< 1 Yohanna 3 >
1 Dubi irin ƙaunar da Uba ya ƙaunace mu da ita mana, har ana ce da mu’ya’yan Allah! Haka kuwa muke! Dalilin da ya sa duniya ba tă san mu ba shi ne, don ba tă san shi ba.
Behold what manner of charity the Father hath bestowed upon us, that we should be called, and should be the sons of God. Therefore the world knoweth not us, because it knew not him.
2 Abokaina ƙaunatattu, yanzu, mu’ya’yan Allah ne, kuma abin da za mu zama nan gaba ba a riga an bayyana ba. Sai dai mun san cewa sa’ad da Kiristi ya bayyana, za mu zama kamar sa, domin za mu gan shi kamar yadda yake.
Dearly beloved, we are now the sons of God; and it hath not yet appeared what we shall be. We know, that, when he shall appear, we shall be like to him: because we shall see him as he is.
3 Duk mai wannan bege a cikinsa yakan tsarkake kansa, kamar yadda shi Kiristi yake da tsabta.
And every one that hath this hope in him, sanctifieth himself, as he also is holy.
4 Duk mai yin zunubi yana karya doka ne; tabbatacce, zunubi, karya doka ne.
Whosoever committeth sin committeth also iniquity; and sin is iniquity.
5 Sai dai kun san cewa Kiristi ya bayyana ne domin yă ɗauke zunubanmu. A cikinsa kuwa babu zunubi.
And you know that he appeared to take away our sins, and in him there is no sin.
6 Ba mai rayuwa a cikinsa da yake cin gaba da yin zunubi. Kowa da yake aikata zunubi, bai taɓa ganinsa ba, bai ma san shi ba.
Whosoever abideth in him, sinneth not; and whosoever sinneth, hath not seen him, nor known him.
7 ’Ya’yana ƙaunatattu, kada ku yarda wani yă ruɗe ku. Duk mai yin abin da yake daidai mai adalci ne, yadda Kiristi yake mai adalci.
Little children, let no man deceive you. He that doth justice is just, even as he is just.
8 Duk mai aikata abin da yake zunubi shi na Iblis ne, domin Iblis mai aikata zunubi ne tun farko. Dalilin da ya sa Ɗan Allah ya bayyana kuwa shi ne don yă rushe aikin Iblis.
He that committeth sin is of the devil: for the devil sinneth from the beginning. For this purpose, the Son of God appeared, that he might destroy the works of the devil.
9 Babu haifaffe na Allah da zai ci gaba da yin zunubi, domin iri na Allah yana a cikinsa; ba zai iya ci gaba da yin zunubi ba, domin haifaffe ne na Allah.
Whosoever is born of God, committeth not sin: for his seed abideth in him, and he can not sin, because he is born of God.
10 Ta haka muka san waɗanda suke’ya’yan Allah da kuma waɗanda suke’ya’yan Iblis. Duk wanda ba ya yin abin da yake daidai, ba ɗan Allah ba ne; haka ma wanda ba ya ƙaunar ɗan’uwansa.
In this the children of God are manifest, and the children of the devil. Whosoever is not just, is not of God, nor he that loveth not his brother.
11 Wannan shi ne saƙon da kuka ji tun farko. Ya kamata mu ƙaunaci juna.
For this is the declaration, which you have heard from the beginning, that you should love one another.
12 Kada ku zama kamar Kayinu, wanda ya zama na mugun nan, ya kuma kashe ɗan’uwansa. Me ya sa ya kashe shi? Domin ayyukansa mugaye ne, na ɗan’uwansa kuma na adalci ne.
Not as Cain, who was of the wicked one, and killed his brother. And wherefore did he kill him? Because his own works were wicked: and his brother’s just.
13 Kada ku yi mamaki’yan’uwana, in duniya ta ƙi ku.
Wonder not, brethren, if the world hate you.
14 Mun san cewa mun riga mun ratsa daga mutuwa zuwa rai, domin muna ƙaunar’yan’uwanmu. Duk wanda ba ya ƙauna matacce ne har yanzu.
We know that we have passed from death to life, because we love the brethren. He that loveth not, abideth in death.
15 Duk mai ƙin ɗan’uwansa mai kisankai ne, kun kuma san cewa ba mai kisankan da yake da rai madawwami a cikinsa. (aiōnios )
Whosoever hateth his brother is a murderer. And you know that no murderer hath eternal life abiding in himself. (aiōnios )
16 Yadda muka san ƙauna ke nan, wato, Yesu Kiristi ya ba da ransa dominmu. Ya kamata mu ma mu ba da rayukanmu domin’yan’uwanmu.
In this we have known the charity of God, because he hath laid down his life for us: and we ought to lay down our lives for the brethren.
17 In wani yana da arziki, ya kuma ga ɗan’uwansa cikin rashi, bai kuwa taimake shi ba, anya, ƙaunar Allah tana a cikinsa kuwa?
He that hath the substance of this world, and shall see his brother in need, and shall shut up his bowels from him: how doth the charity of God abide in him?
18 ’Ya’yana ƙaunatattu, kada mu yi ƙauna da fatar baki kawai, sai dai mu nuna ta ta wurin aikatawa da kuma gaskiya.
My little children, let us not love in word, nor in tongue, but in deed, and in truth.
19 Ta haka muka san cewa mu na gaskiya ne, kuma za mu iya tsaya a gaban Allah ba tare da rawar jiki ba.
In this we know that we are of the truth: and in his sight shall persuade our hearts.
20 Idan zuciyarmu ta nuna mana muna da laifi, mun san cewa Allah ya fi zuciyarmu, ya kuma san dukan kome.
For if our heart reprehend us, God is greater than our heart, and knoweth all things.
21 Abokaina ƙaunatattu, in zukatanmu ba su ba mu laifi ba, muna da ƙarfin halin tsayawa a gaban Allah ke nan.
Dearly beloved, if our heart do not reprehend us, we have confidence towards God:
22 Muna kuma samun dukan abin da muka roƙa daga gare shi, domin muna biyayya da umarnansa, muna kuma yin abin da ya gamshe shi.
And whatsoever we shall ask, we shall receive of him: because we keep his commandments, and do those things which are pleasing in his sight.
23 Umarninsa kuwa shi ne, mu gaskata da sunan Ɗansa, Yesu Kiristi, mu kuma ƙaunaci juna kamar yadda ya umarce mu.
And this is his commandment, that we should believe in the name of his Son Jesus Christ: and love one another, as he hath given commandment unto us.
24 Waɗanda suke biyayya da umarnansa kuwa suna rayuwa a cikinsa, shi kuma a cikinsu. Ta haka muka san cewa yana raye a cikinmu. Mun san haka ta wurin Ruhun da ya ba mu.
And he that keepeth his commandments, abideth in him, and he in him. And in this we know that he abideth in us, by the Spirit which he hath given us.