< 1 Korintiyawa 15 >

1 To,’yan’uwa, ina so in tuna muku da bisharar da na yi muku wa’azinta, wadda kuka karɓa, wadda kuma kuka yanke shawara ku tsaya a kai.
Je vous annonce maintenant, frères, la bonne nouvelle que je vous ai annoncée, que vous avez aussi reçue, dans laquelle vous vous tenez aussi,
2 Ta wurin wannan bisharar ce kuka sami ceto, muddin kuna riƙe da wa’azin da na yi muku kam-kam. In ba haka ba, kun gaskata a banza ke nan.
par laquelle aussi vous êtes sauvés, si vous retenez fermement la parole que je vous ai annoncée - à moins que vous n'ayez cru en vain.
3 Gama abu farko mafi muhimmancin da na karɓo shi ne na ba ku cewa Kiristi ya mutu domin zunubanmu bisa ga Nassi,
Je vous ai transmis avant tout ce que j'ai moi-même reçu, à savoir que, selon les Écritures, Christ est mort pour nos péchés,
4 cewa an binne shi an kuma tashe shi a rana ta uku bisa ga Nassi,
qu'il a été enseveli, qu'il est ressuscité le troisième jour, selon les Écritures,
5 cewa ya bayyana ga Bitrus, sa’an nan ga Sha Biyun.
et qu'il est apparu à Céphas, puis aux douze.
6 Bayan haka, ya bayyana ga fiye da ɗari biyar daga cikin’yan’uwa a lokaci guda. Yawancinsu kuwa suna nan da rai, ko da yake waɗansu sun riga sun yi barci.
Puis il est apparu à plus de cinq cents frères à la fois, dont la plupart sont restés jusqu'à présent, mais dont quelques-uns se sont aussi endormis.
7 Sa’an nan ya bayyana ga Yaƙub, sa’an nan ga dukan manzannin,
Il est ensuite apparu à Jacques, puis à tous les apôtres,
8 a ƙarshe duka, ya bayyana a gare ni, kamar wanda an haifa a lokacin da bai kamata ba.
et enfin, comme à l'enfant né à contretemps, à moi aussi il est apparu.
9 Gama ni ne mafi ƙanƙanta a cikin manzanni, ban kuma isa a kira ni manzo ba, domin na tsananta wa ikkilisiyar Allah.
Car je suis le plus petit des apôtres, qui n'est pas digne d'être appelé apôtre, parce que j'ai persécuté l'assemblée de Dieu.
10 Amma bisa ga alherin Allah, na zama abin da nake, alherinsa zuwa gare ni kuwa bai zama a banza ba. A’a, na yi aiki fiye da dukansu, duk da haka, ba ni ba ne, sai dai alherin Allah da yake tare da ni ne.
Mais c'est par la grâce de Dieu que je suis ce que je suis. La grâce qui m'a été accordée n'a pas été vaine; mais j'ai travaillé plus qu'eux tous, non pas moi, mais la grâce de Dieu qui était avec moi.
11 To, ko ni ne, ko su ne, wannan shi ne abin da muke wa’azi, shi ne kuma abin da kuka gaskata.
Que ce soit donc moi ou eux, ainsi nous prêchons, et ainsi vous avez cru.
12 Amma in ana wa’azi cewa Kiristi ya tashi daga matattu, yaya waɗansu a cikinku suke cewa babu tashin matattu?
Or, si l'on prêche que le Christ est ressuscité des morts, comment quelques-uns d'entre vous disent-ils qu'il n'y a pas de résurrection des morts?
13 In babu tashin matattu, to, ba a tā da Kiristi ma ba ke nan.
Mais s'il n'y a pas de résurrection des morts, Christ non plus n'est pas ressuscité.
14 In ba a tashe Kiristi ba kuwa, ai, wa’azinmu, da bangaskiyarku banza ne.
Si Christ n'est pas ressuscité, notre prédication est donc vaine, et votre foi aussi est vaine.
15 Sai ma ya zama mun zama masu ba da shaidar ƙarya game da Allah ke nan, domin mun shaida game da Allah cewa ya tashe Kiristi daga matattu. Bai tashe Kiristi ba ke nan, in lalle ba a tā da matattu.
