< 1 Korintiyawa 1 >

1 Bulus, wanda aka kira domin yă zama manzon Kiristi Yesu, bisa ga nufin Allah, da kuma ɗan’uwanmu Sostenes,
Paulo, chamado apóstolo de Jesus Cristo pela vontade de Deus, e o irmão Sóstenes,
2 Zuwa ga ikkilisiyar Allah da take a Korint, da waɗanda aka tsarkake cikin Kiristi Yesu, aka kuma kira domin su zama masu tsarki, tare da dukan waɗanda suke ko’ina da suke kiran sunan Ubangijinmu Yesu Kiristi, Ubangijinsu da kuma namu.
À igreja de Deus que está em Corinto, aos santificados em Cristo Jesus, chamados santos, com todos os que em todo lugar invocam o nome de nosso Senhor Jesus Cristo, [Senhor] deles, e nosso;
3 Alheri da salama daga Allah Ubanmu, da Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
Graça [seja] convosco, e a paz de Deus nosso Pai, e do Senhor Jesus Cristo.
4 Ina gode wa Allah kullum dominku, saboda alherinsa da aka ba ku a cikin Kiristi Yesu.
Sempre agradeço ao meu Deus por causa de vós, pela graça de Deus, que é dada a vós em Cristo Jesus.
5 Gama a cikinsa kuka sami wadata ta kowace hanya, a cikin dukan maganarku, da kuma cikin dukan saninku
Que em todas as coisas estais enriquecidos nele, em toda palavra, e em todo conhecimento;
6 gama shaidarmu game da Kiristi ta tabbata a cikinku.
Assim como o testemunho de Jesus Cristo foi confirmado entre vós.
7 Saboda haka, ba ku rasa kowace baiwa ta ruhaniya ba, yayinda kuke jira da marmari, saboda bayyanuwar Ubangijinmu Yesu Kiristi.
De maneira que nenhum dom vos falta, enquanto esperais a manifestação do nosso Senhor Jesus Cristo,
8 Zai ƙarfafa ku har zuwa ƙarshe, domin ku zama marasa aibi a ranar Ubangijinmu Yesu Kiristi.
o qual também vos firmará até o fim, irrepreensíveis no dia de nosso Senhor Jesus Cristo.
9 Allah, wanda ya kira ku zuwa ga zumunci tare da Ɗansa Yesu Kiristi Ubangijinmu, shi mai aminci ne.
Fiel é Deus, por quem fostes chamados para a comunhão do seu Filho Jesus Cristo, nosso Senhor.
10 Ina roƙonku’yan’uwa, a cikin sunan Ubangijinmu Yesu Kiristi, dukanku ku yarda da juna, domin kada a sami tsattsaguwa a cikinku, domin kuma ku zama ɗaya, cikakku a cikin halinku da tunaninku.
Mas eu vos rogo, irmãos, pelo nome do nosso Senhor Jesus Cristo, que todos faleis uma mesma coisa, e não haja divisões entre vós; antes estejais juntos com o mesmo entendimento, e com a mesma opinião.
11 ’Yan’uwana, waɗansu daga iyalin gidan Kulos sun gaya mini cewa, akwai faɗa a cikinku.
Porque, meus irmãos, foi-me informado acerca de vós, pelos [da casa] de Cloé, de que há brigas entre vós.
12 Abin da nake nufi shi ne, ɗaya daga cikinku na cewa, “Ni ina bin Bulus,” wani na cewa, “Ni ina bin Afollos,” wani kuma, “Ni ina bin Kefas,” har wa yau wani kuma, “Ni ina bin Kiristi.”
E digo isto, que cada um de vós diz: “Eu sou de Paulo” e “Eu [sou] de Apolo” e “Eu [sou] de Cefas” e “Eu [sou] de Cristo”.
13 Kiristi a rabe ne? Bulus ne aka gicciye dominku? An yi muku baftisma a cikin sunan Bulus ne?
Cristo está dividido? Paulo foi crucificado por vós? Ou fostes vós batizados no nome de Paulo?
14 Ina godiya domin ban yi wa wani baftisma a cikinku ba, sai dai Kirisbus da Gayus kaɗai.
Agradeço a Deus que batizei nenhum de vós, a não ser Crispo e Gaio;
15 Don haka, ba wanda na iya cewa an yi muku baftisma a cikin sunana.
para que ninguém diga que eu tenha batizado em meu nome.
16 (I, na kuma yi wa iyalin gidan Istifanas baftisma, ban da wannan, ban tuna da wani da na yi masa baftisma ba.)
