< 1 Yohanna 2 >

1 ’Ya’yana ƙaunatattu, ina rubuta muku wannan ne don kada ku yi zunubi. Amma in wani ya yi zunubi, muna da wani wanda yake magana da Uba don taimakonmu, wato, Yesu Kiristi, Mai Adalci.
My little children, I write these things to you, that you may not sin: and yet, if any one sin, we have an advocate with the Father, Jesus Christ the righteous.
2 Shi ne hadayar kafara saboda zunubanmu, kuma ba don namu kaɗai ba amma har ma da zunuban duniya duka.
And he is the expiation for our sins: not for ours only, but for the sins of the whole world.
3 Ta haka za mu tabbata cewa mun san shi in muna yin biyayya da umarnansa.
And by this we know that we do know him, if we keep his commandments.
4 Mutumin da ya ce, “Na san shi,” amma ba ya yin abin da ya umarta, maƙaryaci ne, gaskiya kuwa ba ta cikinsa.
He that says, I know him, and keeps not his commandments, is a liar, and the truth is not in him.
5 Amma in wani ya yi biyayya da maganarsa, ƙaunar Allah ta zama cikakkiya ke nan a cikinsa. Ta haka muka san cewa muna cikinsa.
But whoever keeps his word, in him truly is the love of God perfected: by this we know that we are in him.
6 Duk wanda ya ce yana rayuwa a cikinsa dole yă yi tafiya kamar yadda Yesu ya yi.
He that says, he abides in him, ought himself also so to walk, even as he walked.
7 Abokaina ƙaunatattu, ba sabon umarni nake rubuta muku ba, a’a, daɗaɗɗen umarnin nan ne, wanda kuke da shi tun farko. Wannan tsohon umarni shi ne saƙon da kuka riga kuka ji.
Beloved, I write no new commandment to you, but an old commandment, which you have had from the beginning; the old commandment is the word, which you have heard from the beginning.
8 Duk da haka ina rubuta muku sabon umarni; ana ganin gaskiyar umarnin a cikinsa da kuma cikinku, gama duhu yana shuɗewa, haske na gaskiya kuwa yana haskakawa.
Again, a new commandment I do write to you, which is true as it respects him and you; because the darkness is past, and the true light now shines.
9 Duk wanda ya ce yana cikin haske yana kuma ƙin ɗan’uwansa, ashe a duhu yake har yanzu.
He that says he is in the light, and hates his brother, is in darkness till now.
10 Duk wanda yake ƙaunar ɗan’uwansa, a cikin hasken yake rayuwa ke nan, kuma babu wani abin da yake cikinsa da zai sa yă yi tuntuɓe.
He that loves his brother abides in the light, and there is in him no cause for offense.
11 Amma duk wanda yake ƙin ɗan’uwansa, cikin duhu yake, yana kuma tafiya cikin duhu ke nan; bai ma san inda za shi ba, domin duhun ya makanta shi.
He that hates his brother is in darkness, and walks in darkness; and he knows not whither he goes, because darkness has blinded his eyes.
12 Ina rubuta muku,’ya’yana ƙaunatattu, domin an gafarta muku zunubanku saboda sunansa.
I write to you, little children, because your sins are forgiven for his name’s sake.
13 Ina rubuta muku, ubanni, domin kun san shi wanda yake tun farko. Ina rubuta muku, samari, domin kun ci nasara a kan mugun nan.
I write to you, fathers, because you have known him that is from the beginning. I write to you, young men, because you have overcome the wicked one. I write to you, my little children, because you have known the Father.
14 Ina rubuta muku,’ya’yana ƙaunatattu, domin kun san Uba. Ina rubuta muku, ubanni, domin kun san shi wanda yake tun farko. Ina rubuta muku, samari, domin kuna da ƙarfi, maganar Allah kuwa tana zaune a cikinku, kun kuma ci nasara a kan mugun nan.
I have written to you, fathers, because you have known him that is from the beginning. I have written to you, young men, because you are strong, and the word of God abides in you, and you have overcome the wicked one.
15 Kada ku ƙaunaci duniya, ko wani abin da yake cikinta. In wani yana ƙaunar duniya, ƙaunar Uba ba ta cikinsa.
Love not the world, nor the things that are in the world. If any man loves the world, the love of the Father is not in him.
