< 1 Korintiyawa 14 >
1 Ku bi halin ƙauna kuna kuma marmarin neman baye-bayen ruhaniya, musamman baiwar annabci.
Higer efter Kærligheden, og tragter efter de aandelige Gaver, men mest efter at profetere.
2 Gama duk wanda yake magana da wani harshe ba da mutane yake magana ba, sai dai da Allah. Tabbatacce, ba wanda yake fahimtarsa; yana faɗin asirai ta wurin ruhu ne.
Thi den, som taler i Tunger, taler ikke for Mennesker, men for Gud; thi ingen forstaar det, men han taler Hemmeligheder i Aanden.
3 Amma duk wanda yake annabci, yana magana ne da mutane domin yă gina su, yă ƙarfafa su, yă kuma yi musu ta’aziyya.
Men den, som profeterer, taler Mennesker til Opbyggelse og Formaning og Trøst.
4 Wanda yake magana da wani harshe kuwa, kansa yake gina, amma mai annabci, ikkilisiya ce yake gina.
Den, som taler i Tunger, opbygger sig selv; men den, som profeterer, opbygger en Menighed.
5 Zan so kowannenku yă yi magana da harsuna, sai dai zan fi so ku yi annabci. Wanda yake annabci ya fi wanda yake magana da harsuna, sai dai in ya fassara don ikkilisiya ta ginu.
Men jeg ønsker, at I alle maatte tale i Tunger, men endnu hellere, at I maatte profetere; den, som profeterer, er større end den, som taler i Tunger, med mindre han udlægger det, for at Menigheden kan faa Opbyggelse deraf.
6 To,’yan’uwa, a ce na zo wurinku ina kuma yin magana da waɗansu harsuna, amfanin me zan yi muku in ban zo muku da wani bayani ko sani ko annabci, ko kuma kalmar koyarwa ba?
Men nu, Brødre! dersom jeg kommer til eder og taler i Tunger, hvad vil jeg da gavne eder, hvis jeg ikke taler til eder enten ved Aabenbaring eller ved Kundskab, enten ved Profeti eller ved Lære?
7 Abubuwan nan marasa rai ma da sukan yi ƙara, kamar su algaita ko molo, in muryarsu ba tă fita sosai ba, yaya wani zai san abin da ake busawa ko kaɗawa?
Selv de livløse Ting, som give Lyd, være sig en Fløjte eller en Harpe, naar de ikke gøre Skel imellem Tonerne, hvorledes skal man saa kunne forstaa, hvad der spilles paa Fløjten eller Harpen?
8 Haka ma in ba a busa ƙaho sosai ba, wa zai yi shirin yaƙi?
Ja, ogsaa naar en Basun giver en utydelig Lyd, hvem vil da berede sig til Krig?
9 Haka yake sa’ad da kuka yi magana da waɗansu harsunan da ba a fahimta. In babu wanda zai san abin da kuke faɗi, za ka dai yi wa iska magana ne kawai.
Saaledes ogsaa med eder: dersom I ikke ved Tungen fremføre tydelig Tale, hvorledes skal man da kunne forstaa det, som tales? I ville jo tale hen i Vejret.
10 Ba shakka akwai harsuna iri-iri a duniya, duk da haka kowane a cikinsu yana da ma’ana.
Der er i Verden, lad os sige, saa og saa mange Slags Sprog, og der er intet af dem, som ikke har sin Betydning.
11 To, in ban gane ma’anar abin da wani yake faɗi ba, ni baƙo ne ga mai maganar, shi kuma baƙo ne a gare ni.
Dersom jeg nu ikke kender Sprogets Betydning, bliver jeg en Barbar for den, som taler, og den, som taler, bliver en Barbar for mig.
12 Haka yake a gare ku. Da yake kuna marmarin samun baye-bayen ruhaniya, sai ku ba da ƙarfinku ga yin amfani da waɗanda za su gina ikkilisiya.
Saaledes ogsaa med eder: naar I tragte efter aandelige Gaver, da lad det være til Menighedens Opbyggelse, at I søge at blive rige derpaa!
