< 1 Korintiyawa 1 >
1 Bulus, wanda aka kira domin yă zama manzon Kiristi Yesu, bisa ga nufin Allah, da kuma ɗan’uwanmu Sostenes,
PAUL, called and sent by Jesus Messiah in the good pleasure of God; and Sosthenes, a brother;
2 Zuwa ga ikkilisiyar Allah da take a Korint, da waɗanda aka tsarkake cikin Kiristi Yesu, aka kuma kira domin su zama masu tsarki, tare da dukan waɗanda suke ko’ina da suke kiran sunan Ubangijinmu Yesu Kiristi, Ubangijinsu da kuma namu.
to the church of God which is at Corinth, to the people called and sanctified, who are sanctified in Jesus Messiah; and to all them, in every place, who invoke the name of our Lord Jesus Messiah, their and our Lord:
3 Alheri da salama daga Allah Ubanmu, da Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
Grace be with you, and peace; from God our Father, and from our Lord Jesus Messiah.
4 Ina gode wa Allah kullum dominku, saboda alherinsa da aka ba ku a cikin Kiristi Yesu.
I thank my God at all times on your behalf, for the grace of God which is given to you in Jesus Messiah;
5 Gama a cikinsa kuka sami wadata ta kowace hanya, a cikin dukan maganarku, da kuma cikin dukan saninku
that in every thing ye are enriched by him, in all discourse, and in all knowledge;
6 gama shaidarmu game da Kiristi ta tabbata a cikinku.
even as the testimony of Messiah was confirmed among you:
7 Saboda haka, ba ku rasa kowace baiwa ta ruhaniya ba, yayinda kuke jira da marmari, saboda bayyanuwar Ubangijinmu Yesu Kiristi.
so that ye are not inferior in any one of his gifts; but are waiting for the manifestation of our Lord Jesus Messiah:
8 Zai ƙarfafa ku har zuwa ƙarshe, domin ku zama marasa aibi a ranar Ubangijinmu Yesu Kiristi.
who will confirm you unto the end, so that ye may be blameless in the day of our Lord Jesus Messiah.
9 Allah, wanda ya kira ku zuwa ga zumunci tare da Ɗansa Yesu Kiristi Ubangijinmu, shi mai aminci ne.
God is faithful; by whom ye have been called into the fellowship of his Son, Jesus Messiah, our Lord.
10 Ina roƙonku’yan’uwa, a cikin sunan Ubangijinmu Yesu Kiristi, dukanku ku yarda da juna, domin kada a sami tsattsaguwa a cikinku, domin kuma ku zama ɗaya, cikakku a cikin halinku da tunaninku.
And I beseech you, my Brethren, by the name of our Lord Jesus Messiah, that to you all there may be one language; and that there may be no divisions among you: but that ye may become perfectly of one mind, and of one way of thinking.
11 ’Yan’uwana, waɗansu daga iyalin gidan Kulos sun gaya mini cewa, akwai faɗa a cikinku.
For concerning you, my Brethren, it hath been reported to me by the house of Chloe, that there are contentions among you.
12 Abin da nake nufi shi ne, ɗaya daga cikinku na cewa, “Ni ina bin Bulus,” wani na cewa, “Ni ina bin Afollos,” wani kuma, “Ni ina bin Kefas,” har wa yau wani kuma, “Ni ina bin Kiristi.”
And this I state: That one of you saith, I am of Paul; and another saith, I am of Apollos; and another saith, I am of Cephas; and another saith, I am of Messiah.
13 Kiristi a rabe ne? Bulus ne aka gicciye dominku? An yi muku baftisma a cikin sunan Bulus ne?
Now was Messiah divided? Or was Paul crucified for you? Or were ye baptized in the name of Paul?
14 Ina godiya domin ban yi wa wani baftisma a cikinku ba, sai dai Kirisbus da Gayus kaɗai.
I thank my God that I baptized none of you, except Crispus and Gaius;
15 Don haka, ba wanda na iya cewa an yi muku baftisma a cikin sunana.
lest any one should say, that I baptized in my own name.
16 (I, na kuma yi wa iyalin gidan Istifanas baftisma, ban da wannan, ban tuna da wani da na yi masa baftisma ba.)