Oui, nous sommes aussi trouvés faux témoins de Dieu, parce que nous avons témoigné de Dieu qu'il a ressuscité le Christ, qu'il n'a pas ressuscité, s'il est vrai que les morts ne ressuscitent pas.
16 Gama in ba a tā da matattu ba, to, Kiristi ma ba a tashe shi ba ke nan.
Car si les morts ne ressuscitent pas, Christ non plus n'est pas ressuscité.
17 In kuwa ba a tashe Kiristi ba, bangaskiyarku a banza take, ya zama har yanzu kuna cikin zunubanku ke nan.
Si Christ n'est pas ressuscité, votre foi est vaine; vous êtes encore dans vos péchés.
18 Ashe, waɗanda suka yi barci a cikin Kiristi ma sun hallaka ke nan.
Et ceux qui se sont endormis en Christ ont péri.
19 In a wannan rayuwar ce kaɗai muke da bege cikin Kiristi, mun zama abin tausayi fiye da dukan mutane.
Si nous n'avons espéré en Christ qu'en cette vie, nous sommes de tous les hommes les plus à plaindre.
20 Amma tabbatacce, an tā da Kiristi daga matattu, nunan fari kuwa cikin waɗanda suka yi barci.
Mais maintenant, le Christ est ressuscité des morts. Il est devenu le premier fruit de ceux qui dorment.
21 Da yake mutuwa ta zo ta wurin mutum, haka tashin matattu ma ya zo ta wurin mutum.
En effet, puisque la mort est venue de l'homme, la résurrection des morts est aussi venue de l'homme.
22 Kamar yadda duka suka mutu cikin Adamu, haka duka za su rayu cikin Kiristi.
Car, de même qu'en Adam tous meurent, de même en Christ tous seront rendus à la vie.
23 Sai dai kowa da lokacinsa. Kiristi ne nunan fari; sa’an nan sa’ad da ya dawo; za a tā da waɗanda suke nasa.
Mais chacun selon son propre ordre: Christ, les prémices, puis ceux qui appartiendront à Christ lors de son avènement.
24 Sa’an nan sai ƙarshen ta zo, sa’ad da zai miƙa wa Allah Uba mulki, bayan ya hallaka dukan sarauta, mulki da iko.
Puis viendra la fin, quand il remettra le Royaume à Dieu le Père, quand il aura aboli toute domination, toute autorité et toute puissance.
25 Gama dole yă yi mulki har sai ya sa dukan abokan gābansa a ƙarƙashin ƙafafunsa.
Car il faut qu'il règne jusqu'à ce qu'il ait mis tous ses ennemis sous ses pieds.
26 Abokin gāba na ƙarshen da za a hallaka kuwa, shi ne mutuwa.
Le dernier ennemi qui sera aboli, c'est la mort.
27 Gama ya “sa kome a ƙarƙashin ƙafafunsa.” To, da aka ce an sa “kome” a ƙarƙashinsa, a fili yake cewa ba a haɗa da Allah a ciki ba, shi wannan da ya sa kome a ƙarƙashin Kiristi.
Car « il a soumis toutes choses sous ses pieds ». Mais quand il dit: « Toutes choses lui sont soumises », il est évident que c'est lui qui lui a soumis toutes choses.
28 Sa’ad da ya yi haka, sa’an nan Ɗan kansa yă koma a ƙarƙashin shi wanda ya sa kome a ƙarƙashinsa, domin Allah yă zama kome da kome.
Quand toutes choses lui auront été soumises, alors le Fils aussi sera soumis à celui qui lui a soumis toutes choses, afin que Dieu soit tout en tous.
29 To, in babu tashin matattu, mene ne waɗanda ake musu baftisma saboda matattu za su yi? In ba a tā da matattu sam, me ya sa ake yin wa mutane baftisma saboda su?
Ou bien que feront ceux qui sont baptisés pour les morts? Si les morts ne ressuscitent pas du tout, pourquoi donc sont-ils baptisés pour les morts?
30 Mu ma don me muke sa kanmu cikin hatsari a kowace sa’a?
Pourquoi nous aussi, à chaque heure, sommes-nous en péril?
31 Ina fuskantar mutuwa kowace rana. I, kamar yadda yake tabbatacce cewa ina taƙama da ku cikin Kiristi Yesu Ubangijinmu.