13 Saboda haka, duk wanda yake magana da harshe, sai yă yi addu’a a yi masa baiwar fassara.
Derfor, den, som taler i Tunger, han bede om, at han maa kunne udlægge det.
14 Gama in na yi addu’a da wani harshe, ruhuna ne yake addu’a, amma tunanina bai amfana kome ba.
Thi dersom jeg taler i Tunger og beder, da beder vel min Aand, men min Forstand er uden Frugt.
15 To, me zan yi? Akwai lokutan da zan yi addu’a da ruhuna; akwai kuma lokutan da zan yi addu’a da hankalina. Wani lokaci ya kamata in yi waƙa da ruhuna, a wani lokacin kuma in yi waƙa da hankalina.
Hvad da? Jeg vil bede med Aanden, men jeg vil ogsaa bede med Forstanden; jeg vil lovsynge med Aanden, men jeg vil ogsaa lovsynge med Forstanden.
16 A cewa waɗansu baƙi suna cikin sujadarku, sa’ad da kuke yabon Allah da ruhunku, yaya waɗanda suke tare ku za su fahimta, har su ce, “Amin,” da yake ba su san abin da kuke faɗi ba?
Ellers, naar du priser Gud i Aanden, hvorledes vil da den, som indtager den uindviedes Plads, kunne sige sit Amen til din Taksigelse, efterdi han ikke ved, hvad du siger?
17 Ko da yake kuna ba da godiya da kyau, amma wancan mutumin da yake tare da ku bai ginu ba.
Thi vel er din Taksigelse smuk, men den anden opbygges ikke.
18 Na gode wa Allah, domin ina magana da harsuna fiye da ku duka.
Jeg takker Gud for, at jeg mere end I alle taler i Tunger.
19 Amma a cikin ikkilisiya zan gwammace in yi magana da kalmomi biyar da za a fahimta don in koyar da waɗansu da a ce in yi magana da kalmomi guda dubu goma a wani harshe.
Men i en Menighed vil jeg hellere tale fem Ord med min Forstand, for at jeg ogsaa kan undervise andre, end ti Tusinde Ord i Tunger.
20 ’Yan’uwa, ku daina tunani kamar yara. Wajen mugunta ku zama jarirai, sai dai wajen tunaninku, ku zama manya.
Brødre! vorder ikke Børn i Forstand, men værer Børn i Ondskab, i Forstand derimod vorder fuldvoksne!
21 A cikin Doka yana a rubuce cewa, “Ta wurin mutane masu baƙin harsuna da kuma ta leɓunan baƙi zan yi magana da waɗannan mutane, amma duk da haka, ba za su saurare ni ba,” in ji Ubangiji.
Der er skrevet i Loven: „Ved Folk med fremmede Tungemaal og ved fremmedes Læber vil jeg tale til dette Folk, og de skulle end ikke saaledes høre mig, siger Herren.‟
22 Harsuna fa alama ce ba ga masu bi ba, sai dai ga marasa bi. Annabci kuwa ga masu bi ne ba ga marasa bi ba.
Saaledes er Tungetalen til et Tegn, ikke for dem, som tro, men for de vantro; men den profetiske Gave er det ikke for de vantro, men for dem, som tro.
23 Saboda haka, in dukan ikkilisiya ta taru, kowa kuma yana magana da waɗansu harsuna, sai waɗansu jahilai ko waɗansu marasa bi suka shigo, ashe, ba za su ce kuna hauka ba?
Naar altsaa den hele Menighed kommer sammen, og alle tale i Tunger, men der kommer uindviede eller vantro ind, ville de da ikke sige, at I rase?
24 Amma in wani marar bi, ko jahili ya shigo sa’ad da kowa yana annabci, sai maganar kowa ta ratsa shi, za su shawo kansa yă gane cewa shi mai zunubi ne saboda abin da kowa yake faɗi,
Men dersom alle profetere, og der kommer nogen vantro eller uindviet ind, da overbevises han af alle, han bedømmes af alle,
25 asirin zuciyarsa kuma su bayyana a fili. Don haka, zai fāɗi a ƙasa yă yi wa Allah sujada yana cewa, “Lalle, Allah yana cikinku!”
hans Hjertes skjulte Tanker aabenbares, og saa vil han falde paa sit Ansigt og tilbede Gud og forkynde, at Gud er virkelig i eder.