16 Gama duk abin da yake na duniya, kamar sha’awace-sha’awacen mutuntaka, sha’awar idanunsa, da kuma taƙama da abin da yake da shi, yake kuma yi, ba daga wurin Uba suke fitowa ba sai dai daga duniya.
For all that is in the world, the desire of the flesh, and the desire of the eyes, and the pride of life, is not of the Father, but is of the world.
17 Duniya da sha’awace-sha’awacenta suna shuɗewa, amma mutumin da yake aikata nufin Allah, zai rayu har abada. (aiōn g165)
And the world and its desire passes away: but he that does the will of God, abides forever. (aiōn g165)
18 ’Ya’yana ƙaunatattu, waɗannan su ne kwanakin ƙarshe; kuma kamar yadda kuka ji cewa magabcin Kiristi yana zuwa, ko yanzu ma abokan gāban Kiristi da yawa sun zo. Ta haka muka san cewa kwanakin ƙarshe sun iso.
Little children, it is the last time; and, as you have heard that the antichrist is coming, even now there are many antichrists; by which we know that it is the last time.
19 Waɗannan masu gāba da Kiristi suna cikinmu a dā, amma sun bar mu, don tun dā ma su ba namu ba ne. Ai, da su namu ne, da har yanzu suna tare da mu. Amma sun bar mu, wannan ya nuna a fili cewa su ba namu ba ne.
They went out from us, but they were not of us: for, if they had been of us, they would have remained with us; but they went out, that they might be made manifest that they were not all of us.
20 Amma ku kam, kuna da shafewa daga wurin Mai Tsarkin nan, kuma dukanku kun san gaskiya.
And you have an anointing from the Holy One, and know all things.
21 Ina rubuta muku ba domin ba ku san gaskiya ba ne, a’a, sai dai domin kun santa, kun kuma san cewa babu yadda ƙarya za tă fito daga gaskiya.
I have not written to you because you do not know the truth, but because you know it, and because no lie is of the truth.
22 Wane ne maƙaryaci? Ai, shi ne mutumin da yake mūsun cewa Yesu shi ne Kiristi. Irin wannan mutum shi ne magabcin Kiristi, ya yi mūsun Uban da kuma Ɗan.
Who is a liar, but he that denies that Jesus is the Christ? He is antichrist, who denies the Father and the Son.
23 Ba wanda yake mūsun Ɗan, sa’an nan yă ce yana da Uban; duk wanda ya yarda da Ɗan, yana da Uban a cikinsa ke nan.
Whoever denies the Son, has not the Father: he that confesses the Son, has the Father also.
24 Ku lura fa cewa abin da kuka ji daga farko, bari yă ci gaba da kasance a cikinku. In kuwa ya ci gaba da zama a cikinku, za ku kasance a cikin Ɗan, da kuma a cikin Uban.
Let that, therefore, abide in you which you have heard from the beginning. If that abide in you which you have heard from the beginning, you also shall abide in the Son and in the Father.
25 Wannan shi ne abin da ya yi mana alkawari, wato, rai madawwami. (aiōnios g166)
And this is the promise which he has promised us, even eternal life. (aiōnios g166)
26 Ina rubuta muku waɗannan abubuwa ne game da waɗanda suke ƙoƙari su sa ku kauce.
I have written these things to you concerning those who deceive you.
27 Game da ku kuwa, shafan nan da kuka karɓa daga gare shi tana nan a cikinku, ba kwa kuma bukata wani yă koyar da ku. Amma kamar yadda shafan nan tasa tana koya muku kome, ita kuwa gaskiya ce ba ƙarya ba, yadda dai ta koya muku, to, sai ku zauna a cikinsa.
And the anointing which you have received from him abides in you; and you have no need that any one should teach you: but, as the same anointing teaches you concerning all things, and is true and is no lie, even as it has taught you, abide in it.
28 Yanzu fa, ya ku’ya’yana ƙaunatattu, sai ku ci gaba a cikinsa, domin sa’ad da ya bayyana, mu iya tsaya gabagadi babu kunya a dawowarsa.
And now, little children, abide in him, that when he appears, we may have confidence, and may not be made ashamed by him at his coming.
29 In kun san cewa shi mai adalci ne, to, kun dai san cewa duk mai aikata abin da yake daidai haifaffensa ne.
If you know that he is righteous, you know that every one that works righteousness has been begotten by him.

< 1 Yohanna 2 >