< 1 Korintiyawa 3 >

1 ’Yan’uwa, ban iya yi muku magana kamar masu ruhaniya ba, sai dai kamar masu halin mutuntaka, jarirai cikin bin Kiristi kawai.
Et pour moi, mes frères, je n'ai pu vous parler comme à des [hommes] spirituels, mais comme à des [hommes] charnels, [c'est-à-dire], comme à des enfants en Christ.
2 Na ba ku madara ba abinci mai tauri ba, domin ba ku balaga ba a lokacin. Kai, har yanzu ma, ba ku balaga ba.
Je vous ai donné du lait à boire, et non pas de la viande, parce que vous ne la pouviez pas encore [porter]; même maintenant vous ne le pouvez pas encore; parce que vous êtes encore charnels.
3 Har yanzu kuna rayuwa bisa ga halin mutuntaka. Da yake akwai kishi da faɗace-faɗace a cikinku, ba rayuwa irin ta halin mutuntaka ke nan kuke yi ba? Kuma ba rayuwa irin ta mutane ce kawai kuke yi ba?
Car puisqu'il y a parmi vous de l'envie, et des dissensions, et des divisions, n'êtes-vous pas charnels, et ne vous conduisez-vous pas à la manière des hommes?
4 Gama sa’ad da wani ya ce, “Ni na Bulus ne,” wani kuma ya ce, “Ni na Afollos ne,” ba rayuwa irin ta mutane ke nan kuke yi ba?
Car quand l'un dit: pour moi, je suis de Paul; et l'autre: pour moi, je suis d'Apollos; n'êtes-vous pas charnels?
5 Shin, wane ne Afollos? Wane ne kuma Bulus? Ai, bayi ne kawai waɗanda ta wurinsu kuka gaskata, kamar yadda Ubangiji ya ba kowannensu aikinsa.
Qui est donc Paul, et qui est Apollos, sinon des Ministres, par lesquels vous avez cru, selon que le Seigneur a donné à chacun?
6 Ni na shuka iri, Afollos kuma ya yi banruwa, amma Allah ne ya sa irin ya yi girma.
J'ai planté; Apollos a arrosé; mais c'est Dieu qui a donné l'accroissement.
7 Don haka, da wanda ya yi shuki, da wanda ya yi banruwa, ba a bakin kome suke ba, sai dai Allah kaɗai, mai sa abubuwa su yi girma.
Or ni celui qui plante, ni celui qui arrose, ne sont rien; mais Dieu, qui donne l'accroissement.
8 Mutumin da ya yi shuki, da mutumin da ya yi banruwa nufinsu ɗaya ne, kuma kowannensu zai sami lada gwargwadon aikinsa.
Et tant celui qui plante, que celui qui arrose, ne sont qu'une même chose; mais chacun recevra sa récompense selon son travail.
9 Gama mu abokan aiki ne na Allah; ku kuwa gonar ce ta Allah, ginin Allah kuma.
Car nous sommes ouvriers avec Dieu; [et] vous êtes le labourage de Dieu, [et] l'édifice de Dieu.
10 Ta wurin alherin da Allah ya ba ni, na kafa tushen gini kamar ƙwararren magini, wani kuma dabam yana gini a kai. Amma kowa yă lura da yadda yake gini.
Selon la grâce de Dieu qui m'a été donnée, j'ai posé le fondement comme un sage architecte, et un autre édifie dessus; mais que chacun examine comment il édifie dessus.
11 Gama babu wanda zai iya kafa wani tushen gini dabam da wanda aka riga aka kafa, wanda yake Yesu Kiristi.
Car personne ne peut poser d'autre fondement que celui qui est posé, lequel est Jésus-Christ.
12 In wani ya yi gini a kan tushen ginin nan da zinariya, azurfa, duwatsu masu daraja, itace, ciyawa ko kara,
Que si quelqu'un édifie sur ce fondement, de l'or, de l'argent, des pierres précieuses, du bois, du foin, du chaume;
13 aikin zai bayyana kansa, domin za a nuna shi a sarari a Ranar. Wuta ce za tă bayyana aikin, wutar kuwa za tă gwada ingancin aikin kowa.
L'œuvre de chacun sera manifestée; car le jour la fera connaître, parce qu'elle sera manifestée par le feu; et le feu éprouvera quelle sera l'œuvre de chacun.
14 In abin da kowane mutum ya gina ya tsaya, zai sami lada.
Si l'œuvre de quelqu'un qui aura édifié dessus, demeure, il en recevra la récompense.
15 In ya ƙone, zai yi hasara, amma zai sami ceto, sai dai kamar wanda ya bi ta tsakiyar wuta ne.
Si l'œuvre de quelqu'un brûle, il en fera la perte; mais pour lui, il sera sauvé, toutefois comme par le feu.
16 Ashe, ba ku sani ba cewa ku kanku haikalin Allah ne, Ruhun Allah kuma yana zaune a cikinku?
Ne savez-vous pas que vous êtes le Temple de Dieu, et que l’Esprit de Dieu habite en vous?
17 Duk wanda ya ɓata haikalin Allah, Allah zai ɓata shi, don haikalin Allah mai tsarki ne, ku ne kuwa haikalin nan.
Si quelqu'un détruit le Temple de Dieu, Dieu le détruira; car le Temple de Dieu est saint, et vous êtes ce [Temple].
18 Kada ku ruɗi kanku. In waninku yana tsammani cewa yana da hikima, yadda duniya ta ɗauki hikima, to, sai ya mai da kansa “wawa” don yă zama mai hikima. (aiōn g165)
Que personne ne s'abuse lui-même; si quelqu'un d'entre vous croit être sage en ce monde, qu'il se rende fou, afin de devenir sage. (aiōn g165)
19 Gama hikimar duniyan nan, wauta ce a gaban Allah, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Yakan kama masu hikima a cikin makircinsu”;
Parce que la sagesse de ce monde est une folie devant Dieu; car il est écrit: il surprend les sages en leur ruse.
20 kuma a rubuce yake cewa, “Ubangiji ya san dukan tunanin masu hikima banza ne.”
Et encore: le Seigneur connaît que les discours des sages sont vains.
21 Saboda haka, kada wani yă yi taƙama da mutum! Gama kome naku ne,
Que personne donc ne se glorifie dans les hommes; car toutes choses sont à vous;
22 ko Bulus ko Afollos ko Kefas ko duniya ko rai ko mutuwa ko abubuwa na yanzu ko na nan gaba, ai, duka naku ne,
Soit Paul, soit Apollos, soit Céphas, soit le monde, soit la vie, soit la mort, soit les choses présentes, soit les choses à venir, toutes choses sont à vous,
23 ku kuwa na Kiristi ne, Kiristi kuma na Allah ne.
Et vous à Christ, et Christ à Dieu.

< 1 Korintiyawa 3 >