< 1 Yohanna 2 >

1 ’Ya’yana ƙaunatattu, ina rubuta muku wannan ne don kada ku yi zunubi. Amma in wani ya yi zunubi, muna da wani wanda yake magana da Uba don taimakonmu, wato, Yesu Kiristi, Mai Adalci.
Mine Børn! dette skriver jeg til eder, for at I ikke skulle synde. Og dersom nogen synder, have vi en Talsmand hos Faderen, Jesus Kristus, den retfærdige,
2 Shi ne hadayar kafara saboda zunubanmu, kuma ba don namu kaɗai ba amma har ma da zunuban duniya duka.
og han er en Forsoning for vore Synder, dog ikke alene for vore, men også for hele Verdens.
3 Ta haka za mu tabbata cewa mun san shi in muna yin biyayya da umarnansa.
Og derpå kende vi, at vi have kendt ham, om vi holde hans Bud.
4 Mutumin da ya ce, “Na san shi,” amma ba ya yin abin da ya umarta, maƙaryaci ne, gaskiya kuwa ba ta cikinsa.
Den, som siger: "Jeg kender ham," og ikke holder hans Bud. han er en Løgner, og i ham er Sandheden ikke;
5 Amma in wani ya yi biyayya da maganarsa, ƙaunar Allah ta zama cikakkiya ke nan a cikinsa. Ta haka muka san cewa muna cikinsa.
men den, som holder hans Ord, i ham er sandelig Guds Kærlighed fuldkommet. Derpå kende vi, at vi ere i ham.
6 Duk wanda ya ce yana rayuwa a cikinsa dole yă yi tafiya kamar yadda Yesu ya yi.
Den, som siger, at han bliver i ham, han er også skyldig selv at vandre således, som han vandrede.
7 Abokaina ƙaunatattu, ba sabon umarni nake rubuta muku ba, a’a, daɗaɗɗen umarnin nan ne, wanda kuke da shi tun farko. Wannan tsohon umarni shi ne saƙon da kuka riga kuka ji.
I elskede, jeg skriver til eder ikke et nyt Bud, men et gammelt Bud, som I have haft fra Begyndelsen. Det gamle Bud er det Ord, som I have hørt.
8 Duk da haka ina rubuta muku sabon umarni; ana ganin gaskiyar umarnin a cikinsa da kuma cikinku, gama duhu yana shuɗewa, haske na gaskiya kuwa yana haskakawa.
Og dog skriver jeg til eder et nyt Bud, hvilket er sandt i ham og i eder, thi Mørket drager bort, og det sande Lys skinner allerede.
9 Duk wanda ya ce yana cikin haske yana kuma ƙin ɗan’uwansa, ashe a duhu yake har yanzu.
Den, som siger, at han er i Lyset, og hader sin Broder, han er i Mørket endnu.
10 Duk wanda yake ƙaunar ɗan’uwansa, a cikin hasken yake rayuwa ke nan, kuma babu wani abin da yake cikinsa da zai sa yă yi tuntuɓe.
Den, som elsker sin Broder, bliver i Lyset, og der er ingen Forargelse i ham.
11 Amma duk wanda yake ƙin ɗan’uwansa, cikin duhu yake, yana kuma tafiya cikin duhu ke nan; bai ma san inda za shi ba, domin duhun ya makanta shi.
Men den, som hader sin Broder, er i Mørket og vandrer i Mørket, og han ved ikke, hvor han går hen, fordi Mørket har blindet hans Øjne.
12 Ina rubuta muku,’ya’yana ƙaunatattu, domin an gafarta muku zunubanku saboda sunansa.
Jeg skriver til eder, mine Børn! fordi eders Synder ere eder forladte for hans Navns Skyld.
13 Ina rubuta muku, ubanni, domin kun san shi wanda yake tun farko. Ina rubuta muku, samari, domin kun ci nasara a kan mugun nan.
Jeg skriver til eder, I Fædre! fordi I kende ham, som er fra Begyndelsen. Jeg skriver til eder, I unge! fordi I have overvundet den onde. Jeg har skrevet til eder, mine Børn! fordi I kende Faderen.
14 Ina rubuta muku,’ya’yana ƙaunatattu, domin kun san Uba. Ina rubuta muku, ubanni, domin kun san shi wanda yake tun farko. Ina rubuta muku, samari, domin kuna da ƙarfi, maganar Allah kuwa tana zaune a cikinku, kun kuma ci nasara a kan mugun nan.
Jeg har skrevet til eder, I Fædre! fordi I kende ham, som er fra Begyndelsen. Jeg har skrevet til eder, I unge! fordi I ere stærke, og Guds Ord bliver i eder, og I have overvundet den onde.
15 Kada ku ƙaunaci duniya, ko wani abin da yake cikinta. In wani yana ƙaunar duniya, ƙaunar Uba ba ta cikinsa.
Elsker ikke Verden, ikke heller de Ting, som ere i Verden! Dersom nogen elsker Verden, er Faderens Kærlighed ikke i ham.
