< 1 Korintiyawa 5 >

1 Ana ba da labari cewa ana lalata a cikinku, irin da ba a ma samu a cikin masu bautar gumaka. Har mutum yana kwana da matar mahaifinsa.
Ami huni bole pai ase ta te kunba khan ase jun khan bebichar laga kaam apnikhan majote kori ase, aru eneka biya kaam khan juntu Porjati khan majote kitia bhi huna nai- jineka ekjon manu tai laga baba laga maiki ke loi kene ase.
2 Har ya zama muku abin taƙama! Ashe, bai kamata ku cika da baƙin ciki ku kuma daina zumunci da mutumin da yake aikata wannan ba?
Aru eneka hoi kene bhi apnikhan iman phutani ase! Asol to apnikhan mon dukh hobole lage, eneka hoile jun manu eneka kaam kori ase taikhan ke apnikhan logot pora ulai dibi.
3 Ko da yake ba na nan tare da ku cikin jiki, ina tare da ku a cikin ruhu. Na riga na yanke wa wanda ya aikata wannan hukunci, kamar dai ina tare da ku.
Ami apnikhan majote gaw pora alag thakile bhi, ami laga atma to apnikhan logote ase. Moi poila pora utu manu laga kaam khan nimite bisar kori dise, ami nijor ta te thaka nisena.
4 Saboda haka sa’ad da kun taru ikon Ubangijinmu Yesu kuma yana nan, ni ma ina tare da ku.
Jitia apnikhan Probhu Jisu Khrista laga naam pora joma hoise, aru ami atma pora apnikhan logote ase, amikhan laga Probhu Jisu Khrista laga hokti pora,
5 Ku miƙa irin wannan mutum ga Shaiɗan, don a hallaka halin nan na mutuntaka, ruhunsa kuma yă sami ceto a ranar da Ubangiji zai dawo.
etu manu ke Saitan laga hathte tai laga gaw ke khotom kori dibo nimite dibi, eneka hoile Probhu laga dinte tai laga atma to bachai lobo.
6 Ku daina taƙama. Ba ku san cewa ɗan ƙanƙanin yisti ne yakan sa dukan curin burodi yă kumbura ba?
Apnikhan phutani dikhai thaka to bhal nohoi. Apnikhan najane naki, ekta chutu khomir to pura atta ke phulai diye?
7 Ku kawar da tsohon yisti don ku zama kamar sabon curi da aka yi babu yisti yadda dai kuke. Gama an miƙa Kiristi Ɗan Ragon Bikin Ƙetarewarmu.
Purana khomir ke ulai dibi eneka hoile apnikhan ekta notun roti bona bole laga atta hoi jabo. Kilekoile Khrista, amikhan laga Nistar laga mer bacha to bolidan hoi jaise.
8 Saboda haka, sai mu kiyaye Bikin ba da burodi mai tsohon yisti ba, ba kuma da yisti na ƙeta da mugunta ba, sai dai da burodi marar yisti na sahihanci da na gaskiya.
Etu nimite ahibi amikhan khushi laga din ke manabo, purana khomir logote nohoi, nohoile bhi biya adat aru biya kaam laga khomir pora nohoi, kintu hosa aru ekta naphula laga roti nisena sapha hoi kene.
9 Na rubuta muku cikin wasiƙata, kada ku yi haɗa kai da masu aikin lalata.
Ami poila laga chithi te bhi likhise, bebichar kora manu khan logote namilibi.
10 Ko kusa, ba na nufin fasikai marasa bi, ko makwaɗaita da mazambata, ko matsafa, don in haka ne, sai yă zama dole ku fita daga duniya.
Ami laga chithi te, etu prithibi laga bebichar kaam kora khan, nohoile lalchi thaka, nohoile thogai diya manu, nohoile murti puja kora khan logote namili kene thakibi kowa nohoi, eneka hoile apnikhan etu prithibi pora bahar te jabole lagibo.
11 Yanzu dai ina rubuta muku cewa kada ku haɗa kai da duk mai kiran kansa ɗan’uwa, amma yana fasikanci, ko kwaɗayi, ko bautar gumaka, ko ɓata suna, ko mashayi, ko mazambaci. Kada ku ko ci abinci da irin wannan mutum.
Kintu etiya ami apnikhan ke likha to utu manu khan logote namilibi jun tai nijorke ekjon bhai nisena koi kintu jun bebichar ase, nohoile lalchi ase, nohoile murti puja kora, nohoile kotha pora biya gali kora, nohoile nisa pani kore, nohoile manu ke thogai diye. Eneka manu logote kha luwa bhi na koribi.
12 Me zai kai yin hukunci ga waɗanda ba’yan ikkilisiya ba. Ai, waɗanda suke’yan ikkilisiya ne za ku hukunta.
Ki kori bole ami abiswasi khan ke bisar koribo? Bhitor te thaka khan ke bisar koribo lage nohoi?
13 Allah zai hukunta waɗanda ba namu ba. “Ku yi waje da irin mugun mutumin nan daga cikinku.”
Kintu Isor to abiswasi khan ke bisar kore. “Etu biya manu ke apnikhan laga majot pora ulai dibi.”

< 1 Korintiyawa 5 >