< 1 Yohanna 2 >
1 ’Ya’yana ƙaunatattu, ina rubuta muku wannan ne don kada ku yi zunubi. Amma in wani ya yi zunubi, muna da wani wanda yake magana da Uba don taimakonmu, wato, Yesu Kiristi, Mai Adalci.
My little children, these things I write to you, that ye sin not. And if any man sinneth, we have an advocate with the Father, Jesus Christ the righteous:
2 Shi ne hadayar kafara saboda zunubanmu, kuma ba don namu kaɗai ba amma har ma da zunuban duniya duka.
And he is the propitiation for our sins: and not for ours only, but also for the sins of the whole world.
3 Ta haka za mu tabbata cewa mun san shi in muna yin biyayya da umarnansa.
And by this we do know that we know him, if we keep his commandments.
4 Mutumin da ya ce, “Na san shi,” amma ba ya yin abin da ya umarta, maƙaryaci ne, gaskiya kuwa ba ta cikinsa.
He that saith, I know him, and keepeth not his commandments, is a liar, and the truth is not in him.
5 Amma in wani ya yi biyayya da maganarsa, ƙaunar Allah ta zama cikakkiya ke nan a cikinsa. Ta haka muka san cewa muna cikinsa.
But whoever keepeth his word, in him verily is the love of God perfected: by this we know that we are in him.
6 Duk wanda ya ce yana rayuwa a cikinsa dole yă yi tafiya kamar yadda Yesu ya yi.
He that saith he abideth in him ought himself also so to walk, even as he walked.
7 Abokaina ƙaunatattu, ba sabon umarni nake rubuta muku ba, a’a, daɗaɗɗen umarnin nan ne, wanda kuke da shi tun farko. Wannan tsohon umarni shi ne saƙon da kuka riga kuka ji.
Brethren, I write no new commandment to you, but an old commandment which ye had from the beginning. The old commandment is the word which ye have heard from the beginning.
8 Duk da haka ina rubuta muku sabon umarni; ana ganin gaskiyar umarnin a cikinsa da kuma cikinku, gama duhu yana shuɗewa, haske na gaskiya kuwa yana haskakawa.
Again, a new commandment I write to you, which thing is true in him and in you: because the darkness is past, and the true light now shineth.
9 Duk wanda ya ce yana cikin haske yana kuma ƙin ɗan’uwansa, ashe a duhu yake har yanzu.
He that saith he is in the light, and hateth his brother, is in darkness even until now.
10 Duk wanda yake ƙaunar ɗan’uwansa, a cikin hasken yake rayuwa ke nan, kuma babu wani abin da yake cikinsa da zai sa yă yi tuntuɓe.
He that loveth his brother abideth in the light, and there is no cause for stumbling in him.
11 Amma duk wanda yake ƙin ɗan’uwansa, cikin duhu yake, yana kuma tafiya cikin duhu ke nan; bai ma san inda za shi ba, domin duhun ya makanta shi.
But he that hateth his brother is in darkness, and walketh in darkness, and knoweth not where he goeth, because that darkness hath blinded his eyes.
12 Ina rubuta muku,’ya’yana ƙaunatattu, domin an gafarta muku zunubanku saboda sunansa.
I write to you, little children, because your sins are forgiven you for his name’s sake.
13 Ina rubuta muku, ubanni, domin kun san shi wanda yake tun farko. Ina rubuta muku, samari, domin kun ci nasara a kan mugun nan.
I write to you, fathers, because ye have known him that is from the beginning. I write to you, young men, because ye have overcome the wicked one. I write to you, little children, because ye have known the Father.
14 Ina rubuta muku,’ya’yana ƙaunatattu, domin kun san Uba. Ina rubuta muku, ubanni, domin kun san shi wanda yake tun farko. Ina rubuta muku, samari, domin kuna da ƙarfi, maganar Allah kuwa tana zaune a cikinku, kun kuma ci nasara a kan mugun nan.
I have written to you, fathers, because ye have known him that is from the beginning. I have written to you, young men, because ye are strong, and the word of God abideth in you, and ye have overcome the wicked one.
15 Kada ku ƙaunaci duniya, ko wani abin da yake cikinta. In wani yana ƙaunar duniya, ƙaunar Uba ba ta cikinsa.
Love not the world, neither the things that are in the world. If any man loveth the world, the love of the Father is not in him.
