< 1 Korintiyawa 15 >
1 To,’yan’uwa, ina so in tuna muku da bisharar da na yi muku wa’azinta, wadda kuka karɓa, wadda kuma kuka yanke shawara ku tsaya a kai.
But let me recall to you, brethren, the Good News which I brought you, which you accepted, and on which you are standing,
2 Ta wurin wannan bisharar ce kuka sami ceto, muddin kuna riƙe da wa’azin da na yi muku kam-kam. In ba haka ba, kun gaskata a banza ke nan.
through which also you are obtaining salvation, if you bear in mind the words in which I proclaimed it--unless indeed your faith has been unreal from the very first.
3 Gama abu farko mafi muhimmancin da na karɓo shi ne na ba ku cewa Kiristi ya mutu domin zunubanmu bisa ga Nassi,
For I repeated to you the all-important fact which also I had been taught, that Christ died for our sins in accordance with the Scriptures;
4 cewa an binne shi an kuma tashe shi a rana ta uku bisa ga Nassi,
that He was buried; that He rose to life again on the third day in accordance with the Scriptures,
5 cewa ya bayyana ga Bitrus, sa’an nan ga Sha Biyun.
and was seen by Peter, and then by the Twelve.
6 Bayan haka, ya bayyana ga fiye da ɗari biyar daga cikin’yan’uwa a lokaci guda. Yawancinsu kuwa suna nan da rai, ko da yake waɗansu sun riga sun yi barci.
Afterwards He was seen by more than five hundred brethren at once, most of whom are still alive, although some of them have now fallen asleep.
7 Sa’an nan ya bayyana ga Yaƙub, sa’an nan ga dukan manzannin,
Afterwards He was seen by James, and then by all the Apostles.
8 a ƙarshe duka, ya bayyana a gare ni, kamar wanda an haifa a lokacin da bai kamata ba.
And last of all, as to one of untimely birth, He appeared to me also.
9 Gama ni ne mafi ƙanƙanta a cikin manzanni, ban kuma isa a kira ni manzo ba, domin na tsananta wa ikkilisiyar Allah.
For I am the least of the Apostles, and am not fit to be called an Apostle--because I persecuted the Church of God.
10 Amma bisa ga alherin Allah, na zama abin da nake, alherinsa zuwa gare ni kuwa bai zama a banza ba. A’a, na yi aiki fiye da dukansu, duk da haka, ba ni ba ne, sai dai alherin Allah da yake tare da ni ne.
But what I am I am by the grace of God, and His grace bestowed upon me did not prove ineffectual. But I labored more strenuously than all the rest--yet it was not I, but God's grace working with me.
11 To, ko ni ne, ko su ne, wannan shi ne abin da muke wa’azi, shi ne kuma abin da kuka gaskata.
But whether it is I or they, this is the way we preach and the way that you came to believe.
12 Amma in ana wa’azi cewa Kiristi ya tashi daga matattu, yaya waɗansu a cikinku suke cewa babu tashin matattu?
But if Christ is preached as having risen from the dead, how is it that some of you say that there is no such thing as a resurrection of the dead?
13 In babu tashin matattu, to, ba a tā da Kiristi ma ba ke nan.
If there is no such thing as a resurrection of the dead, then Christ Himself has not risen to life.
14 In ba a tashe Kiristi ba kuwa, ai, wa’azinmu, da bangaskiyarku banza ne.
And if Christ has not risen, it follows that what we preach is a delusion, and that your faith also is a delusion.
15 Sai ma ya zama mun zama masu ba da shaidar ƙarya game da Allah ke nan, domin mun shaida game da Allah cewa ya tashe Kiristi daga matattu. Bai tashe Kiristi ba ke nan, in lalle ba a tā da matattu.
Nay more, we are actually being discovered to be bearing false witness about God, because we have testified that God raised Christ to life, whom He did not raise, if in reality none of the dead are raised.
16 Gama in ba a tā da matattu ba, to, Kiristi ma ba a tashe shi ba ke nan.
For if none of the dead are raised to life, then Christ has not risen;
17 In kuwa ba a tashe Kiristi ba, bangaskiyarku a banza take, ya zama har yanzu kuna cikin zunubanku ke nan.
and if Christ has not risen, your faith is a vain thing--you are still in your sins.
18 Ashe, waɗanda suka yi barci a cikin Kiristi ma sun hallaka ke nan.
It follows also that those who have fallen asleep in Christ have perished.
19 In a wannan rayuwar ce kaɗai muke da bege cikin Kiristi, mun zama abin tausayi fiye da dukan mutane.
If in this present life we have a hope resting on Christ, and nothing more, we are more to be pitied than all the rest of the world.
20 Amma tabbatacce, an tā da Kiristi daga matattu, nunan fari kuwa cikin waɗanda suka yi barci.
But, in reality, Christ has risen from among the dead, being the first to do so of those who are asleep.
21 Da yake mutuwa ta zo ta wurin mutum, haka tashin matattu ma ya zo ta wurin mutum.
For seeing that death came through man, through man comes also the resurrection of the dead.
