi, mu kuma ƙaunaci juna kamar yadda ya umarce mu.
And this is his commandment, that we should believe in the name of his Son Jesus Christ, and love one another, as He hath given us a charge to do.
24 Waɗanda suke biyayya da umarnansa kuwa suna rayuwa a cikinsa, shi kuma a cikinsu. Ta haka muka san cewa yana raye a cikinmu. Mun san haka ta wurin Ruhun da ya ba mu.
And he, that keepeth his commandments, abideth in Him, and He in him: and hereby we know that He abideth in us, even by the Spirit which He hath given us.