< 1 Korintiyawa 8 >

1 To, game da abincin da aka miƙa hadaya ga gumaka kuwa. Mun san cewa dukanmu muna da ilimi. Ilimi yakan kawo girman kai, amma ƙauna takan gina.
Ahora, sobre las cosas que se ofrecen a las imágenes: todos parecemos tener conocimiento. El conocimiento da orgullo, pero el amor edifica.
2 Mutumin da yake tsammani ya san abu, sanin da yake da shi bai isa ba.
Si alguien parece tener conocimiento, hasta ahora no sabe nada, cómo debe saberlo;
3 Amma mutumin da yake ƙaunar Allah, Allah yana sane da shi.
Pero si alguien ama a Dios, Dios tiene conocimiento de él.
4 To, game da cin abincin da aka miƙa hadaya ga gumaka kuwa, mun san cewa “Gunki ba kome ba ne a duniya”, kuma “Babu wani Allah sai dai ɗaya.”
Entonces, en cuanto a la cuestión de tomar alimentos ofrecidos a las imágenes, estamos seguros de que una imagen no es nada en el mundo, y que no hay más Dios que uno.
5 Gama ko da akwai abubuwan da ake ce da su alloli, a sama ko a ƙasa (don kuwa akwai “alloli” da “iyayengiji” da yawa),
Porque aunque hay quienes tienen el nombre de dioses, en el cielo o en la tierra, como hay muchos dioses y muchos señores,
6 duk da haka a gare mu dai akwai Allah ɗaya kaɗai, Uba, wanda dukan abubuwa suke daga gare shi, wanda kuma saboda shi ne muke rayuwa, kuma akwai Ubangiji ɗaya, Yesu Kiristi, wanda ta wurinsa ne aka yi dukan abu, ta wurinsa ne kuma muke rayuwa.
hay para nosotros un solo Dios, el Padre, de los cuales son todas las cosas, y somos para él; y un Señor, Jesucristo, por quien son todas las cosas, y tenemos nuestro ser por medio de él.
7 Amma ba kowa ne ya san wannan ba. Har yanzu, waɗansu mutane sun saba da tunani cewa gumaka ainihi ne, saboda haka sa’ad da suka ci irin abincin nan, sukan ɗauka cewa kamar an miƙa wa ga gunki ne, kuma da yake lamirinsu ba ƙarfi, yakan ƙazantu.
Aún así, no todos los hombres tienen ese conocimiento: pero algunos, siendo acostumbrados hasta ahora a la imagen, son conscientes de que están tomando comida que se le ha ofrecido a la imagen; y su conciencia que es débil los hace sentirse contaminados por él ídolo.
8 Gaskiya ne cewa ba ma samun yardar Allah ta wurin abin da muke ci. Ba ma rasa wani abu idan ba mu ci ba, kuma ba ma ƙaru da wani abu in muka ci.
Pero la aprobación de Dios no se basa en la comida que tomamos: si no la tomamos, no estamos peor por eso; y si lo tomamos, no somos mejores. A Dios no los importa si comemos, o no comemos.
9 Sai dai ku yi hankali, kada yin amfani da’yancinku yă zama abin sa tuntuɓe ga marasa ƙarfi.
Pero ten cuidado de que este poder tuyo no cause problemas a los débiles.
10 Gama in wani wanda lamirinsa ba shi da ƙarfi ya gan ka, kai da kake da wannan sani, kana ci a haikalin gumaka, ashe, ba zai sami ƙarfin halin cin abin da aka miƙa wa gumaka ba?
Porque si un hombre te ve a ti, que tiene conocimiento, tomando comida como invitado en la casa de una imagen, ¿no le dará, si es débil, la idea de que pueda tomar comida ofrecida a las imágenes?
11 Saboda haka ta wurin sanin nan naka sai ka sa wannan ɗan’uwa marar ƙarfi wanda Kiristi ya mutu dominsa yă hallaka.
Y así, a través de tu conocimiento, eres la causa de la destrucción de tu hermano, por quien Cristo También murió.
12 Sa’ad da ka rushe lamiri mai bi marar ƙarfi, ka yi wa Kiristi zunubi ke nan.
Y de esta manera, haciendo mal a los hermanos, y causando problemas a aquellos cuya fe es débil, estás pecando contra Cristo.
13 Saboda haka, in abin da nake ci zai sa ɗan’uwana yă yi zunubi, ba zan ƙara cin nama ba, don kada in sa shi yă yi tuntuɓe. (aiōn g165)
Por esta razón, si la comida causa problemas a mi hermano, dejaré de tomar carne para siempre, para que no cause problemas a mi hermano. (aiōn g165)

< 1 Korintiyawa 8 >