< 1 Korintiyawa 8 >

1 To, game da abincin da aka miƙa hadaya ga gumaka kuwa. Mun san cewa dukanmu muna da ilimi. Ilimi yakan kawo girman kai, amma ƙauna takan gina.
Henu kuhusu fyakulya fafitolibhu sadaka kwa sanamu: Timanya ya kwamba “tete tabhoa tuyele ni maarifa.” Maarifa ghileta majifuno, bal upendo hujenga.
2 Mutumin da yake tsammani ya san abu, sanin da yake da shi bai isa ba.
Ikiwa munu yeywoha yhela idhani kwamba imanya jambo fulani, munu oyu okona amanyilepi kama ikampasa kumanya.
3 Amma mutumin da yake ƙaunar Allah, Allah yana sane da shi.
Lakini ikiwa mmonga kati ya bhang anganili K'yara, munu oyu ijulikana ni muene.
4 To, game da cin abincin da aka miƙa hadaya ga gumaka kuwa, mun san cewa “Gunki ba kome ba ne a duniya”, kuma “Babu wani Allah sai dai ɗaya.”
Basi kuhusu kulya fyakulya fafitolibhu sadaka kwa sanamu: Timanyili kuwa “sanamu si kenu mu dunia eye,” na yakuwa ayelepi K'yara ila mmonga tu.”
5 Gama ko da akwai abubuwan da ake ce da su alloli, a sama ko a ƙasa (don kuwa akwai “alloli” da “iyayengiji” da yawa),
Kwa maana bhayele bhingi bhabhikutibhwa miungu ikiwa ni kumbinguni au duniani kama khela bhakiyele “'miungu ni mabwana bhingi.”
6 duk da haka a gare mu dai akwai Allah ɗaya kaɗai, Uba, wanda dukan abubuwa suke daga gare shi, wanda kuma saboda shi ne muke rayuwa, kuma akwai Ubangiji ɗaya, Yesu Kiristi, wanda ta wurinsa ne aka yi dukan abu, ta wurinsa ne kuma muke rayuwa.
ijapokuwa kwatete kuyele K'yara mmonga tu ambayi ni Dadi, fhenu fhoa fihomili kwa muene, nitete twiishi kwa muene, ni Bwana mmonga Yesu Kristu, ambayi kwa muene fhenu fhoa fiyele, ni kwa muene tete tuyele.”
7 Amma ba kowa ne ya san wannan ba. Har yanzu, waɗansu mutane sun saba da tunani cewa gumaka ainihi ne, saboda haka sa’ad da suka ci irin abincin nan, sukan ɗauka cewa kamar an miƙa wa ga gunki ne, kuma da yake lamirinsu ba ƙarfi, yakan ƙazantu.
Hata naha, ujuzi obho uyelepi mugati mwa khila mmonga. Badala yiaki, bhangi bhashiriki ibada sa sanamu muandi, na hata henu bhilya fyakulya efe kana kwamba ni khenu kakitolibhu sadakakwa sanamu. Dhamiri sabhene sipotosibhu kwa ndabha ni dhaifu.
8 Gaskiya ne cewa ba ma samun yardar Allah ta wurin abin da muke ci. Ba ma rasa wani abu idan ba mu ci ba, kuma ba ma ƙaru da wani abu in muka ci.
Lakini kyakulya kilotahee kututhibitisha tete kwa K'yara. Tete tibhabayalepi sana kama tibelili kulya, wala wema sana ikiwa tilili.
9 Sai dai ku yi hankali, kada yin amfani da’yancinku yă zama abin sa tuntuɓe ga marasa ƙarfi.
Lakini muyelai makini ya kwamba uhuru wa muenga ukolokuya ndabha ya kumkwaza yayele dhaifu mu imani.
10 Gama in wani wanda lamirinsa ba shi da ƙarfi ya gan ka, kai da kake da wannan sani, kana ci a haikalin gumaka, ashe, ba zai sami ƙarfin halin cin abin da aka miƙa wa gumaka ba?
Hebu fikirilai kwamba munu oyu ithibitika lepi hata muene ni muene alyai fhenu fafilolibhu sadaka kwa sanamu?
11 Saboda haka ta wurin sanin nan naka sai ka sa wannan ɗan’uwa marar ƙarfi wanda Kiristi ya mutu dominsa yă hallaka.
Henu kwa ndabha ya ufahamu wa yobhi wa ukueli juu ya asili ya sanamu, mhaja ni ndhombhobhu yayele dhaifu, ambayi kambhele Kristu afwili kwa ajili ya muene, iangamizwa.
12 Sa’ad da ka rushe lamiri mai bi marar ƙarfi, ka yi wa Kiristi zunubi ke nan.
Hivyo, pawifuanya dhambi dhidi ya mhaja ni ndhombhobhu ni kuzijeruhi dhamiri sa bhene sasujele dhaifu, mwitenda dhambi dhidi ya Kistu.
13 Saboda haka, in abin da nake ci zai sa ɗan’uwana yă yi zunubi, ba zan ƙara cin nama ba, don kada in sa shi yă yi tuntuɓe. (aiōn g165)
Henu, ikiwa kyakulya kisababisya kunkwaza mhaja ni ndhombho nilyalepi nyama kamwe, ili mkolokunsababishila mhaja ni ndhombho bhangu kubina. (aiōn g165)

< 1 Korintiyawa 8 >