16 Gama duk abin da yake na duniya, kamar sha’awace-sha’awacen mutuntaka, sha’awar idanunsa, da kuma taƙama da abin da yake da shi, yake kuma yi, ba daga wurin Uba suke fitowa ba sai dai daga duniya.
For all that is in the world, the lust of the flesh, and the lust of the eyes, and the pride of life, is not from the Father, but is from the world.
17 Duniya da sha’awace-sha’awacenta suna shuɗewa, amma mutumin da yake aikata nufin Allah, zai rayu har abada. (aiōn )
And the world passeth away, and its lust: but he that doeth the will of God abideth for ever. (aiōn )
18 ’Ya’yana ƙaunatattu, waɗannan su ne kwanakin ƙarshe; kuma kamar yadda kuka ji cewa magabcin Kiristi yana zuwa, ko yanzu ma abokan gāban Kiristi da yawa sun zo. Ta haka muka san cewa kwanakin ƙarshe sun iso.
Little children, it is the last time: and as ye have heard that antichrist cometh, even now are there many antichrists; by which we know that it is the last time.
19 Waɗannan masu gāba da Kiristi suna cikinmu a dā, amma sun bar mu, don tun dā ma su ba namu ba ne. Ai, da su namu ne, da har yanzu suna tare da mu. Amma sun bar mu, wannan ya nuna a fili cewa su ba namu ba ne.
They went out from us, but they were not of us; for if they had been of us, they would no doubt have continued with us: but they went out, that they might be shown that they were not all of us.
20 Amma ku kam, kuna da shafewa daga wurin Mai Tsarkin nan, kuma dukanku kun san gaskiya.
But ye have an unction from the Holy One, and ye know all things.
21 Ina rubuta muku ba domin ba ku san gaskiya ba ne, a’a, sai dai domin kun santa, kun kuma san cewa babu yadda ƙarya za tă fito daga gaskiya.
I have not written to you because ye know not the truth, but because ye know it, and that no lie is of the truth.
22 Wane ne maƙaryaci? Ai, shi ne mutumin da yake mūsun cewa Yesu shi ne Kiristi. Irin wannan mutum shi ne magabcin Kiristi, ya yi mūsun Uban da kuma Ɗan.
Who is a liar but he that denieth that Jesus is the Christ? He is antichrist, that denieth the Father and the Son.
23 Ba wanda yake mūsun Ɗan, sa’an nan yă ce yana da Uban; duk wanda ya yarda da Ɗan, yana da Uban a cikinsa ke nan.
Whoever denieth the Son, the same hath not the Father: (but) he that confesseth the Son hath the Father also.
24 Ku lura fa cewa abin da kuka ji daga farko, bari yă ci gaba da kasance a cikinku. In kuwa ya ci gaba da zama a cikinku, za ku kasance a cikin Ɗan, da kuma a cikin Uban.
Let that therefore abide in you, which ye have heard from the beginning. If that which ye have heard from the beginning shall remain in you, ye also shall continue in the Son, and in the Father.
25 Wannan shi ne abin da ya yi mana alkawari, wato, rai madawwami. (aiōnios )
And this is the promise that he hath promised us, even eternal life. (aiōnios )
26 Ina rubuta muku waɗannan abubuwa ne game da waɗanda suke ƙoƙari su sa ku kauce.
These things have I written to you concerning them that seduce you.
27 Game da ku kuwa, shafan nan da kuka karɓa daga gare shi tana nan a cikinku, ba kwa kuma bukata wani yă koyar da ku. Amma kamar yadda shafan nan tasa tana koya muku kome, ita kuwa gaskiya ce ba ƙarya ba, yadda dai ta koya muku, to, sai ku zauna a cikinsa.
But the anointing which ye have received from him abideth in you, and ye need not that any man should teach you: but as the same anointing teacheth you concerning all things, and is truth, and is no lie, and even as it hath taught you, ye shall abide in him.
28 Yanzu fa, ya ku’ya’yana ƙaunatattu, sai ku ci gaba a cikinsa, domin sa’ad da ya bayyana, mu iya tsaya gabagadi babu kunya a dawowarsa.
And now, little children, abide in him; that, when he shall appear, we may have confidence, and not be ashamed before him at his coming.
29 In kun san cewa shi mai adalci ne, to, kun dai san cewa duk mai aikata abin da yake daidai haifaffensa ne.
If ye know that he is righteous, ye know that every one that doeth righteousness is born of him.