22 Kamar yadda duka suka mutu cikin Adamu, haka duka za su rayu cikin Kiristi.
For just as through Adam all die, so also through Christ all will be made alive again.
23 Sai dai kowa da lokacinsa. Kiristi ne nunan fari; sa’an nan sa’ad da ya dawo; za a tā da waɗanda suke nasa.
But this will happen to each in the right order--Christ having been the first to rise, and afterwards Christ's people rising at His return.
24 Sa’an nan sai ƙarshen ta zo, sa’ad da zai miƙa wa Allah Uba mulki, bayan ya hallaka dukan sarauta, mulki da iko.
Later on, comes the End, when He is to surrender the Kingship to God, the Father, when He shall have overthrown all other government and all other authority and power.
25 Gama dole yă yi mulki har sai ya sa dukan abokan gābansa a ƙarƙashin ƙafafunsa.
For He must continue King until He shall have put all His enemies under His feet.
26 Abokin gāba na ƙarshen da za a hallaka kuwa, shi ne mutuwa.
The last enemy that is to be overthrown is Death;
27 Gama ya “sa kome a ƙarƙashin ƙafafunsa.” To, da aka ce an sa “kome” a ƙarƙashinsa, a fili yake cewa ba a haɗa da Allah a ciki ba, shi wannan da ya sa kome a ƙarƙashin Kiristi.
for He will have put all things in subjection under His feet. And when He shall have declared that "All things are in subjection," it will be with the manifest exception of Him who has reduced them all to subjection to Him.
28 Sa’ad da ya yi haka, sa’an nan Ɗan kansa yă koma a ƙarƙashin shi wanda ya sa kome a ƙarƙashinsa, domin Allah yă zama kome da kome.
But when the whole universe has been made subject to Him, then the Son Himself will also become subject to Him who has made the universe subject to Him, in order that GOD may be all in all.
29 To, in babu tashin matattu, mene ne waɗanda ake musu baftisma saboda matattu za su yi? In ba a tā da matattu sam, me ya sa ake yin wa mutane baftisma saboda su?
Otherwise what will become of those who got themselves baptized for the dead? If the dead do not rise at all, why are these baptized for them?
30 Mu ma don me muke sa kanmu cikin hatsari a kowace sa’a?
Why also do we Apostles expose ourselves to danger every hour?
31 Ina fuskantar mutuwa kowace rana. I, kamar yadda yake tabbatacce cewa ina taƙama da ku cikin Kiristi Yesu Ubangijinmu.
I protest, brethren, as surely as I glory over you--which I may justly do in Christ Jesus our Lord--that I die day by day.
32 In na yi kokawa da mugayen namomin jeji a Afisa bisa ga ra’ayin mutane ne kawai, mece ce ribata, in har ba a tā da matattu? Ai, “Sai mu ci mu sha, da yake gobe za mu mutu.”
If from merely human motives I have fought with wild beasts in Ephesus, what profit is it to me? If the dead do not rise, let us eat and drink, for tomorrow we are to die.
33 Kada fa a ruɗe ku, “Ajiyar mugayen abokai yana ɓata hali mai kyau.”
Do not deceive yourselves: "Evil companionships corrupt good morals."
34 Ku koma cikin hankalinku yadda ya kamata, ku kuma daina yin zunubi, gama akwai waɗansu da ba su san Allah ba, na faɗi wannan ne don ku kunyata.
Wake from this drunken fit; live righteous lives, and cease to sin; for some have no knowledge of God: I speak thus in order to move you to shame.
35 Amma wani yana iya tambaya yă ce, “Ta yaya ake tā da matattun? Da wane irin jiki za su tashi?”
But some one will say, "How can the dead rise? And with what kind of body do they come back?"
36 Kai, marar azanci! Abin da kuka shuka ba zai tsira ba sai ya mutu.
Foolish man! the seed you yourself sow has no life given to it unless it first dies;
37 Sa’ad da kuke shuki, ba tsiron da zai yi girma ba ne kuka shuka, ƙwayar ce kawai, ko ta alkama ko kuma na wani irin dabam.
and as for what you sow, it is not the plant which is to be that you are sowing, but a bare grain, of wheat (it may be) or of something else, and God gives it a body as He has seen fit,
38 Amma Allah yakan ba ƙwayar jiki yadda ya yi niyya, kuma ga kowane irin ƙwaya yakan ba ta irin jikinta.
and to each kind of seed a body of its own.
39 Ba dukan nama ne iri ɗaya ba. Mutane da irin nasu, dabbobi da irin nasu, tsuntsaye da irin nasu, kifaye kuma da irin nasu.
All flesh is not the same: there is human flesh, and flesh of cattle, of birds, and of fishes.
40 Akwai jikuna iri na samaniya, akwai kuma jikuna iri na duniya; sai dai darajar jikunan samaniya dabam take, darajar jikunan duniya kuma dabam take.
