< 1 Korintiyawa 1 >

1 Bulus, wanda aka kira domin yă zama manzon Kiristi Yesu, bisa ga nufin Allah, da kuma ɗan’uwanmu Sostenes,
Paul a called apostle of Christ Jesus through [the] will of God and Sosthenes the brother
2 Zuwa ga ikkilisiyar Allah da take a Korint, da waɗanda aka tsarkake cikin Kiristi Yesu, aka kuma kira domin su zama masu tsarki, tare da dukan waɗanda suke ko’ina da suke kiran sunan Ubangijinmu Yesu Kiristi, Ubangijinsu da kuma namu.
To the church of God which is being in Corinth, sanctified in Christ Jesus called holy, together with all those calling on the name of the Lord of us Jesus Christ in every place, both theirs (then *k*) and ours:
3 Alheri da salama daga Allah Ubanmu, da Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
Grace to you and peace from God Father of us and [the] Lord Jesus Christ.
4 Ina gode wa Allah kullum dominku, saboda alherinsa da aka ba ku a cikin Kiristi Yesu.
I thank the God of mine always concerning you for the grace of God which having been given you in Christ Jesus
5 Gama a cikinsa kuka sami wadata ta kowace hanya, a cikin dukan maganarku, da kuma cikin dukan saninku
for in everything you have been enriched in Him in all speech and in all knowledge,
6 gama shaidarmu game da Kiristi ta tabbata a cikinku.
even as the testimony about Christ was confirmed in you,
7 Saboda haka, ba ku rasa kowace baiwa ta ruhaniya ba, yayinda kuke jira da marmari, saboda bayyanuwar Ubangijinmu Yesu Kiristi.
so as for you not to be lacking in not one gift eagerly awaiting the revelation of the Lord of us Jesus Christ;
8 Zai ƙarfafa ku har zuwa ƙarshe, domin ku zama marasa aibi a ranar Ubangijinmu Yesu Kiristi.
who also will sustain you to [the] end blameless in the day of the Lord of us Jesus Christ.
9 Allah, wanda ya kira ku zuwa ga zumunci tare da Ɗansa Yesu Kiristi Ubangijinmu, shi mai aminci ne.
Faithful [is] God, through whom you were called into fellowship with the Son of Him Jesus Christ the Lord of us.
10 Ina roƙonku’yan’uwa, a cikin sunan Ubangijinmu Yesu Kiristi, dukanku ku yarda da juna, domin kada a sami tsattsaguwa a cikinku, domin kuma ku zama ɗaya, cikakku a cikin halinku da tunaninku.
I exhort now you, brothers, through the name of the Lord of us Jesus Christ that the same thing you may speak all and not there may be among you divisions, you may be however knit together in the same mind and in the same judgment.
11 ’Yan’uwana, waɗansu daga iyalin gidan Kulos sun gaya mini cewa, akwai faɗa a cikinku.
It was shown for to me concerning you, brothers of mine, by those of Chloe that quarrels among you there are.
12 Abin da nake nufi shi ne, ɗaya daga cikinku na cewa, “Ni ina bin Bulus,” wani na cewa, “Ni ina bin Afollos,” wani kuma, “Ni ina bin Kefas,” har wa yau wani kuma, “Ni ina bin Kiristi.”
I mean now this, that each of you says; I myself indeed am of Paul, I myself however of Apollos, I myself however of Cephas, I myself however of Christ.
13 Kiristi a rabe ne? Bulus ne aka gicciye dominku? An yi muku baftisma a cikin sunan Bulus ne?
Has been divided Christ? Surely not Paul was crucified for you? Or into the name of Paul were you baptized?
14 Ina godiya domin ban yi wa wani baftisma a cikinku ba, sai dai Kirisbus da Gayus kaɗai.
I thank God that no [one] of you I baptized only except Crispus and Gaius,
15 Don haka, ba wanda na iya cewa an yi muku baftisma a cikin sunana.
so that not anyone may say that into my name (you were baptized. *N(K)O*)
16 (I, na kuma yi wa iyalin gidan Istifanas baftisma, ban da wannan, ban tuna da wani da na yi masa baftisma ba.)
I baptized now also the of Stephanas household; as to the rest not I know whether any other I baptized.
