< 1 Korintiyawa 6 >
1 In wani a cikinku yana da damuwa da wani, don me zai kai ƙara a gaban marasa bi, maimakon yă kai ƙara a gaban tsarkaka?
Doth any one of you, who hath a matter against another, dare to go to law before the unrighteous, and not before the holy?
2 Ba ku san cewa tsarkaka ne za su yi wa duniya shari’a ba? In kuwa za ku yi wa duniya shari’a, ai, kun isa ku yi shari’a a kan ƙananan damuwoyi ke nan.
Or do ye not know, that the holy will judge the world? And if the world is to be judged by you, are ye unworthy to judge in causes of the least importance?
3 Ba ku san cewa za mu yi wa mala’iku shari’a ba? Balle al’amuran da suka shafi duniyan nan!
Know ye not, that we shall pass judgment upon angels? How much more, concerning affairs of this life?
4 Saboda haka, in kuna da damuwa game da irin waɗannan al’amura, sai ku naɗa alƙalai ko cikin waɗanda ba kome ba ne a ikkilisiya!
If then ye have any causes relating to this life, set them to judge who are of no repute in the church.
5 Na faɗi haka ne don ku ji kunya. Ashe, ba za a iya samun wani a cikinku mai hikima wanda zai iya sasanta tsakanin masu bi ba?
I speak to your shame. Is it so, that there is not a wise man among you, not one that will be able to judge between his brethren?
6 Me zai sa ɗan’uwa yă kai ƙarar ɗan’uwa, a gaban marasa bi?
Nay, brother goeth to law with brother, and that before unbelievers.
7 Ƙarar junanku ma da kuke yi, ai, kāsawa ce a gare ku. Ba gara ku haƙura a cuce ku ba? Ku kuma haƙura ko an zambace ku?
Now therefore it is altogether an evil among you, that ye have suits against each other. Why do ye not rather submit to wrong? Why do ye not rather allow yourselves to be defrauded?
8 Amma ga shi ku da kanku kuna cuta, kuna kuma zamba, har ma ga’yan’uwanku ne kuke yi wannan.
But ye yourselves wrong, and defraud, and that too your brethren.
9 Ba ku sani ba cewa mugaye ba za su gāji mulkin Allah ba? Kada fa a ruɗe ku. Ba masu fasikanci ko masu bautar gumaka ko masu zina ko karuwan maza, ko’yan daudu,
Know ye not, that wrongdoers shall not inherit the kingdom of God? Be not deceived; neither fornicators, nor idolaters, nor adulterers, nor the effeminate, nor abusers of themselves with mankind,
10 ko ɓarayi ko masu kwaɗayi ko mashaya ko masu ɓata suna ko masu zamba da za su gāji mulkin Allah.
nor thieves, nor the covetous, nor drunkards, nor revilers, nor extortioners, shall inherit the kingdom of God.
11 Haka waɗansu a cikinku ma suke a dā. Amma an wanke ku, an tsarkake ku, aka kuma sa kuka zama marasa laifi cikin sunan Ubangijinmu Yesu Kiristi da kuma ta wurin Ruhun Allahnmu.
And such were some of you; but ye were washed, but ye were made holy, but ye were accepted as righteous in the name of the Lord Jesus, and in the Spirit of our God.
12 “Ina da dama in yi kome,” sai dai ba kome ba ne yake da amfani. “Ina da dama in yi kome” sai dai ba abin da zai mallake ni.
All things are lawful for me, but all things are not profitable; all things are lawful for me, but I will not be brought under the power of anything.
13 “An yi abinci domin ciki ne, ciki kuma domin abinci.” Amma Allah zai hallaka su duka. Ba a yi jiki saboda fasikanci ba, sai dai domin Ubangiji, Ubangiji kuma domin jiki.
Meats are for the stomach, and the stomach for meats; but God will make an end of both it and them. But the body is not for fornication, but for the Lord, and the Lord for the body;
14 Ta wurin ikonsa, Allah ya tashe Ubangiji daga matattu, haka zai tashe mu mu ma.
and God both raised up the Lord, and will also raise up us by his power.
15 Ba ku sani ba cewa jikunanku gaɓoɓin Kiristi ne kansa? Zai kyautu in ɗauki gaɓoɓin Kiristi in haɗa da jikin karuwa? Sam!
Know ye not, that your bodies are members of Christ? Shall I then take the members of Christ, and make them members of a harlot? God forbid!
16 Ba ku san cewa shi wanda ya haɗa jikinsa da karuwa sun zama ɗaya a cikin jiki ke nan ba? Gama an ce, “Biyun za su zama jiki ɗaya.”
Know ye not, that he who is connected with a harlot is one body with her? “For the two,” saith he, “shall become one flesh;”
17 Wanda kuwa ya haɗa jikinsa da Ubangiji ya zama ɗaya da shi ke nan a ruhu.
but he that is connected with the Lord is one spirit with him.
18 Ku guji fasikanci. Duk sauran zunubai da mutum yakan aikata suna waje da jikinsa, amma mai yin fasikanci, yana ɗaukar alhalin jikinsa ne.
Flee fornication. Every other sin which a man may commit, is apart from the body; but he that committeth fornication, sinneth against his own body.
19 Ba ku san cewa jikin nan naku haikalin Ruhu Mai Tsarki ba ne wanda yake cikinku yake kuma daga Allah? Ku ba na kanku ba ne;
Know ye not, that your bodies are temples of the Holy Spirit which is in you, which ye have from God, and that ye are not your own?
20 saye ku fa aka yi da tsada, saboda haka, sai ku girmama Allah da jikinku.
For ye were bought with a price. Therefore glorify God in your body.