< 1 Yohanna 2 >
1 ’Ya’yana ƙaunatattu, ina rubuta muku wannan ne don kada ku yi zunubi. Amma in wani ya yi zunubi, muna da wani wanda yake magana da Uba don taimakonmu, wato, Yesu Kiristi, Mai Adalci.
My little children, I write these things unto you, that ye may not sin. And if any man sin, we have an advocate with the Father, Jesus Christ the righteous.
2 Shi ne hadayar kafara saboda zunubanmu, kuma ba don namu kaɗai ba amma har ma da zunuban duniya duka.
And He is the propitiation for our sins; and not for ours only, but also for the sins of the whole world.
3 Ta haka za mu tabbata cewa mun san shi in muna yin biyayya da umarnansa.
And by this we know that we have known Him, if we keep his commandments.
4 Mutumin da ya ce, “Na san shi,” amma ba ya yin abin da ya umarta, maƙaryaci ne, gaskiya kuwa ba ta cikinsa.
He that saith, I know Him, and keepeth not his commandments, is a liar, and the truth is not in him.
5 Amma in wani ya yi biyayya da maganarsa, ƙaunar Allah ta zama cikakkiya ke nan a cikinsa. Ta haka muka san cewa muna cikinsa.
But whosoever keepeth his word, in him verily is the love of God perfected: and by this we know that we are in Him.
6 Duk wanda ya ce yana rayuwa a cikinsa dole yă yi tafiya kamar yadda Yesu ya yi.
He that saith, he abideth in Him, ought himself also so to walk even as He walked.
7 Abokaina ƙaunatattu, ba sabon umarni nake rubuta muku ba, a’a, daɗaɗɗen umarnin nan ne, wanda kuke da shi tun farko. Wannan tsohon umarni shi ne saƙon da kuka riga kuka ji.
Brethren, I write not a new commandment unto you, but an old commandment which ye had from the beginning: the old commandment is the word which ye have heard from the beginning:
8 Duk da haka ina rubuta muku sabon umarni; ana ganin gaskiyar umarnin a cikinsa da kuma cikinku, gama duhu yana shuɗewa, haske na gaskiya kuwa yana haskakawa.
though I write it again as a new commandment, which is truth in Him and in you: because the darkness is past, and the true light now shineth.
9 Duk wanda ya ce yana cikin haske yana kuma ƙin ɗan’uwansa, ashe a duhu yake har yanzu.
Now he that saith he is in the light, and hateth his brother, is still in darkness:
10 Duk wanda yake ƙaunar ɗan’uwansa, a cikin hasken yake rayuwa ke nan, kuma babu wani abin da yake cikinsa da zai sa yă yi tuntuɓe.
whereas, he that loveth his brother, abideth in the light, and is in no danger of stumbling.
11 Amma duk wanda yake ƙin ɗan’uwansa, cikin duhu yake, yana kuma tafiya cikin duhu ke nan; bai ma san inda za shi ba, domin duhun ya makanta shi.
But he, that hateth his brother, is in darkness, and walketh in darkness, and knoweth not where he goeth, because the darkness hath blinded his eyes.
12 Ina rubuta muku,’ya’yana ƙaunatattu, domin an gafarta muku zunubanku saboda sunansa.
I write unto you, little children, because for his sake your sins are forgiven you:
13 Ina rubuta muku, ubanni, domin kun san shi wanda yake tun farko. Ina rubuta muku, samari, domin kun ci nasara a kan mugun nan.
I write unto you, fathers, because ye have known Him that is from the beginning: and I write unto you, young men, because ye have overcome the wicked one. Yea I have written to you, little children, because ye have known the Father:
14 Ina rubuta muku,’ya’yana ƙaunatattu, domin kun san Uba. Ina rubuta muku, ubanni, domin kun san shi wanda yake tun farko. Ina rubuta muku, samari, domin kuna da ƙarfi, maganar Allah kuwa tana zaune a cikinku, kun kuma ci nasara a kan mugun nan.
I have written unto you, fathers, because ye have known Him that is from the beginning: and I have written to you, young men, because ye are strong, and the word of God abideth in you, and ye have overcome the wicked one---
15 Kada ku ƙaunaci duniya, ko wani abin da yake cikinta. In wani yana ƙaunar duniya, ƙaunar Uba ba ta cikinsa.
Love not the world, nor the things that are in the world; for if any one love the world to excess, the love of the Father is not in him.
