< 1 Korintiyawa 3 >
1 ’Yan’uwa, ban iya yi muku magana kamar masu ruhaniya ba, sai dai kamar masu halin mutuntaka, jarirai cikin bin Kiristi kawai.
Brothers, I could not address you as spiritual, but as worldly—as infants in Christ.
2 Na ba ku madara ba abinci mai tauri ba, domin ba ku balaga ba a lokacin. Kai, har yanzu ma, ba ku balaga ba.
I gave you milk, not solid food, for you were not yet ready for solid food. In fact, you are still not ready,
3 Har yanzu kuna rayuwa bisa ga halin mutuntaka. Da yake akwai kishi da faɗace-faɗace a cikinku, ba rayuwa irin ta halin mutuntaka ke nan kuke yi ba? Kuma ba rayuwa irin ta mutane ce kawai kuke yi ba?
for you are still worldly. For since there is jealousy and dissension among you, are you not worldly? Are you not walking in the way of man?
4 Gama sa’ad da wani ya ce, “Ni na Bulus ne,” wani kuma ya ce, “Ni na Afollos ne,” ba rayuwa irin ta mutane ke nan kuke yi ba?
For when one of you says, “I follow Paul,” and another, “I follow Apollos,” are you not mere men?
5 Shin, wane ne Afollos? Wane ne kuma Bulus? Ai, bayi ne kawai waɗanda ta wurinsu kuka gaskata, kamar yadda Ubangiji ya ba kowannensu aikinsa.
What then is Apollos? And what is Paul? They are servants through whom you believed, as the Lord has assigned to each his role.
6 Ni na shuka iri, Afollos kuma ya yi banruwa, amma Allah ne ya sa irin ya yi girma.
I planted the seed and Apollos watered it, but God made it grow.
7 Don haka, da wanda ya yi shuki, da wanda ya yi banruwa, ba a bakin kome suke ba, sai dai Allah kaɗai, mai sa abubuwa su yi girma.
So neither he who plants nor he who waters is anything, but only God, who makes things grow.
8 Mutumin da ya yi shuki, da mutumin da ya yi banruwa nufinsu ɗaya ne, kuma kowannensu zai sami lada gwargwadon aikinsa.
He who plants and he who waters are one in purpose, and each will be rewarded according to his own labor.
9 Gama mu abokan aiki ne na Allah; ku kuwa gonar ce ta Allah, ginin Allah kuma.
For we are God’s fellow workers; you are God’s field, God’s building.
10 Ta wurin alherin da Allah ya ba ni, na kafa tushen gini kamar ƙwararren magini, wani kuma dabam yana gini a kai. Amma kowa yă lura da yadda yake gini.
By the grace God has given me, I laid a foundation as an expert builder, and someone else is building on it. But each one must be careful how he builds.
11 Gama babu wanda zai iya kafa wani tushen gini dabam da wanda aka riga aka kafa, wanda yake Yesu Kiristi.
For no one can lay a foundation other than the one already laid, which is Jesus Christ.
12 In wani ya yi gini a kan tushen ginin nan da zinariya, azurfa, duwatsu masu daraja, itace, ciyawa ko kara,
If anyone builds on this foundation using gold, silver, precious stones, wood, hay, or straw,
13 aikin zai bayyana kansa, domin za a nuna shi a sarari a Ranar. Wuta ce za tă bayyana aikin, wutar kuwa za tă gwada ingancin aikin kowa.
his workmanship will be evident, because the Day will bring it to light. It will be revealed with fire, and the fire will prove the quality of each man’s work.
14 In abin da kowane mutum ya gina ya tsaya, zai sami lada.
If what he has built survives, he will receive a reward.
15 In ya ƙone, zai yi hasara, amma zai sami ceto, sai dai kamar wanda ya bi ta tsakiyar wuta ne.
If it is burned up, he will suffer loss. He himself will be saved, but only as if through the flames.
16 Ashe, ba ku sani ba cewa ku kanku haikalin Allah ne, Ruhun Allah kuma yana zaune a cikinku?
Do you not know that you yourselves are God’s temple, and that God’s Spirit dwells in you?
17 Duk wanda ya ɓata haikalin Allah, Allah zai ɓata shi, don haikalin Allah mai tsarki ne, ku ne kuwa haikalin nan.
If anyone destroys God’s temple, God will destroy him; for God’s temple is holy, and you are that temple.
18 Kada ku ruɗi kanku. In waninku yana tsammani cewa yana da hikima, yadda duniya ta ɗauki hikima, to, sai ya mai da kansa “wawa” don yă zama mai hikima. (aiōn )
Let no one deceive himself. If any of you thinks he is wise in this age, he should become a fool, so that he may become wise. (aiōn )
19 Gama hikimar duniyan nan, wauta ce a gaban Allah, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Yakan kama masu hikima a cikin makircinsu”;
For the wisdom of this world is foolishness in God’s sight. As it is written: “He catches the wise in their craftiness.”
20 kuma a rubuce yake cewa, “Ubangiji ya san dukan tunanin masu hikima banza ne.”
And again, “The Lord knows that the thoughts of the wise are futile.”
21 Saboda haka, kada wani yă yi taƙama da mutum! Gama kome naku ne,
Therefore, stop boasting in men. All things are yours,
22 ko Bulus ko Afollos ko Kefas ko duniya ko rai ko mutuwa ko abubuwa na yanzu ko na nan gaba, ai, duka naku ne,
whether Paul or Apollos or Cephas or the world or life or death or the present or the future. All of them belong to you,
23 ku kuwa na Kiristi ne, Kiristi kuma na Allah ne.
and you belong to Christ, and Christ belongs to God.