26 Me za mu ce ke nan’yan’uwa? Sa’ad da kuka taru, wani yakan yi waƙa, wani koyarwa, wani wahayi, wani yin magana da wani harshe, wani kuma fassara. Dole ne a yi duka don gina ikkilisiya.
Hvad da, Brødre? Naar I komme sammen, da har enhver en Lovsang, en Lære, en Aabenbaring, en Tungetale, en Udlægning; alt ske til Opbyggelse!
27 In kuwa waɗansu za su yi magana a wani harshe, to, kada su fi mutum biyu ko uku, kuma a yi bi da bi, wani kuma yă fassara.
Dersom nogen taler i Tunger, da være det to, eller i det højeste tre hver Gang, og den ene efter den anden, og een udlægge det!
28 In babu mai fassara, sai mai magana yă yi shiru a cikin ikkilisiya, yă yi wa kansa magana da kuma Allah.
Men dersom der ingen Udlægger er til Stede, da tie hin i Menigheden, men han tale for sig selv og for Gud!
29 Annabawa biyu ko uku za su iya yin magana, sauran kuma sai su auna a hankali abin da aka faɗa.
Men af Profeter tale to eller tre, og de andre bedømme det;
30 In kuma wahayi ya zo wa wani da yake zaune, sai mai magana na farko yă yi shiru.
men dersom en anden, som sidder der, faar en Aabenbarelse, da tie den første!
31 Dukanku kuna iya yin annabci bi da bi, domin kowa yă sami koyarwa da ƙarfafawa.
Thi I kunne alle profetere, den ene efter den anden, for at alle kunne lære, og alle blive formanede,
32 Ruhohin annabawa kuwa suna ƙarƙashin sarrafawar annabawa.
og Profeters Aander ere Profeter undergivne.
33 Gama Allah, ba Allah mai sa rikicewa ba ne, sai dai mai salama. Kamar yadda yake a dukan ikkilisiyoyi na tsarkaka.
Thi Gud er ikke Forvirringens, men Fredens Gud. Ligesom i alle de helliges Menigheder
34 Ya kamata mata su zauna shiru a cikin ikkilisiyoyi. Ba su da izinin yin magana, sai dai su yi biyayya yadda Doka ta faɗi.
skulle eders Kvinder tie i Forsamlingerne; thi det tilstedes dem ikke at tale, men lad dem underordne sig, ligesom ogsaa Loven siger.
35 In suna so su yi tambaya game da wani abu, ya kamata su tambayi mazansu a gida, domin abin kunya ne mace tă yi magana a cikin ikkilisiya.
Men ville de lære noget, da adspørge de deres egne Mænd hjemme; thi det er usømmeligt for en Kvinde at tale i en Menighedsforsamling.
36 Shin, a kanku ne maganar Allah ta fara? Ko kuma a gare ku ne kaɗai ta iso?
Eller er det fra eder, at Guds Ord er udgaaet? eller er det til eder alene, at det er kommet?
37 In wani yana tsammani shi annabi ne, ko yana da baiwar ruhaniya, bari yă gane cewa abin da nake rubuta muku umarnin Ubangiji ne.
Dersom nogen tykkes, at han er en Profet eller aandelig, han erkende, at hvad jeg skriver til eder, er Herrens Bud.
38 In ya ƙi kula da wannan, shi ma sai a ƙi kula da shi.
Men er nogen uvidende derom, saa faar han være uvidende!
39 Saboda haka’yan’uwana, ku yi marmarin yin annabci, kada kuma ku hana magana da harsuna.
Altsaa, mine Brødre! tragter efter at profetere og forhindrer ikke Talen i Tunger!
40 Sai dai a yi kome daidai da kuma cikin tsari.
Men alt ske sømmeligt og med Orden!