< 1 Korintiyawa 4 >
1 Saboda haka, ya kamata mutane su ɗauke mu a matsayin bayin Kiristi, da kuma a matsayin waɗanda aka ba su amanar asirin abubuwan Allah.
Let a man, so, be reckoning of us, as officers of Christ, and stewards of sacred secrets of God.
2 Yanzu fa, ana bukatar waɗanda aka ba su riƙon amana, dole su zama masu aminci.
Here, furthermore, it is sought in stewards, that, faithful, one be found.
3 Ƙaramin abu ne a gare ni a ce ku ne za ku gwada ni, ko kuwa a gwada ni a wata kotun mutane, ai, ko ni kaina ba na yanka wa kaina hukunci.
With me, however, it counteth for the very smallest thing, that, by you, I should be examined, or by a human day. Nay! I am not even examining myself,
4 Lamirina bai ba ni laifi ba, sai dai wannan bai mai da ni marar laifi ba. Ubangiji ne mai hukunta ni.
For, of nothing, to myself, am I conscious: nevertheless, not hereby, am I declared righteous, but, he that doth examine me, is the Lord.
5 Saboda haka, kada ku shari’anta kome tun lokaci bai yi ba. Ku jira sai Ubangiji ya zo. Zai bayyana abin da yake a ɓoye a cikin duhu a sarari, zai kuma tone nufin zukatan mutane. A lokacin ne fa kowa zai karɓi yabo daga wurin Allah daidai gwargwado.
So then, not before the fitting time, be judging anything, —until the Lord shall come, who will both bring to light the hidden things of darkness, and make manifest the counsels of the hearts; and, then, the praise shall come to each one, from God.
6 To, fa’yan’uwa, ga zancen waɗannan abubuwa, na misalta su ne ga kaina, da kuma Afollos saboda ku, don ku yi koyi da mu a kan abin da ake nufi da cewa, “Kada ku zarce abin da yake a rubuce.” Ta haka, ba za ku yi taƙama da wani mutum fiye da wani ba.
But, these things, brethren, have I transferred unto myself and Apollos, for your sakes, that, in us, ye might learn [the lesson] —Not beyond the things that are written…! that ye do not puff yourselves up, individually, for this one against that.
7 Wa ya ce ka fi sauran mutane? Me kuma kake da shi, wanda ba karɓa ka yi ba? In kuma karɓa ka yi, me ya sa kake taƙama kamar ba karɓa ba ne ka yi?
For who maketh thee to differ? and what hast thou which thou didst not receive? But, if thou didst even receive it, why dost thou boast, as though thou hadst not received it?
8 Kun riga kun sami duk abin da kuke nema! Kun riga kun yi arziki! Kun zama sarakuna, kun kuma zama haka ɗin ba tare da mu ba! Da a ce kun riga kun zama sarakuna mana da sai mu zama sarakuna tare da ku!
Already, ye have become full, already, ye are become rich, —apart from us, ye are become kings! And I would indeed ye had become kings, that, we also, with you, might have together become kings!
9 Gama a ganina fa, Allah ya baje mu manzanni a ƙarshen jerin gwanon, a matsayin mutanen da aka hukunta ga mutuwa a filin wasanni. Mun zama abin kallo ga dukan duniya, ga mala’iku da kuma mutane.
For I think that, God, hath set forth, us the apostles, to be last of all, as men devoted to death, —in that, a spectacle, have we been made, unto the world, —both unto messengers and unto men.
10 Mun zama masu wauta saboda Kiristi, ku kuwa kuna da hikima sosai a cikin Kiristi! Ba mu da ƙarfi, amma ku kuna da ƙarfi! Ana girmama ku, mu kuwa ana ƙasƙantar da mu!
We, are foolish for Christ’s sake, but, ye, prudent in Christ; we are weak, but, ye, mighty; ye, all-glorious, but, we, dishonoured.
11 Har yă zuwa wannan sa’a, yunwa da ƙishirwa muke ciki, muna sanye da tsummoki, ana wulaƙanta mu, ba mu kuma da gida.
Until the present hour, we both hunger and thirst, and are naked, and are buffeted, and are wanderers,
12 Muna aiki da gaske da hannuwanmu. In aka la’anta mu, mukan sa albarka. In aka tsananta mana, mukan jimre;
And toil, working with our own hands: being reviled, we bless, being persecuted, we hold on,
13 in aka ɓata mana suna, mukan mayar da alheri. Har yă zuwa wannan lokaci, mu ne kamar jujin duniya, abin ƙyamar kowa.
Being defamed, we beseech: as the sweepings of the world have we become, the offscouring of all—until even now.
14 Ba don in kunyata ku ba ne na rubuta wannan, sai dai don in gargaɗe ku a kan cewa ku’ya’yana ne, ƙaunatattu.
Not, to shame you, write I these things; but, as my beloved children, I admonish you.
15 Ko da kuna da iyayen riƙo dubu goma cikin Kiristi, ba ku da ubanni da yawa, gama a cikin Kiristi Yesu, na zama mahaifi a gare ku, ta wurin bishara.
For, though myriads of tutors ye should have in Christ, yet not many fathers; for, in Christ Jesus, through means of the joyful message, I, begat you.
16 Saboda haka, ina roƙonku ku yi koyi da ni.
I beseech you, therefore, —become imitators of me.
17 Saboda wannan dalili ina aika muku Timoti, ɗana, wanda nake ƙauna, mai aminci kuma a cikin Ubangiji. Zai tunashe ku game da yadda za ku bi Kiristi Yesu da kuma yadda ya yi daidai da yadda nake koyarwa a ko’ina, a kowace ikkilisiya.
For this cause, sent I unto you, Timothy, —who is my beloved and faithful child in the Lord, who shall put, you, in mind of my ways which are in Christ [Jesus], even as, everywhere, in every assembly, I teach.
18 Waɗansunku suna tsammani ba zan zo wurinku ba har suna ɗagankai.
But, as though I were not coming unto you, some are puffed up!
19 Amma in Ubangiji ya yarda zan zo wurinku ba da daɗewa ba. Sa’an nan zan bincike ko masu wannan yawan ɗagan kan nan suna da wani iko.
Howbeit, I will come quickly unto you, —if, the Lord, please, —and will get to know—not the speech of them who are puffed up, but, the power;
20 Gama mulkin Allah ba cika baki ba ne, sai dai ga iko.
For, not in speech, is the kingdom of God, but, in power.
21 Wanne kuka fi so in na zo? Kuna so in tsananta muku ko in zama mai hankali da kuma sauƙinkai?
What will ye? that, with a rod, I should come unto you? or, with love, and a spirit of meekness?