17 Gama Kiristi bai aike ni yin baftisma ba, sai dai wa’azin bishara ba da kalmomin hikimar mutum ba, domin kada gicciyen Kiristi ya rasa ikonsa.
Not for sent me Christ to baptize but to evangelise; not in wisdom of discourse, that not may be emptied of power the cross of the Christ.
18 Gama saƙon gicciye wauta ne ga waɗanda suke hallaka, amma a gare mu, mu da ake ceto, ikon Allah ne.
The message for of the cross to those indeed perishing foolishness is, to those however being saved to us power of God it is.
19 Gama a rubuce yake cewa, “Zan rushe hikimar mai hikima, basirar mai azanci kuma zan rikita shi.”
It has been written for: I will destroy the wisdom of the wise, and the intelligence of the intelligent I will frustrate.
20 Ina mai hikima? Ina mai zurfin bincike? Ina masana na wannan zamani? Ashe, Allah bai wofinta hikimar duniya ba? (aiōn g165)
Where [is the] wise? Where [the] scribe? Where [the] debater of the age this? Surely has made foolish God the wisdom of the world (this? *k*) (aiōn g165)
21 Gama tun da a cikin hikimar Allah, duniya a cikin hikimarta ba tă san shi ba, Allah ya ji daɗin ceton waɗanda suka ba da gaskiya ta wurin wautar wa’azin bishara.
Since for in the wisdom of God not knew the world through the wisdom God, was pleased God through the foolishness of the proclamation to save those believing;
22 Yahudawa suna so su ga alama, Hellenawa kuma suna neman hikima,
Seeing that both Jews (signs *N(K)O*) ask for and Greeks wisdom seek,
23 amma mu, muna wa’azin Kiristi wanda aka gicciye ne, wanda ya zama dutsen tuntuɓe ga Yahudawa, wauta kuma ga Al’ummai,
we ourselves however preach Christ crucified, to [the] Jews indeed a stumbling block (to Gentiles *N(K)O*) however foolishness
24 amma ga su waɗanda Allah ya kira, Yahudawa da Hellenawa, Kiristi ikon Allah ne, da kuma hikimar Allah.
to them however to those called, Jews both and to Greeks, Christ of God [the] power and of God [the] wisdom.
25 Gama wautar Allah ta fi hikimar mutum, kuma rashin ƙarfin Allah ya fi ƙarfin mutum.
For the foolishness of God wiser than men is and the weakness of God stronger than men (is. *k*)
26 ’Yan’uwa, ku tuna yadda kuke sa’ad da aka kira ku. Babu masu hikima da yawa a cikinku, bisa ga ganin mutum; babu masu iko da yawa, babu masu martaba da yawa bisa ga haihuwa.
Consider for the calling of you, brothers, that not many wise according to flesh [were], not many powerful, not many of noble birth,
27 Amma Allah ya zaɓi abubuwa masu wautata duniya, don yă kunyata masu hikima. Allah ya zaɓi abubuwa marasa ƙarfi na duniya, domin ya ba wa masu ƙarfi kunya.
But the foolish things of the world has chosen God that He may shame the wise and the weak things of the world chose God that He may shame the strong,
28 Ya zaɓi abubuwa marasa martaba na wannan duniya da kuma abubuwan da aka rena da abubuwan da ba a ɗauka a bakin kome ba, domin a wofinta abubuwan da ake ganinsu da daraja,
and the low-born of the world and the [things] despised chose God, (and *ko*) the [things] not being, that the [things] being He may annul,
29 domin kada wani ya yi taƙama a gabansa.
so that not may boast all flesh before (God. *N(K)O*)
30 Saboda Allah ne kuke cikin Kiristi Yesu, shi wanda ya zama hikima a gare mu daga Allah. Kiristi shi ne adalcinmu, da tsarkinmu, da kuma fansarmu.
Out of Him however you yourselves are in Christ Jesus, who has been made wisdom unto us from God, righteousness and also sanctification and redemption,
31 Saboda haka, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Duk wanda yake taƙama, ya yi taƙama a cikin Ubangiji.”
in order that even as it has been written: The [one] boasting in [the] Lord he should boast.

< 1 Korintiyawa 1 >