16 Gama duk abin da yake na duniya, kamar sha’awace-sha’awacen mutuntaka, sha’awar idanunsa, da kuma taƙama da abin da yake da shi, yake kuma yi, ba daga wurin Uba suke fitowa ba sai dai daga duniya.
For all that is in the world, the desire of the flesh, and the desire of the eyes, and the pride of life, is not of the Father, but of the world.
17 Duniya da sha’awace-sha’awacenta suna shuɗewa, amma mutumin da yake aikata nufin Allah, zai rayu har abada. (aiōn )
And the world passeth away, and the desire of it: but he, that doth the will of God, abideth for ever. (aiōn )
18 ’Ya’yana ƙaunatattu, waɗannan su ne kwanakin ƙarshe; kuma kamar yadda kuka ji cewa magabcin Kiristi yana zuwa, ko yanzu ma abokan gāban Kiristi da yawa sun zo. Ta haka muka san cewa kwanakin ƙarshe sun iso.
Little children, it is the last time: and as ye have heard that an antichrist will come, there are even now many antichrists, whereby we know that it is the last time.
19 Waɗannan masu gāba da Kiristi suna cikinmu a dā, amma sun bar mu, don tun dā ma su ba namu ba ne. Ai, da su namu ne, da har yanzu suna tare da mu. Amma sun bar mu, wannan ya nuna a fili cewa su ba namu ba ne.
They went out from us, but they were not of us: for if they had been indeed of us, they would have continued with us; but this was done that they might be made manifest, because all, that are with us, are not indeed of us.
20 Amma ku kam, kuna da shafewa daga wurin Mai Tsarkin nan, kuma dukanku kun san gaskiya.
And ye have an unction from the holy One, and know all.
21 Ina rubuta muku ba domin ba ku san gaskiya ba ne, a’a, sai dai domin kun santa, kun kuma san cewa babu yadda ƙarya za tă fito daga gaskiya.
I have not therefore written to you, because ye know not the truth; but because ye know it, and that no lie is of the truth.
22 Wane ne maƙaryaci? Ai, shi ne mutumin da yake mūsun cewa Yesu shi ne Kiristi. Irin wannan mutum shi ne magabcin Kiristi, ya yi mūsun Uban da kuma Ɗan.
Who is a liar, if not he who denieth that Jesus is the Christ? This is the antichrist, that denieth the Father as well as the Son;
23 Ba wanda yake mūsun Ɗan, sa’an nan yă ce yana da Uban; duk wanda ya yarda da Ɗan, yana da Uban a cikinsa ke nan.
for whosoever denieth the Son, hath not the Father: but he that confesseth the Son acknowledgeth the Father also.
24 Ku lura fa cewa abin da kuka ji daga farko, bari yă ci gaba da kasance a cikinku. In kuwa ya ci gaba da zama a cikinku, za ku kasance a cikin Ɗan, da kuma a cikin Uban.
Let that therefore, which ye have heard from the beginning, abide in you: for if that, which ye heard from the beginning, remain in you, ye also will remain in the Son and in the Father.
25 Wannan shi ne abin da ya yi mana alkawari, wato, rai madawwami. (aiōnios )
And this is the promise which He hath promised us, even eternal life. (aiōnios )
26 Ina rubuta muku waɗannan abubuwa ne game da waɗanda suke ƙoƙari su sa ku kauce.
These things have I written unto you concerning those who would seduce you.
27 Game da ku kuwa, shafan nan da kuka karɓa daga gare shi tana nan a cikinku, ba kwa kuma bukata wani yă koyar da ku. Amma kamar yadda shafan nan tasa tana koya muku kome, ita kuwa gaskiya ce ba ƙarya ba, yadda dai ta koya muku, to, sai ku zauna a cikinsa.
But the unction, which ye have received from Him, abideth in you; and therefore ye have no need that any should teach you: since this very unction teacheth you concerning all things, and is truth and not falshood; even as that hath taught you, abide in Him.
28 Yanzu fa, ya ku’ya’yana ƙaunatattu, sai ku ci gaba a cikinsa, domin sa’ad da ya bayyana, mu iya tsaya gabagadi babu kunya a dawowarsa.
And now, little children, abide, I say, in Him; that, when He shall appear, we may have confidence, and may not be ashamed before Him at his coming.
29 In kun san cewa shi mai adalci ne, to, kun dai san cewa duk mai aikata abin da yake daidai haifaffensa ne.
If ye know that He is righteous, ye know that every one, who practiseth righteousness, is born of Him.