I moreover baptized the household of Stephanas: but further, I know not that I baptized any other.
17 Gama Kiristi bai aike ni yin baftisma ba, sai dai wa’azin bishara ba da kalmomin hikimar mutum ba, domin kada gicciyen Kiristi ya rasa ikonsa.
For Messiah did not send me to baptize, but to preach; not with wisdom of words, lest the cross of Messiah should be inefficient.
18 Gama saƙon gicciye wauta ne ga waɗanda suke hallaka, amma a gare mu, mu da ake ceto, ikon Allah ne.
For a discourse concerning the cross is, to them who perish, foolishness; but to us who live, it is the energy of God.
19 Gama a rubuce yake cewa, “Zan rushe hikimar mai hikima, basirar mai azanci kuma zan rikita shi.”
For it is written: I will destroy the wisdom of the wise; and I will dissipate the intelligence of the sagacious.
20 Ina mai hikima? Ina mai zurfin bincike? Ina masana na wannan zamani? Ashe, Allah bai wofinta hikimar duniya ba? (aiōn )
Where is the wise? Or where is the scribe? Or where is the disputant of this world? Lo, hath not God showed, that the wisdom of this world is folly? (aiōn )
21 Gama tun da a cikin hikimar Allah, duniya a cikin hikimarta ba tă san shi ba, Allah ya ji daɗin ceton waɗanda suka ba da gaskiya ta wurin wautar wa’azin bishara.
For in the wisdom of God, because the world by wisdom knew not God, it pleased God, by the foolishness of preaching, to quicken them who believe.
22 Yahudawa suna so su ga alama, Hellenawa kuma suna neman hikima,
Because the Jews ask for signs, and the Gentiles demand wisdom.
23 amma mu, muna wa’azin Kiristi wanda aka gicciye ne, wanda ya zama dutsen tuntuɓe ga Yahudawa, wauta kuma ga Al’ummai,
But we preach Messiah as crucified; which is a stumbling-block to the Jews, and foolishness to the Gentiles;
24 amma ga su waɗanda Allah ya kira, Yahudawa da Hellenawa, Kiristi ikon Allah ne, da kuma hikimar Allah.
but to them who are called, both Jews and Gentiles, Messiah is the energy of God, and the wisdom of God.
25 Gama wautar Allah ta fi hikimar mutum, kuma rashin ƙarfin Allah ya fi ƙarfin mutum.
Because the foolishness of God, is wiser than men; and the feebleness of God, is stronger than men.
26 ’Yan’uwa, ku tuna yadda kuke sa’ad da aka kira ku. Babu masu hikima da yawa a cikinku, bisa ga ganin mutum; babu masu iko da yawa, babu masu martaba da yawa bisa ga haihuwa.
For look also at your calling, my Brethren; that not many among you are wise, according to the flesh; and not many among you are mighty, and not many among you are of high birth.
27 Amma Allah ya zaɓi abubuwa masu wautata duniya, don yă kunyata masu hikima. Allah ya zaɓi abubuwa marasa ƙarfi na duniya, domin ya ba wa masu ƙarfi kunya.
But God hath chosen the foolish ones of the world, to shame the wise; and he hath chosen the feeble ones of the world, to shame the mighty;
28 Ya zaɓi abubuwa marasa martaba na wannan duniya da kuma abubuwan da aka rena da abubuwan da ba a ɗauka a bakin kome ba, domin a wofinta abubuwan da ake ganinsu da daraja,
and he hath chosen those of humble birth in the world, and the despised, and them who are nothing, to bring to naught them who are something:
29 domin kada wani ya yi taƙama a gabansa.
so that no flesh might, glory before him.
30 Saboda Allah ne kuke cikin Kiristi Yesu, shi wanda ya zama hikima a gare mu daga Allah. Kiristi shi ne adalcinmu, da tsarkinmu, da kuma fansarmu.
And ye, moreover, are of him in Jesus Messiah; who hath become to us wisdom from God, and righteousness and sanctification, and redemption:
31 Saboda haka, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Duk wanda yake taƙama, ya yi taƙama a cikin Ubangiji.”
according to that which is written: He that glorieth, let him glory in the Lord.