< 1 Korintiyawa 16 >

1 To, game da tara kuɗi domin taimakon mutanen Allah, ku yi abin da na gaya wa ikkilisiyoyin Galatiyawa.
Now concerning the collections that are made for the saints, as I have given order to the churches of Galatia, so do ye also.
2 A ranar farko ta kowace mako, ya kamata kowannenku yă keɓe’yan kuɗi bisa ga abin da yake samu, yă ajiye, ba sai na zo kafin a tara taimakon ba.
On the first day of the week let every one of you put apart with himself, laying up what it shall well please him; that when I come, the collections be not then to be made.
3 In kuwa na iso sai in ba da wasiƙun gabatarwa ga mutanen da kuka amince da su, in kuma aike su da taimakonku zuwa Urushalima.
And when I shall be with you, whomsoever you shall approve by letters, them will I send to carry your grace to Jerusalem.
4 In kuma ya dace in tafi, to, sai su tafi tare da ni.
And if it be meet that I also go, they shall go with me.
5 Bayan na zazzaga Makidoniya, zan zo wurinku, domin zan ratsa ta Makidoniya.
Now I will come to you, when I shall have passed through Macedonia. For I shall pass through Macedonia.
6 Wataƙila zan ɗan jima a wajenku, ko ma in ci damina a can, domin ku yi mini rakiya a tafiyata, duk inda za ni.
And with you perhaps I shall abide, or even spend the winter: that you may bring me on my way whithersoever I shall go.
7 Ba na so in gan ku yanzu in wuce kawai, ina fata zan yi’yan kwanaki tare da ku, in Ubangiji ya yarda.
For I will not see you now by the way, for I trust that I shall abide with you some time, if the Lord permit.
8 Sai dai zan kasance a Afisa har lokacin Fentekos,
But I will tarry at Ephesus until Pentecost.
9 domin an buɗe mini wata hanya mai fāɗi don aiki mai amfani, ko da yake akwai mutane da yawa masu gāba da ni.
For a great door and evident is opened unto me: and many adversaries.
10 In Timoti ya zo, ku tabbata ya sami sakewa a cikinku, domin aikin Ubangiji yake yi kamar yadda nake yi.
Now if Timothy come, see that he be with you without fear, for he worketh the work of the Lord, as I also do.
11 Kada fa wani yă ƙi karɓansa. Ku sallame shi lafiya, domin yă koma wurina. Ina duban hanyarsa tare da’yan’uwa.
Let no man therefore despise him, but conduct ye him on his way in peace: that he may come to me. For I look for him with the brethren.
12 Batun ɗan’uwanmu Afollos kuwa, na roƙe shi sosai yă zo wurinku tare da’yan’uwa. Bai so zuwa yanzu ba, amma zai zo in ya sami zarafi.
And touching our brother Apollo, I give you to understand, that I much entreated him to come unto you with the brethren: and indeed it was not his will at all to come at this time. But he will come when he shall have leisure.
13 Ku zauna a faɗake; ku dāge cikin bangaskiya; ku zauna da ƙarfafawa; ku yi ƙarfi.
Watch ye, stand fast in the faith, do manfully, and be strengthened.
14 Ku yi kome da ƙauna.
Let all your things be done in charity.
15 Kun san cewa iyalin gidan Istifanas ne suka fara tuba a Akayya. Sun kuma ba da kansu ga yi wa tsarkaka hidima. Ina roƙonku’yan’uwa,
And I beseech you, brethren, you know the house of Stephanas, and of Fortunatus, and of Achaicus, that they are the firstfruits of Achaia, and have dedicated themselves to the ministry of the saints:
16 ku ba da kanku ga irin waɗannan, ga kuma kowa da ya haɗa hannu a aikin, yana kuma faman a cikinsa.
That you also be subject to such, and to every one that worketh with us, and laboureth.
17 Na yi farin ciki da isowar Istifanas, Fortunatus da Akaikus, domin sun biya bukatar da ba ku iya biya ba.
And I rejoice in the presence of Stephanas, and Fortunatus, and Achaicus, because that which was wanting on your part, they have supplied.
18 Gama sun wartsake ruhuna da kuma naku. Ya kamata ku girmama irin waɗannan mutane.
For they have refreshed both my spirit and yours. Know them, therefore, that are such.
19 Ikkilisiyoyin da suke a lardin Asiya suna gaisuwa. Akwila da Firiskila suna gaishe ku sosai cikin Ubangiji, haka ma ikkilisiyar da takan taru a gidansu.
The churches of Asia salute you. Aquila and Priscilla salute you much in the Lord, with the church that is in their house, with whom I also lodge.
20 Dukan’yan’uwa a nan suna gaisuwa. Ku gai da juna da sumba mai tsarki.
All the brethren salute you. Salute one another with a holy kiss.
21 Ni, Bulus nake rubuta wannan gaisuwa da hannuna.
The salutation of me Paul, with my own hand.
22 Duk wanda ba ya ƙaunar Ubangiji, la’ana ta zauna a kansa. Zo, ya Ubangiji!
If any man love not our Lord Jesus Christ, let him be anathema, maranatha.
23 Alherin Ubangiji Yesu yă kasance tare da ku.
The grace of our Lord Jesus Christ be with you.
24 Ina gaishe ku duka, gaisuwar ƙaunata cikin Kiristi Yesu. Amin.
My charity be with you all in Christ Jesus. Amen.

< 1 Korintiyawa 16 >