< 1 Yohanna 3 >
1 Dubi irin ƙaunar da Uba ya ƙaunace mu da ita mana, har ana ce da mu’ya’yan Allah! Haka kuwa muke! Dalilin da ya sa duniya ba tă san mu ba shi ne, don ba tă san shi ba.
See what marvellous love the Father has bestowed upon us--that we should be called God's children: and that is what we are. For this reason the world does not recognize us--because it has not known Him.
2 Abokaina ƙaunatattu, yanzu, mu’ya’yan Allah ne, kuma abin da za mu zama nan gaba ba a riga an bayyana ba. Sai dai mun san cewa sa’ad da Kiristi ya bayyana, za mu zama kamar sa, domin za mu gan shi kamar yadda yake.
Dear friends, we are now God's children, but what we are to be in the future has not yet been fully revealed. We know that if Christ reappears we shall be like Him, because we shall see Him as He is.
3 Duk mai wannan bege a cikinsa yakan tsarkake kansa, kamar yadda shi Kiristi yake da tsabta.
And every man who has this hope fixed on Him, purifies himself so as to be as pure as He is.
4 Duk mai yin zunubi yana karya doka ne; tabbatacce, zunubi, karya doka ne.
Every one who is guilty of sin is also guilty of violating Law; for sin is the violation of Law.
5 Sai dai kun san cewa Kiristi ya bayyana ne domin yă ɗauke zunubanmu. A cikinsa kuwa babu zunubi.
And you know that He appeared in order to take away sins; and in Him there is no sin.
6 Ba mai rayuwa a cikinsa da yake cin gaba da yin zunubi. Kowa da yake aikata zunubi, bai taɓa ganinsa ba, bai ma san shi ba.
No one who continues in union with Him lives in sin: no one who lives in sin has seen Him or knows Him.
7 ’Ya’yana ƙaunatattu, kada ku yarda wani yă ruɗe ku. Duk mai yin abin da yake daidai mai adalci ne, yadda Kiristi yake mai adalci.
Dear children, let no one lead you astray. The man who acts righteously is righteous, just as He is righteous.
8 Duk mai aikata abin da yake zunubi shi na Iblis ne, domin Iblis mai aikata zunubi ne tun farko. Dalilin da ya sa Ɗan Allah ya bayyana kuwa shi ne don yă rushe aikin Iblis.
He who is habitually guilty of sin is a child of the Devil, because the Devil has been a sinner from the very beginning. The Son of God appeared for the purpose of undoing the work of the Devil.
9 Babu haifaffe na Allah da zai ci gaba da yin zunubi, domin iri na Allah yana a cikinsa; ba zai iya ci gaba da yin zunubi ba, domin haifaffe ne na Allah.
No one who is a child of God is habitually guilty of sin. A God-given germ of life remains in him, and he cannot habitually sin--because he is a child of God.
10 Ta haka muka san waɗanda suke’ya’yan Allah da kuma waɗanda suke’ya’yan Iblis. Duk wanda ba ya yin abin da yake daidai, ba ɗan Allah ba ne; haka ma wanda ba ya ƙaunar ɗan’uwansa.
By this we can distinguish God's children and the Devil's children: no one who fails to act righteously is a child of God, nor he who does not love his brother man.
11 Wannan shi ne saƙon da kuka ji tun farko. Ya kamata mu ƙaunaci juna.
For this is the Message you have heard from the beginning--that we are to love one another.
12 Kada ku zama kamar Kayinu, wanda ya zama na mugun nan, ya kuma kashe ɗan’uwansa. Me ya sa ya kashe shi? Domin ayyukansa mugaye ne, na ɗan’uwansa kuma na adalci ne.
We are not to resemble Cain, who was a child of the Evil one and killed his own brother. And why did he kill him? Because his own actions were wicked and his brother's actions righteous.
13 Kada ku yi mamaki’yan’uwana, in duniya ta ƙi ku.
Do not be surprised, brethren, if the world hates you.
14 Mun san cewa mun riga mun ratsa daga mutuwa zuwa rai, domin muna ƙaunar’yan’uwanmu. Duk wanda ba ya ƙauna matacce ne har yanzu.
As for us, we know that we have already passed out of death into Life--because we love our brother men. He who is destitute of love continues dead.
15 Duk mai ƙin ɗan’uwansa mai kisankai ne, kun kuma san cewa ba mai kisankan da yake da rai madawwami a cikinsa. (aiōnios )
Every one who hates his brother man is a murderer; and you know that no murderer has the Life of the Ages continuing in him. (aiōnios )
16 Yadda muka san ƙauna ke nan, wato, Yesu Kiristi ya ba da ransa dominmu. Ya kamata mu ma mu ba da rayukanmu domin’yan’uwanmu.
We know what love is--through Christ's having laid down His life on our behalf; and in the same way we ought to lay down our lives for our brother men.
17 In wani yana da arziki, ya kuma ga ɗan’uwansa cikin rashi, bai kuwa taimake shi ba, anya, ƙaunar Allah tana a cikinsa kuwa?
But if any one has this world's wealth and sees that his brother man is in need, and yet hardens his heart against him--how can such a one continue to love God?
18 ’Ya’yana ƙaunatattu, kada mu yi ƙauna da fatar baki kawai, sai dai mu nuna ta ta wurin aikatawa da kuma gaskiya.
Dear children, let us not love in words only nor with the lips, but in deed and in truth.
19 Ta haka muka san cewa mu na gaskiya ne, kuma za mu iya tsaya a gaban Allah ba tare da rawar jiki ba.
And in this way we shall come to know that we are loyal to the truth, and shall satisfy our consciences in His presence
20 Idan zuciyarmu ta nuna mana muna da laifi, mun san cewa Allah ya fi zuciyarmu, ya kuma san dukan kome.
in whatever matters our hearts condemn us--because God is greater than our hearts and knows everything.
21 Abokaina ƙaunatattu, in zukatanmu ba su ba mu laifi ba, muna da ƙarfin halin tsayawa a gaban Allah ke nan.
Dear friends, if our hearts do not condemn us, we have perfect confidence towards God;
22 Muna kuma samun dukan abin da muka roƙa daga gare shi, domin muna biyayya da umarnansa, muna kuma yin abin da ya gamshe shi.
and whatever we ask for we obtain from Him, because we obey His commands and do the things which are pleasing in His sight.
23 Umarninsa kuwa shi ne, mu gaskata da sunan Ɗansa, Yesu Kiristi, mu kuma ƙaunaci juna kamar yadda ya umarce mu.
And this is His command--that we are to believe in His Son Jesus Christ and love one another, just as He has commanded us to do.
24 Waɗanda suke biyayya da umarnansa kuwa suna rayuwa a cikinsa, shi kuma a cikinsu. Ta haka muka san cewa yana raye a cikinmu. Mun san haka ta wurin Ruhun da ya ba mu.
The man who obeys His commands continues in union with God, and God continues in union with him; and through His Spirit whom He has given us we can know that He continues in union with us.