There are bodies which are celestial and there are bodies which are earthly, but the glory of the celestial ones is one thing, and that of the earthly ones is another.
41 Rana tana da wata irin daraja, wata yana da wata darajar dabam, taurari kuma suna da tasu dabam. Wani tauraro kuwa yakan bambanta da wani a wajen daraja.
There is one glory of the sun, another of the moon, and another of the stars; for star differs from star in glory.
42 Haka ne tashin matattu zai kasance. Abin da aka shuka yakan ruɓe, abin da aka tā da shi kuma ba ya ruɓewa;
It is the same with the resurrection of the dead. The body is sown in a state of decay, it is raised free from decay;
43 akan shuka shi cikin ƙasƙanci, a kuma tā da shi cikin ɗaukaka, akan shuka shi da rashin ƙarfi, a kuma tā da shi da ƙarfi;
it is sown in dishonor, it is raised in glory; it is sown in weakness, it is raised in power;
44 akan shuka shi da jiki na mutuntaka, a kuma tā da shi da jikin ruhaniya. In akwai jiki na mutuntaka, to, lalle akwai jikin ruhaniya ma.
an animal body is sown, a spiritual body is raised. As surely as there is an animal body, so there is also a spiritual body.
45 Haka yake a rubuce cewa, “Adamu, mutumin farko ya zama mai rai”; Adamu na ƙarshe kuwa ruhu ne mai ba da rai.
In the same way also it is written, "The first man Adam became a living animal"; the last Adam is a life-giving Spirit.
46 Ba jikin ruhaniya ne ya zo da farko ba, na mutuntakan ne, daga baya kuma sai na ruhaniya.
Nevertheless, it is not what is spiritual that came first, but what is animal; what is spiritual came afterwards.
47 Mutumin farko daga turɓaya ce ya fito, mutum na biyu kuwa daga sama ne ya fito.
The first man is a man of earth, earthy; the second man is from Heaven.
48 Kamar yadda mutumin turɓaya yake, haka ma waɗanda suke na turɓaya. Kuma kamar yadda mutumin sama yake, haka ma waɗanda suke na sama.
What the earthy one is, that also are those who are earthy; and what the heavenly One is, that also are those who are heavenly.
49 Kamar dai yadda muka ɗauki siffar mutumin turɓaya, haka kuma za mu ɗauki siffar mutumin sama.
And as we have borne a resemblance to the earthy one, let us see to it that we also bear a resemblance to the heavenly One.
50 Ina sanar da ku,’yan’uwa, cewa nama da jini ba za su gāji mulkin Allah ba, haka ma ruɓa ba zai gāji rashin ruɓa ba.
But this I tell you, brethren: our mortal bodies cannot inherit the Kingdom of God, nor will what is perishable inherit what is imperishable.
51 Ku saurara, in gaya muku wani asiri. Ba dukanmu ne za mu yi barci ba, sai dai duk za a sauya kamanninmu
I tell you a truth hitherto kept secret: we shall not all sleep, but we shall all be changed,
52 farat ɗaya, cikin ƙyaftawar ido, da busan ƙaho na ƙarshe. Gama za a busa ƙaho, za a tā da matattu da jiki irin da ba ya ruɓewa, za a kuma sauya kamanninmu.
in a moment, in the twinkling of an eye, at the sounding of the last trumpet; for the trumpet will sound, and the dead will be raised incapable of decay, and we shall be changed.
53 Gama dole mai ruɓa yă maye wa mai ruɓan nan, marar mutuwa kuma yă maye wa mai mutuwan nan.
For so it must be: this perishable nature must clothe itself with what is imperishable, and this mortality must clothe itself with immortality.
54 Sa’ad da mai ruɓan nan ya maye marar ruɓan nan, mai mutuwa kuma ya maye marar mutuwan nan, sa’an nan ne karin maganar da yake a rubuce zai zama gaskiya cewa, “An haɗiye mutuwa cikin nasara.”
But when this perishable nature has put on what is imperishable, and this mortality has put on immortality, then will the words of Scripture be fulfilled, "Death has been swallowed up in victory."
55 “Ya ke mutuwa, ina nasararki? Ya ke mutuwa, ina dafinki?” (Hadēs )
"Where, O death, is thy victory? Where, O death, is thy sting?" (Hadēs )
56 Zunubi ne yake ba wa mutuwa dafi, Doka kuma take ba wa zunubi iko.
Now sin is the sting of death, and sin derives its power from the Law;
57 Amma godiya ga Allah! Shi ne ya ba mu nasara ta wurin Ubangijinmu Yesu Kiristi.
but God be thanked who gives us the victory through our Lord Jesus Christ!
58 Saboda haka, ƙaunatattu’yan’uwana, ku tsaya da daram. Kada wani abu yă jijjiga ku. Ku ba da kanku kullum ga aikin Ubangiji, domin kun san cewa famar da kuke yi saboda Ubangiji ba a banza take ba.
Therefore, my dear brethren, be firm, unmovable, busily occupied at all times in the Lord's work, knowing that your toil is not fruitless in the Lord.