< 1 Korintiyawa 2 >

1 Da na zo wurinku’yan’uwa, ban zo da iya magana ko wani mafificin hikima yayinda na yi muku shelar shaida game da Allah ba.
And I, when I came among you, brethren, came not with excellency of language, or of human wisdom, declaring unto you the testimony of God:
2 Don na ƙudura a raina sa’ad da nake tare da ku cewa ba zan mai da hankali ga kome ba sai dai Yesu Kiristi wanda aka gicciye.
for I did not think it meet to know any thing among you, but Jesus Christ, and Him crucified.
3 Na zo wurinku cikin rashin ƙarfi da tsoro, da rawan jiki ƙwarai.
And I was with you in weakness, and in fear, and in much trembling.
4 Saƙona da wa’azina ba su zo cikin hikima da kalmomin lallashi ba, sai dai da nuna ikon Ruhu,
And my discourse, and my preaching was not with the persuasive words of human wisdom, but in the demonstration of the Spirit and of power;
5 domin kada bangaskiyarku ta dogara a kan hikimar mutane, sai dai a kan ikon Allah.
that your faith might not be in the wisdom of men, but in the power of God.
6 Duk da haka, muna sanar da saƙon hikima cikin waɗanda suka balaga, amma ba hikima irin ta wannan zamani ba ne, ko kuwa irin ta masu mulkin zamanin nan, waɗanda za su shuɗe ba. (aiōn g165)
Yet we speak true wisdom among the perfect: though not the wisdom of this world, nor of the rulers of this world, who come to nought. (aiōn g165)
7 A’a, muna magana ne a kan asirin hikimar Allah, hikimar da tun dā, take a ɓoye, wadda Allah ya ƙaddara domin ɗaukakarmu, tun kafin farkon zamanai. (aiōn g165)
But we speak the wisdom of God in a mystery, that hidden wisdom which God ordained before the worlds for our glory: (aiōn g165)
8 Ba ko ɗaya daga cikin masu mulkin wannan zamani da ya fahimce ta, gama da a ce sun fahimce ta, da ba su gicciye Ubangiji mai ɗaukaka ba. (aiōn g165)
which none of the rulers of this age knew; for if they had known it, they would not have crucified the Lord of glory. (aiōn g165)
9 Duk da haka, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Ba idon da ya taɓa gani, ba kunnen da ya taɓa ji, ba kuma zuciyar da ta taɓa tunanin abin da Allah ya shirya wa masu ƙaunarsa.”
But as it is written, "Eye hath not seen, and ear hath not heard, nor have entered into the heart of man, what things God hath prepared for those that love Him."
10 Amma Allah ya bayyana mana shi ta wurin Ruhunsa. Ruhu yana bincika dukan abubuwa, har ma da abubuwa masu zurfi na Allah.
But God hath revealed them to us by his Spirit: for the Spirit searcheth all things, even the deep things of God.
11 Wane ne a cikin mutane ya san tunanin mutum, in ba ruhun mutumin da yake cikinsa ba? Haka kuma ba wanda ya san tunanin Allah, sai dai Ruhun Allah.
For who among men knoweth the things of a man, but the spirit of a man which is in him? so also the things of God no one knoweth, but the Spirit of God.
12 Ba mu karɓi ruhun duniya ba, sai dai Ruhun da yake daga Allah, domin mu fahimci abin da Allah ya ba mu hannu sake.
Now we have received, not the spirit of the world, but the Spirit of God; that we might know the things that are graciously bestowed upon us by God:
13 Wannan shi ne abin da muke sanarwa, ba da kalmomin da muka koya ta wurin hikimar mutum ba, amma da kalmomin da Ruhu yake koyarwa, muna faɗin gaskiya ta ruhaniya da kalmomin ruhaniya.
which we also speak of, not in words dictated by human wisdom, but in those which are dictated by the holy Spirit; explaining spiritual things by spiritual words.
14 Mutumin da ba shi da Ruhu, ba ya yarda da abubuwan da suka fita daga Ruhun Allah, domin wauta ce a gare shi. Ba kuwa zai fahimce su ba, domin ta Ruhu ne ake fahimtarsu.
But the natural man receiveth not the things of the Spirit of God: for they are foolishness to him; and he cannot understand them, because they are spiritually discerned.
15 Mutumin ruhaniya yakan gwada dukan abubuwa, amma shi kansa ba ya ƙarƙashin shari’ar mutum.
Whereas the spiritual man discerneth all things, yet is himself discerned by no one.
16 “Wa ya taɓa sanin hankalin Ubangiji, har da zai koya masa?” Amma muna da tunani iri na Kiristi ne.
For who hath known the mind of the Lord, to instruct him? But we have the mind of Christ.

< 1 Korintiyawa 2 >