Também batizei aos da casa de Estefanas; além desses, não sei se batizei algum outro.
17 Gama Kiristi bai aike ni yin baftisma ba, sai dai wa’azin bishara ba da kalmomin hikimar mutum ba, domin kada gicciyen Kiristi ya rasa ikonsa.
Porque Cristo não me enviou para batizar, mas sim, para evangelizar; não com sabedoria de palavras, para que a cruz de Cristo não se torne inútil.
18 Gama saƙon gicciye wauta ne ga waɗanda suke hallaka, amma a gare mu, mu da ake ceto, ikon Allah ne.
Porque a palavra da cruz é loucura para os que perecem; mas para os que se salvam é poder de Deus.
19 Gama a rubuce yake cewa, “Zan rushe hikimar mai hikima, basirar mai azanci kuma zan rikita shi.”
Porque está escrito: Destruirei a sabedoria dos sábios, e aniquilarei a inteligência dos inteligentes.
20 Ina mai hikima? Ina mai zurfin bincike? Ina masana na wannan zamani? Ashe, Allah bai wofinta hikimar duniya ba? (aiōn g165)
Onde está o sábio? Onde está o escriba? Onde está o questionador desta era? Por acaso Deus não tornou a sabedoria deste mundo em loucura? (aiōn g165)
21 Gama tun da a cikin hikimar Allah, duniya a cikin hikimarta ba tă san shi ba, Allah ya ji daɗin ceton waɗanda suka ba da gaskiya ta wurin wautar wa’azin bishara.
Pois já que, na sabedoria de Deus, o mundo não conheceu a Deus pela sabedoria, Deus se agradou de salvar os que creem por meio da loucura da pregação.
22 Yahudawa suna so su ga alama, Hellenawa kuma suna neman hikima,
Porque os judeus pedem um sinal miraculoso, e os gregos buscam sabedoria.
23 amma mu, muna wa’azin Kiristi wanda aka gicciye ne, wanda ya zama dutsen tuntuɓe ga Yahudawa, wauta kuma ga Al’ummai,
Mas nós pregamos a Cristo crucificado, [que é] motivo de ofensa para os Judeus, e loucura para os gregos.
24 amma ga su waɗanda Allah ya kira, Yahudawa da Hellenawa, Kiristi ikon Allah ne, da kuma hikimar Allah.
Porém aos que são chamados, tanto judeus como gregos, Cristo [é] poder de Deus e sabedoria de Deus.
25 Gama wautar Allah ta fi hikimar mutum, kuma rashin ƙarfin Allah ya fi ƙarfin mutum.
Porque a loucura de Deus é mais sábia que os seres humanos; e a fraqueza de Deus é mais forte que os seres humanos.
26 ’Yan’uwa, ku tuna yadda kuke sa’ad da aka kira ku. Babu masu hikima da yawa a cikinku, bisa ga ganin mutum; babu masu iko da yawa, babu masu martaba da yawa bisa ga haihuwa.
Vede, pois, o vosso chamado, irmãos; pois dentre vós não [há] muitos sábios em sabedoria humana, nem muitos poderosos, nem muitos da elite.
27 Amma Allah ya zaɓi abubuwa masu wautata duniya, don yă kunyata masu hikima. Allah ya zaɓi abubuwa marasa ƙarfi na duniya, domin ya ba wa masu ƙarfi kunya.
Mas Deus escolheu as coisas loucas deste mundo para envergonhar as sábias; e Deus escolheu as fracas deste mundo para envergonhar as fortes.
28 Ya zaɓi abubuwa marasa martaba na wannan duniya da kuma abubuwan da aka rena da abubuwan da ba a ɗauka a bakin kome ba, domin a wofinta abubuwan da ake ganinsu da daraja,
E Deus escolheu as coisas desprezíveis deste mundo, e as sem valor, e as que não são, para reduzir a nada as que são;
29 domin kada wani ya yi taƙama a gabansa.
para que ninguém orgulhe de si mesmo diante dele.
30 Saboda Allah ne kuke cikin Kiristi Yesu, shi wanda ya zama hikima a gare mu daga Allah. Kiristi shi ne adalcinmu, da tsarkinmu, da kuma fansarmu.
Mas vós sois dele em Cristo Jesus, o qual, por parte de Deus, tornou-se para nós sabedoria, justiça, santificação, e resgate;
31 Saboda haka, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Duk wanda yake taƙama, ya yi taƙama a cikin Ubangiji.”
para que, assim como está escrito: “Aquele que se orgulha, orgulhe-se no Senhor”.

< 1 Korintiyawa 1 >