J'affirme, par la vantardise que j'ai en vous dans le Christ Jésus notre Seigneur, que je meurs chaque jour.
32 In na yi kokawa da mugayen namomin jeji a Afisa bisa ga ra’ayin mutane ne kawai, mece ce ribata, in har ba a tā da matattu? Ai, “Sai mu ci mu sha, da yake gobe za mu mutu.”
Si, à Éphèse, j'ai combattu avec des animaux dans un but humain, qu'est-ce que cela me rapporte? Si les morts ne ressuscitent pas, alors « mangeons et buvons, car demain nous mourrons ».
33 Kada fa a ruɗe ku, “Ajiyar mugayen abokai yana ɓata hali mai kyau.”
Ne vous laissez pas tromper! « Les mauvaises fréquentations corrompent les bonnes mœurs ».
34 Ku koma cikin hankalinku yadda ya kamata, ku kuma daina yin zunubi, gama akwai waɗansu da ba su san Allah ba, na faɗi wannan ne don ku kunyata.
Réveillez-vous avec droiture et ne péchez pas, car certains ne connaissent pas Dieu. Je dis cela pour votre honte.
35 Amma wani yana iya tambaya yă ce, “Ta yaya ake tā da matattun? Da wane irin jiki za su tashi?”
Mais quelqu'un dira: « Comment les morts ressuscitent-ils? » et « Avec quelle sorte de corps viennent-ils? »
36 Kai, marar azanci! Abin da kuka shuka ba zai tsira ba sai ya mutu.
Toi, l'insensé, ce que tu sèmes toi-même n'est pas rendu vivant s'il ne meurt pas.
37 Sa’ad da kuke shuki, ba tsiron da zai yi girma ba ne kuka shuka, ƙwayar ce kawai, ko ta alkama ko kuma na wani irin dabam.
Ce que tu sèmes, tu ne sèmes pas le corps qui sera, mais un grain nu, peut-être de blé, ou d'une autre espèce.
38 Amma Allah yakan ba ƙwayar jiki yadda ya yi niyya, kuma ga kowane irin ƙwaya yakan ba ta irin jikinta.
Mais Dieu lui donne un corps comme il lui a plu, et à chaque graine un corps qui lui est propre.
39 Ba dukan nama ne iri ɗaya ba. Mutane da irin nasu, dabbobi da irin nasu, tsuntsaye da irin nasu, kifaye kuma da irin nasu.
Toute chair n'est pas la même chair, mais il y a une chair d'hommes, une autre d'animaux, une autre de poissons, une autre d'oiseaux.
40 Akwai jikuna iri na samaniya, akwai kuma jikuna iri na duniya; sai dai darajar jikunan samaniya dabam take, darajar jikunan duniya kuma dabam take.
Il y a aussi des corps célestes et des corps terrestres; mais la gloire des célestes diffère de celle des terrestres.
41 Rana tana da wata irin daraja, wata yana da wata darajar dabam, taurari kuma suna da tasu dabam. Wani tauraro kuwa yakan bambanta da wani a wajen daraja.
Il y a une gloire du soleil, une autre gloire de la lune, et une autre gloire des étoiles; car une étoile diffère d'une autre étoile en gloire.
42 Haka ne tashin matattu zai kasance. Abin da aka shuka yakan ruɓe, abin da aka tā da shi kuma ba ya ruɓewa;
Il en est de même de la résurrection des morts. Le corps est semé périssable, il ressuscite impérissable.
43 akan shuka shi cikin ƙasƙanci, a kuma tā da shi cikin ɗaukaka, akan shuka shi da rashin ƙarfi, a kuma tā da shi da ƙarfi;
Il a été semé dans le déshonneur, il ressuscite dans la gloire. Il est semé dans la faiblesse, il ressuscite dans la puissance.
44 akan shuka shi da jiki na mutuntaka, a kuma tā da shi da jikin ruhaniya. In akwai jiki na mutuntaka, to, lalle akwai jikin ruhaniya ma.
Il est semé dans un corps naturel, il ressuscite dans un corps spirituel. Il y a un corps naturel, et il y a aussi un corps spirituel.