16 Gama duk abin da yake na duniya, kamar sha’awace-sha’awacen mutuntaka, sha’awar idanunsa, da kuma taƙama da abin da yake da shi, yake kuma yi, ba daga wurin Uba suke fitowa ba sai dai daga duniya.
Thi alt det, som er i Verden, Kødets Lyst og Øjnenes Lyst og Livets Hoffærdighed, er ikke af Faderen, men af Verden.
17 Duniya da sha’awace-sha’awacenta suna shuɗewa, amma mutumin da yake aikata nufin Allah, zai rayu har abada. (aiōn g165)
Og Verden forgår og dens Lyst; men den, som gør Guds Villie, bliver til evig Tid. (aiōn g165)
18 ’Ya’yana ƙaunatattu, waɗannan su ne kwanakin ƙarshe; kuma kamar yadda kuka ji cewa magabcin Kiristi yana zuwa, ko yanzu ma abokan gāban Kiristi da yawa sun zo. Ta haka muka san cewa kwanakin ƙarshe sun iso.
Mine Børn! det er den sidste Time, og som I have hørt, at Antikrist kommer, således ere nu mange Antikrister fremtrådte; deraf kende vi, at det er den sidste Time.
19 Waɗannan masu gāba da Kiristi suna cikinmu a dā, amma sun bar mu, don tun dā ma su ba namu ba ne. Ai, da su namu ne, da har yanzu suna tare da mu. Amma sun bar mu, wannan ya nuna a fili cewa su ba namu ba ne.
De ere udgåede fra os, men de vare ikke af os; thi dersom de havde været af os, da vare de blevne hos os. Dog, det var, for at det skulde blive åbenbart, at de ikke alle ere af os.
20 Amma ku kam, kuna da shafewa daga wurin Mai Tsarkin nan, kuma dukanku kun san gaskiya.
Og I have Salvelse fra den hellige og vide alt.
21 Ina rubuta muku ba domin ba ku san gaskiya ba ne, a’a, sai dai domin kun santa, kun kuma san cewa babu yadda ƙarya za tă fito daga gaskiya.
Jeg har ikke skrevet til eder, fordi I ikke vide Sandheden; men fordi I vide den og vide, at ingen Løgn er af Sandheden.
22 Wane ne maƙaryaci? Ai, shi ne mutumin da yake mūsun cewa Yesu shi ne Kiristi. Irin wannan mutum shi ne magabcin Kiristi, ya yi mūsun Uban da kuma Ɗan.
Hvem er Løgneren uden den, som nægter, at Jesus er Kristus? Denne er Antikristen, som fornægter Faderen og Sønnen.
23 Ba wanda yake mūsun Ɗan, sa’an nan yă ce yana da Uban; duk wanda ya yarda da Ɗan, yana da Uban a cikinsa ke nan.
Hver den, som fornægter Sønnen, har ej heller Faderen; den, som bekender Sønnen, har også Faderen.
24 Ku lura fa cewa abin da kuka ji daga farko, bari yă ci gaba da kasance a cikinku. In kuwa ya ci gaba da zama a cikinku, za ku kasance a cikin Ɗan, da kuma a cikin Uban.
Hvad I have hørt fra Begyndelsen, det blive i eder! Dersom det, som I have hørt fra Begyndelsen, bliver i eder, skulle også I blive i Sønnen og i Faderen.
25 Wannan shi ne abin da ya yi mana alkawari, wato, rai madawwami. (aiōnios g166)
Og dette er den Forjættelse, som han selv tilsagde os, det evige Liv. (aiōnios g166)
26 Ina rubuta muku waɗannan abubuwa ne game da waɗanda suke ƙoƙari su sa ku kauce.
Dette har jeg skrevet til eder om dem, som forføre eder.
27 Game da ku kuwa, shafan nan da kuka karɓa daga gare shi tana nan a cikinku, ba kwa kuma bukata wani yă koyar da ku. Amma kamar yadda shafan nan tasa tana koya muku kome, ita kuwa gaskiya ce ba ƙarya ba, yadda dai ta koya muku, to, sai ku zauna a cikinsa.
Og den Salvelse, som I fik af ham, bliver i eder, og I have ikke nødig, at nogen skal lære eder; men således som hans Salvelse lærer eder alt, er det også sandt og er ikke Løgn, og som den har lært eder, skulle I blive i ham.
28 Yanzu fa, ya ku’ya’yana ƙaunatattu, sai ku ci gaba a cikinsa, domin sa’ad da ya bayyana, mu iya tsaya gabagadi babu kunya a dawowarsa.
Og nu mine Børn! bliver i ham, for at vi, når han åbenbares, kunne have Frimodighed og ikke skulle blive til Skamme for ham ved hans Tilkommelse.
29 In kun san cewa shi mai adalci ne, to, kun dai san cewa duk mai aikata abin da yake daidai haifaffensa ne.
Dersom I vide, at han er retfærdig, da erkender, at hver den, som gør Retfærdighed, er født af ham.

< 1 Yohanna 2 >