< 1 Korintiyawa 3 >
1 ’Yan’uwa, ban iya yi muku magana kamar masu ruhaniya ba, sai dai kamar masu halin mutuntaka, jarirai cikin bin Kiristi kawai.
Hermanos, no pude hablarles como a espirituales, sino como a humanos, como a niños en Cristo.
2 Na ba ku madara ba abinci mai tauri ba, domin ba ku balaga ba a lokacin. Kai, har yanzu ma, ba ku balaga ba.
Les di a beber leche, no alimento sólido, porque todavía no podían recibirlo. Y todavía no pueden
3 Har yanzu kuna rayuwa bisa ga halin mutuntaka. Da yake akwai kishi da faɗace-faɗace a cikinku, ba rayuwa irin ta halin mutuntaka ke nan kuke yi ba? Kuma ba rayuwa irin ta mutane ce kawai kuke yi ba?
pues aún están dominados por la naturaleza humana. Mientras haya entre ustedes envidia y contienda, ¿no están dominados por la naturaleza humana y viven como hombres?
4 Gama sa’ad da wani ya ce, “Ni na Bulus ne,” wani kuma ya ce, “Ni na Afollos ne,” ba rayuwa irin ta mutane ke nan kuke yi ba?
Cuando alguno dice: Yo ciertamente soy de Pablo, y otro dice: Yo de Apolos, ¿no están dominados por la naturaleza humana?
5 Shin, wane ne Afollos? Wane ne kuma Bulus? Ai, bayi ne kawai waɗanda ta wurinsu kuka gaskata, kamar yadda Ubangiji ya ba kowannensu aikinsa.
¿Quién es Apolos? ¿Y quién es Pablo? Somos servidores por medio de quienes creyeron, según el trabajo que el Señor asignó a cada uno.
6 Ni na shuka iri, Afollos kuma ya yi banruwa, amma Allah ne ya sa irin ya yi girma.
Yo planté, Apolos regó, pero Dios produjo el crecimiento.
7 Don haka, da wanda ya yi shuki, da wanda ya yi banruwa, ba a bakin kome suke ba, sai dai Allah kaɗai, mai sa abubuwa su yi girma.
Así que, ni el que planta ni el que riega es algo, sino Dios, Quien produce el crecimiento.
8 Mutumin da ya yi shuki, da mutumin da ya yi banruwa nufinsu ɗaya ne, kuma kowannensu zai sami lada gwargwadon aikinsa.
El que planta y el que riega son iguales, aunque cada uno recibirá su salario según su labor.
9 Gama mu abokan aiki ne na Allah; ku kuwa gonar ce ta Allah, ginin Allah kuma.
Porque somos colaboradores de Dios. [Ustedes] son un campo cultivado por Dios, un edificio suyo.
10 Ta wurin alherin da Allah ya ba ni, na kafa tushen gini kamar ƙwararren magini, wani kuma dabam yana gini a kai. Amma kowa yă lura da yadda yake gini.
Según la gracia que Dios me dio, puse un fundamento como arquitecto experimentado y otro construye sobre él. Pero cada uno tenga cuidado cómo construye.
11 Gama babu wanda zai iya kafa wani tushen gini dabam da wanda aka riga aka kafa, wanda yake Yesu Kiristi.
Porque nadie puede poner otro fundamento distinto del que está puesto, el cual es Jesucristo.
12 In wani ya yi gini a kan tushen ginin nan da zinariya, azurfa, duwatsu masu daraja, itace, ciyawa ko kara,
Si alguno edifica oro, plata, piedras preciosas, madera, pasto, hojarasca sobre el fundamento,
13 aikin zai bayyana kansa, domin za a nuna shi a sarari a Ranar. Wuta ce za tă bayyana aikin, wutar kuwa za tă gwada ingancin aikin kowa.
la obra de cada uno será visible. Porque el día la mostrará, pues con fuego será descubierta. El fuego probará la obra de cada uno.
14 In abin da kowane mutum ya gina ya tsaya, zai sami lada.
Si permanece la obra que alguno construyó, recibirá recompensa.
15 In ya ƙone, zai yi hasara, amma zai sami ceto, sai dai kamar wanda ya bi ta tsakiyar wuta ne.
Si la obra de alguno se quema, se perderá, pero él será salvo, como el que pasa por fuego.
16 Ashe, ba ku sani ba cewa ku kanku haikalin Allah ne, Ruhun Allah kuma yana zaune a cikinku?
¿No saben que ustedes son Santuario de Dios, y que el Espíritu de Dios mora en ustedes?
17 Duk wanda ya ɓata haikalin Allah, Allah zai ɓata shi, don haikalin Allah mai tsarki ne, ku ne kuwa haikalin nan.
Si alguno destruye el Santuario de Dios, Dios lo destruirá, porque el Santuario de Dios es santo. Ustedes son ese Santuario.
18 Kada ku ruɗi kanku. In waninku yana tsammani cewa yana da hikima, yadda duniya ta ɗauki hikima, to, sai ya mai da kansa “wawa” don yă zama mai hikima. (aiōn )
Nadie se engañe. Si alguno de ustedes supone que es sabio en este mundo, vuélvase necio para que sea sabio. (aiōn )
19 Gama hikimar duniyan nan, wauta ce a gaban Allah, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Yakan kama masu hikima a cikin makircinsu”;
Porque la sabiduría de este mundo es necedad ante Dios, pues está escrito: Él atrapa a los sabios en su astucia.
20 kuma a rubuce yake cewa, “Ubangiji ya san dukan tunanin masu hikima banza ne.”
Y otra vez: [El] Señor conoce los pensamientos vanos de los sabios.
21 Saboda haka, kada wani yă yi taƙama da mutum! Gama kome naku ne,
Así que, nadie se enaltezca por lo que es propio de los seres humanos. Porque todo es de ustedes,
22 ko Bulus ko Afollos ko Kefas ko duniya ko rai ko mutuwa ko abubuwa na yanzu ko na nan gaba, ai, duka naku ne,
sea Pablo, Apolos, Cefas, [el] mundo, [la] vida, [la] muerte, cosas que vinieron o que vienen, todo es de ustedes,
23 ku kuwa na Kiristi ne, Kiristi kuma na Allah ne.
y ustedes de Cristo y Cristo de Dios.