45 Haka yake a rubuce cewa, “Adamu, mutumin farko ya zama mai rai”; Adamu na ƙarshe kuwa ruhu ne mai ba da rai.
Ainsi, il est aussi écrit: « Le premier homme, Adam, est devenu une âme vivante. » Le dernier Adam est devenu un esprit qui donne la vie.
46 Ba jikin ruhaniya ne ya zo da farko ba, na mutuntakan ne, daga baya kuma sai na ruhaniya.
Cependant, ce qui est spirituel n'est pas premier, mais ce qui est naturel, puis ce qui est spirituel.
47 Mutumin farko daga turɓaya ce ya fito, mutum na biyu kuwa daga sama ne ya fito.
Le premier homme est de la terre, fait de poussière. Le second homme est le Seigneur du ciel.
48 Kamar yadda mutumin turɓaya yake, haka ma waɗanda suke na turɓaya. Kuma kamar yadda mutumin sama yake, haka ma waɗanda suke na sama.
Tel est celui qui est fait de poussière, tels sont ceux qui sont aussi faits de poussière; et tel est le céleste, tels sont aussi ceux qui sont célestes.
49 Kamar dai yadda muka ɗauki siffar mutumin turɓaya, haka kuma za mu ɗauki siffar mutumin sama.
Comme nous avons porté l'image de ceux qui sont faits de poussière, portons aussi l'image de ceux qui sont célestes.
50 Ina sanar da ku,’yan’uwa, cewa nama da jini ba za su gāji mulkin Allah ba, haka ma ruɓa ba zai gāji rashin ruɓa ba.
Or, je dis ceci, frères: la chair et le sang ne peuvent hériter du royaume de Dieu, et les choses périssables n'héritent pas des choses impérissables.
51 Ku saurara, in gaya muku wani asiri. Ba dukanmu ne za mu yi barci ba, sai dai duk za a sauya kamanninmu
Voici, je vous dis un mystère. Nous ne dormirons pas tous, mais nous serons tous changés,
52 farat ɗaya, cikin ƙyaftawar ido, da busan ƙaho na ƙarshe. Gama za a busa ƙaho, za a tā da matattu da jiki irin da ba ya ruɓewa, za a kuma sauya kamanninmu.
en un instant, en un clin d'œil, à la dernière trompette. Car la trompette sonnera, et les morts ressusciteront incorruptibles, et nous serons changés.
53 Gama dole mai ruɓa yă maye wa mai ruɓan nan, marar mutuwa kuma yă maye wa mai mutuwan nan.
Car il faut que ce corps périssable devienne impérissable, et que ce mortel revête l'immortalité.
54 Sa’ad da mai ruɓan nan ya maye marar ruɓan nan, mai mutuwa kuma ya maye marar mutuwan nan, sa’an nan ne karin maganar da yake a rubuce zai zama gaskiya cewa, “An haɗiye mutuwa cikin nasara.”
Mais quand ce corps périssable sera devenu impérissable, et que ce mortel aura revêtu l'immortalité, alors ce qui est écrit arrivera: « La mort a été engloutie dans la victoire. »
55 “Ya ke mutuwa, ina nasararki? Ya ke mutuwa, ina dafinki?” (Hadēs g86)
« Mort, où est ton aiguillon? Hadès, où est ta victoire? » (Hadēs g86)
56 Zunubi ne yake ba wa mutuwa dafi, Doka kuma take ba wa zunubi iko.
L'aiguillon de la mort, c'est le péché, et la puissance du péché, c'est la loi.
57 Amma godiya ga Allah! Shi ne ya ba mu nasara ta wurin Ubangijinmu Yesu Kiristi.
Mais grâces soient rendues à Dieu, qui nous donne la victoire par notre Seigneur Jésus-Christ.
58 Saboda haka, ƙaunatattu’yan’uwana, ku tsaya da daram. Kada wani abu yă jijjiga ku. Ku ba da kanku kullum ga aikin Ubangiji, domin kun san cewa famar da kuke yi saboda Ubangiji ba a banza take ba.
C'est pourquoi, mes frères bien-aimés, soyez fermes, inébranlables, persévérant dans l'œuvre du Seigneur, sachant que votre travail n'est pas vain dans le Seigneur.

< 1 Korintiyawa 15 >