< 1 Korintiyawa 8 >
1 To, game da abincin da aka miƙa hadaya ga gumaka kuwa. Mun san cewa dukanmu muna da ilimi. Ilimi yakan kawo girman kai, amma ƙauna takan gina.
MA na mea i kaumahaia na na kii, ua ike no kakou, ua naauao no kakou a pau. He mea hookiekie ka naauao: o ke aloha nae ka mea e nui ai ka ikaika.
2 Mutumin da yake tsammani ya san abu, sanin da yake da shi bai isa ba.
Ina i manao kekahi, ua akamai ia, aole ia e akamai iki e like me ke akamai e pono ai oia.
3 Amma mutumin da yake ƙaunar Allah, Allah yana sane da shi.
Aka, ina i aloha aku kekahi i ke Akua, ua ikea mai oia e ia.
4 To, game da cin abincin da aka miƙa hadaya ga gumaka kuwa, mun san cewa “Gunki ba kome ba ne a duniya”, kuma “Babu wani Allah sai dai ɗaya.”
Ma ka ai ana i na mea i kaumahaia na na kii, ua ike no kakou, he mea ole ke kii, ma ka honua nei, aole hoi he Akua e ae, hookahi wale no.
5 Gama ko da akwai abubuwan da ake ce da su alloli, a sama ko a ƙasa (don kuwa akwai “alloli” da “iyayengiji” da yawa),
He mea no nae i kapaia, he Akua, ma ka lani paha, ma ka hopua paha, no ka mea, ua nui na'kua, a ua nui na haku:
6 duk da haka a gare mu dai akwai Allah ɗaya kaɗai, Uba, wanda dukan abubuwa suke daga gare shi, wanda kuma saboda shi ne muke rayuwa, kuma akwai Ubangiji ɗaya, Yesu Kiristi, wanda ta wurinsa ne aka yi dukan abu, ta wurinsa ne kuma muke rayuwa.
Aka, ia kakou, hookahi no Akua, o ka Makua, a nana mai na mea a pau, a ia ia hoi kakou nei: hookaihi no Haku, o Iesu Kristo, ma ona la na mea a pau, a ma ona la hoi kakou.
7 Amma ba kowa ne ya san wannan ba. Har yanzu, waɗansu mutane sun saba da tunani cewa gumaka ainihi ne, saboda haka sa’ad da suka ci irin abincin nan, sukan ɗauka cewa kamar an miƙa wa ga gunki ne, kuma da yake lamirinsu ba ƙarfi, yakan ƙazantu.
Aka, aole i na kanaka a pau keia ike; no ka mea, i keia wa no, me ka manao i na kii, ai no kekahi poe me he mea la i mohaiia na ke kii; a no ka nawaliwali o ko lakou naau, ua haumia.
8 Gaskiya ne cewa ba ma samun yardar Allah ta wurin abin da muke ci. Ba ma rasa wani abu idan ba mu ci ba, kuma ba ma ƙaru da wani abu in muka ci.
Aole hoi kakou e aponoia e ke Akua no ka ai; no ka mea, ina e ai kakou, aole e oi ko kakou maikai ilaila; a i ai ole kakou, aole e oi ko kakou ino ilaila.
9 Sai dai ku yi hankali, kada yin amfani da’yancinku yă zama abin sa tuntuɓe ga marasa ƙarfi.
E malama hoi oukou, o lilo auanei keia pono o oukou, i mea e hihia ai, no ka poe hawawa.
10 Gama in wani wanda lamirinsa ba shi da ƙarfi ya gan ka, kai da kake da wannan sani, kana ci a haikalin gumaka, ashe, ba zai sami ƙarfin halin cin abin da aka miƙa wa gumaka ba?
Ina i ike mai kekahi ia oe, i ka mea naauao, e noho ana e ai iloko o ka heiau o ke kii, aole anei e eueu ka manao o ke kanaka hawawa, e ai i na mea i mohaiia na na kii?
11 Saboda haka ta wurin sanin nan naka sai ka sa wannan ɗan’uwa marar ƙarfi wanda Kiristi ya mutu dominsa yă hallaka.
Alaila, no kou naauao ana, e make no ka hoahanau hawawa, nona i make ai o Kristo.
12 Sa’ad da ka rushe lamiri mai bi marar ƙarfi, ka yi wa Kiristi zunubi ke nan.
A i ka oukou hana hewa ana pela i na hoahanau, a i ko oukou hoeha ana i ko lakou naau nawaliwali, ua hana hewa oukou ia Kristo.
13 Saboda haka, in abin da nake ci zai sa ɗan’uwana yă yi zunubi, ba zan ƙara cin nama ba, don kada in sa shi yă yi tuntuɓe. (aiōn )
No ia mea, ina o ka io ka mea e hewa ai ko'u hoahanau, ma keia hope aku, aole loa au e ai hou i ka io, o hoolilo au i ko'u hoahanau i ka hewa. (aiōn )