< 1 Korintiyawa 1 >

1 Bulus, wanda aka kira domin yă zama manzon Kiristi Yesu, bisa ga nufin Allah, da kuma ɗan’uwanmu Sostenes,
UPhawuli, obizelwe ukuba ngumpostoli kaJesu Khristu ngentando kaNkulunkulu, kanye lomzalwane wethu uSosithene.
2 Zuwa ga ikkilisiyar Allah da take a Korint, da waɗanda aka tsarkake cikin Kiristi Yesu, aka kuma kira domin su zama masu tsarki, tare da dukan waɗanda suke ko’ina da suke kiran sunan Ubangijinmu Yesu Kiristi, Ubangijinsu da kuma namu.
Ebandleni likaNkulunkulu eKhorinte, kulabo abangcweliswe kuJesu Khristu babizelwa ukuba ngabangcwele bakhe kanye labo bonke abasezindaweni zonke abakhuleka ebizweni leNkosi yethu uJesu Khristu, iNkosi yabo leyethu:
3 Alheri da salama daga Allah Ubanmu, da Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
Umusa lokuthula okuvela kuNkulunkulu uBaba leNkosini uJesu Khristu kakube kini.
4 Ina gode wa Allah kullum dominku, saboda alherinsa da aka ba ku a cikin Kiristi Yesu.
Ngihlezi ngimbonga kokuphela uNkulunkulu wami ngani, ngenxa yomusa wakhe eliwuphiweyo kuJesu Khristu.
5 Gama a cikinsa kuka sami wadata ta kowace hanya, a cikin dukan maganarku, da kuma cikin dukan saninku
Ngoba kuye linothiswe ngezindlela zonke, ekukhulumeni kwenu konke lasekwazini konke,
6 gama shaidarmu game da Kiristi ta tabbata a cikinku.
ngoba ubufakazi bethu ngoKhristu baqiniswa kini.
7 Saboda haka, ba ku rasa kowace baiwa ta ruhaniya ba, yayinda kuke jira da marmari, saboda bayyanuwar Ubangijinmu Yesu Kiristi.
Ngakho kalisileli lakusiphi isipho somoya lapho lilindele ngokutshiseka ukuba iNkosi yethu uJesu Khristu ibonakaliswe.
8 Zai ƙarfafa ku har zuwa ƙarshe, domin ku zama marasa aibi a ranar Ubangijinmu Yesu Kiristi.
Izaligcina liqinile kuze kube sekupheleni ukuze lingabi lasici ngosuku lweNkosi yethu uJesu Khristu.
9 Allah, wanda ya kira ku zuwa ga zumunci tare da Ɗansa Yesu Kiristi Ubangijinmu, shi mai aminci ne.
UNkulunkulu olibizele ekuhlanganyeleni leNdodana yakhe uJesu Khristu iNkosi yethu, uthembekile.
10 Ina roƙonku’yan’uwa, a cikin sunan Ubangijinmu Yesu Kiristi, dukanku ku yarda da juna, domin kada a sami tsattsaguwa a cikinku, domin kuma ku zama ɗaya, cikakku a cikin halinku da tunaninku.
Ngiyalincenga bazalwane, ngebizo leNkosi yethu uJesu Khristu, ukuba lonke livumelane ukuze kungabi lokwehlukana phakathi kwenu kanye lokuthi libe ngabamanyeneyo engqondweni lasemcabangweni.
11 ’Yan’uwana, waɗansu daga iyalin gidan Kulos sun gaya mini cewa, akwai faɗa a cikinku.
Bazalwane bami, abanye abendlu yakoKlowe bangitshele ukuthi kulezingxabano phakathi kwenu.
12 Abin da nake nufi shi ne, ɗaya daga cikinku na cewa, “Ni ina bin Bulus,” wani na cewa, “Ni ina bin Afollos,” wani kuma, “Ni ina bin Kefas,” har wa yau wani kuma, “Ni ina bin Kiristi.”
Engikutshoyo yilokhu: Omunye wenu uthi, “Mina ngilandela uPhawuli”; omunye uthi, “Mina ngilandela u-Apholo”; omunye uthi, “Mina ngilandela uKhefasi”; omunye laye uthi, “Mina ngilandela uKhristu.”
13 Kiristi a rabe ne? Bulus ne aka gicciye dominku? An yi muku baftisma a cikin sunan Bulus ne?
Kambe uKhristu wehlukene na? UPhawuli wake wabethelwa ngenxa yenu na? Labhaphathizwa ngebizo likaPhawuli na?
14 Ina godiya domin ban yi wa wani baftisma a cikinku ba, sai dai Kirisbus da Gayus kaɗai.
Ngibonga uNkulunkulu ngokuthi kangibhaphathizanga lamunye wenu ngaphandle kukaKhrispasi loGayiyasi,
15 Don haka, ba wanda na iya cewa an yi muku baftisma a cikin sunana.
ngakho kakho ongathi labhaphathizwa ngebizo lami.
16 (I, na kuma yi wa iyalin gidan Istifanas baftisma, ban da wannan, ban tuna da wani da na yi masa baftisma ba.)
(Yebo ngabhaphathiza abendlu KaStefane, ngaphandle kwalokho angikhumbuli ngibhaphathiza omunye.)
