< 1 Yohanna 3 >
1 Dubi irin ƙaunar da Uba ya ƙaunace mu da ita mana, har ana ce da mu’ya’yan Allah! Haka kuwa muke! Dalilin da ya sa duniya ba tă san mu ba shi ne, don ba tă san shi ba.
See what great love the Father has lavished upon us, that we should be called children of God! The reason the world does not know you is that it did not know him.
2 Abokaina ƙaunatattu, yanzu, mu’ya’yan Allah ne, kuma abin da za mu zama nan gaba ba a riga an bayyana ba. Sai dai mun san cewa sa’ad da Kiristi ya bayyana, za mu zama kamar sa, domin za mu gan shi kamar yadda yake.
Beloved, now we are children of God, and what we will be has not yet been revealed. But we know that when he appears, we will be like him, because we will see him as he is.
3 Duk mai wannan bege a cikinsa yakan tsarkake kansa, kamar yadda shi Kiristi yake da tsabta.
Everyone who places this hope in him purifies himself, just as he is pure.
4 Duk mai yin zunubi yana karya doka ne; tabbatacce, zunubi, karya doka ne.
Everyone who practices sin also practices lawlessness; sin is lawlessness.
5 Sai dai kun san cewa Kiristi ya bayyana ne domin yă ɗauke zunubanmu. A cikinsa kuwa babu zunubi.
But you know that he appeared in order to take away our sins, and in him there is no sin.
6 Ba mai rayuwa a cikinsa da yake cin gaba da yin zunubi. Kowa da yake aikata zunubi, bai taɓa ganinsa ba, bai ma san shi ba.
No one who abides in him continues in sin; no one who continues in sin has either seen him or known him.
7 ’Ya’yana ƙaunatattu, kada ku yarda wani yă ruɗe ku. Duk mai yin abin da yake daidai mai adalci ne, yadda Kiristi yake mai adalci.
Little children, let no one deceive you. Whoever practices righteousness is righteous, just as he is righteous.
8 Duk mai aikata abin da yake zunubi shi na Iblis ne, domin Iblis mai aikata zunubi ne tun farko. Dalilin da ya sa Ɗan Allah ya bayyana kuwa shi ne don yă rushe aikin Iblis.
Whoever practices sin is of the devil, for the devil has been sinning from the beginning. The reason the Son of God appeared was to destroy the works of the devil.
9 Babu haifaffe na Allah da zai ci gaba da yin zunubi, domin iri na Allah yana a cikinsa; ba zai iya ci gaba da yin zunubi ba, domin haifaffe ne na Allah.
No one who has been born of God continues in sin, because God's seed abides in him; he cannot continue in sin, because he has been born of God.
10 Ta haka muka san waɗanda suke’ya’yan Allah da kuma waɗanda suke’ya’yan Iblis. Duk wanda ba ya yin abin da yake daidai, ba ɗan Allah ba ne; haka ma wanda ba ya ƙaunar ɗan’uwansa.
By this the children of God and the children of the devil are revealed: Anyone who does not practice righteousness is not of God, nor is anyone who does not love his brother.
11 Wannan shi ne saƙon da kuka ji tun farko. Ya kamata mu ƙaunaci juna.
For this is the message you have heard from the beginning, that we should love one another.
12 Kada ku zama kamar Kayinu, wanda ya zama na mugun nan, ya kuma kashe ɗan’uwansa. Me ya sa ya kashe shi? Domin ayyukansa mugaye ne, na ɗan’uwansa kuma na adalci ne.
We should not be like Cain, who was of the evil one and murdered his brother. And why did he murder him? Because his own deeds were evil, but the deeds of his brother were righteous.
13 Kada ku yi mamaki’yan’uwana, in duniya ta ƙi ku.
Do not be surprised, my brothers, if the world hates you.
14 Mun san cewa mun riga mun ratsa daga mutuwa zuwa rai, domin muna ƙaunar’yan’uwanmu. Duk wanda ba ya ƙauna matacce ne har yanzu.
We know that we have passed from death to life because we love our brothers. Whoever does not love his brother abides in death.
15 Duk mai ƙin ɗan’uwansa mai kisankai ne, kun kuma san cewa ba mai kisankan da yake da rai madawwami a cikinsa. (aiōnios )
Anyone who hates his brother is a murderer, and you know that no murderer has eternal life abiding in him. (aiōnios )
16 Yadda muka san ƙauna ke nan, wato, Yesu Kiristi ya ba da ransa dominmu. Ya kamata mu ma mu ba da rayukanmu domin’yan’uwanmu.
By this we know love, that he laid down his life for us. And we ought to lay down our lives for our brothers.
17 In wani yana da arziki, ya kuma ga ɗan’uwansa cikin rashi, bai kuwa taimake shi ba, anya, ƙaunar Allah tana a cikinsa kuwa?
If anyone has the world's goods and sees his brother in need but closes his heart against him, how does the love of God abide in him?
18 ’Ya’yana ƙaunatattu, kada mu yi ƙauna da fatar baki kawai, sai dai mu nuna ta ta wurin aikatawa da kuma gaskiya.
My little children, let us not love in word or speech, but in deed and truth.
19 Ta haka muka san cewa mu na gaskiya ne, kuma za mu iya tsaya a gaban Allah ba tare da rawar jiki ba.
By this we know that we are of the truth and can reassure our hearts before him:
20 Idan zuciyarmu ta nuna mana muna da laifi, mun san cewa Allah ya fi zuciyarmu, ya kuma san dukan kome.
If our hearts condemn us, God is greater than our hearts and knows all things.
21 Abokaina ƙaunatattu, in zukatanmu ba su ba mu laifi ba, muna da ƙarfin halin tsayawa a gaban Allah ke nan.
Beloved, if our hearts do not condemn us, we have confidence before God
22 Muna kuma samun dukan abin da muka roƙa daga gare shi, domin muna biyayya da umarnansa, muna kuma yin abin da ya gamshe shi.
and receive from him whatever we ask, because we keep his commandments and do what is pleasing in his sight.
23 Umarninsa kuwa shi ne, mu gaskata da sunan Ɗansa, Yesu Kiristi, mu kuma ƙaunaci juna kamar yadda ya umarce mu.
And this is his commandment, that we believe in the name of his Son Jesus Christ and love one another, just as he commanded.
24 Waɗanda suke biyayya da umarnansa kuwa suna rayuwa a cikinsa, shi kuma a cikinsu. Ta haka muka san cewa yana raye a cikinmu. Mun san haka ta wurin Ruhun da ya ba mu.
Whoever keeps his commandments abides in God, and God abides in him. And we know that he abides in us because of the Spirit he has given us.