17 Gama Kiristi bai aike ni yin baftisma ba, sai dai wa’azin bishara ba da kalmomin hikimar mutum ba, domin kada gicciyen Kiristi ya rasa ikonsa.
Ngoba uKhristu kangithumanga ukuba ngibhaphathize kodwa ukuba ngitshumayele ivangeli, hatshi ngamazwi enhlakanipho yabantu, funa isiphambano silahlekelwe ngamandla aso.
18 Gama saƙon gicciye wauta ne ga waɗanda suke hallaka, amma a gare mu, mu da ake ceto, ikon Allah ne.
Ngoba ilizwi lesiphambano liyibuthutha kulabo ababhubhayo, kodwa kithi abasindisiweyo lingamandla kaNkulunkulu.
19 Gama a rubuce yake cewa, “Zan rushe hikimar mai hikima, basirar mai azanci kuma zan rikita shi.”
Ngoba kulotshiwe ukuthi: “Ngizachitha inhlakanipho yabahlakaniphileyo; ukwazi kwezazi ngizakunqunda.”
20 Ina mai hikima? Ina mai zurfin bincike? Ina masana na wannan zamani? Ashe, Allah bai wofinta hikimar duniya ba? (aiōn g165)
Ungaphi umuntu ohlakaniphileyo na? Singaphi isifundiswa somthetho na? Singaphi isazi salesisikhathi na? UNkulunkulu kenzanga ukuhlakanipha kwasemhlabeni kwaba yibuthutha na? (aiōn g165)
21 Gama tun da a cikin hikimar Allah, duniya a cikin hikimarta ba tă san shi ba, Allah ya ji daɗin ceton waɗanda suka ba da gaskiya ta wurin wautar wa’azin bishara.
Ngoba ekuhlakanipheni kukaNkulunkulu, umhlaba ngokuhlakanipha kwawo kawumazanga, uNkulunkulu wathokoza ngobuthutha balokho okwatshunyayelwayo ukuze kusindise abakholwayo
22 Yahudawa suna so su ga alama, Hellenawa kuma suna neman hikima,
AmaJuda afuna izibonakaliso lezimangaliso lamaGrikhi adinga ukuhlakanipha,
23 amma mu, muna wa’azin Kiristi wanda aka gicciye ne, wanda ya zama dutsen tuntuɓe ga Yahudawa, wauta kuma ga Al’ummai,
kodwa thina sitshumayela uKhristu owabethelwayo: isikhubekiso kumaJuda lobuthutha kwabeZizwe,
24 amma ga su waɗanda Allah ya kira, Yahudawa da Hellenawa, Kiristi ikon Allah ne, da kuma hikimar Allah.
kodwa kulabo ababizwe nguNkulunkulu, amaJuda lamaGrikhi, uKhristu ungamandla lokuhlakanipha kukaNkulunkulu.
25 Gama wautar Allah ta fi hikimar mutum, kuma rashin ƙarfin Allah ya fi ƙarfin mutum.
Ngoba ubuthutha bukaNkulunkulu buhlakaniphile kulokuhlakanipha komuntu, lobuthakathaka bukaNkulunkulu bulamandla kulamandla omuntu.
26 ’Yan’uwa, ku tuna yadda kuke sa’ad da aka kira ku. Babu masu hikima da yawa a cikinku, bisa ga ganin mutum; babu masu iko da yawa, babu masu martaba da yawa bisa ga haihuwa.
Bazalwane, khumbulani ngalokho elaliyikho ekubizweni kwenu. Kababanengi phakathi kwenu ababehlakaniphile ngesilinganiso sabantu; kababanengi ababelamandla; kababanengi ababezalwa yizikhulu.
27 Amma Allah ya zaɓi abubuwa masu wautata duniya, don yă kunyata masu hikima. Allah ya zaɓi abubuwa marasa ƙarfi na duniya, domin ya ba wa masu ƙarfi kunya.
Kodwa uNkulunkulu wakhetha izinto zasemhlabeni eziyizithutha ukuba ayangise izihlakaniphi; uNkulunkulu wakhetha izinto zasemhlabeni ezibuthakathaka ukuba ayangise abalamandla.
28 Ya zaɓi abubuwa marasa martaba na wannan duniya da kuma abubuwan da aka rena da abubuwan da ba a ɗauka a bakin kome ba, domin a wofinta abubuwan da ake ganinsu da daraja,
Wakhetha izinto zalo umhlaba eziphansi lezinto ezeyisekayo kanye lezinto ezingekho ukuba achithe okukhona,
29 domin kada wani ya yi taƙama a gabansa.
ukuze kungabi lamuntu ozazincoma phambi kwakhe.
30 Saboda Allah ne kuke cikin Kiristi Yesu, shi wanda ya zama hikima a gare mu daga Allah. Kiristi shi ne adalcinmu, da tsarkinmu, da kuma fansarmu.
Ngenxa yakhe lina likuKhristu uJesu, yena osebe yikuhlakanipha okuvela kuNkulunkulu esenzela thina, okuyikulunga kwethu, ubungcwele lokusindiswa.
31 Saboda haka, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Duk wanda yake taƙama, ya yi taƙama a cikin Ubangiji.”
Ngakho-ke, njengoba kulotshiwe ukuthi: “Lowo ozincomayo kazincome eNkosini.”

< 1 Korintiyawa 1 >