< 1 Korintiyawa 11 >
1 Ku bi gurbina, kamar yadda ni nake bin gurbin Kiristi.
Soyez mes imitateurs, comme je le suis aussi de Christ.
2 Ina yabonku saboda kuna tunawa da ni a cikin kowane abu, kuna kuma riƙe da koyarwar, yadda na ba ku.
Frères, je vous loue de ce que vous vous souvenez de tout ce qui vient de moi, et de ce que vous retenez mes instructions telles que je vous les ai données.
3 To, ina so ku gane cewa shugaban kowane namiji Kiristi ne, shugaban mace namiji ne, shugaban Kiristi kuma Allah ne.
Mais je veux que vous sachiez que Christ est le Chef de tout homme, et que l'homme est le chef de la femme, et que Dieu est le chef de Christ.
4 Kowane namijin da ya yi addu’a ko annabci da kansa a rufe ya jawo kunya wa kansa.
Tout homme qui prie ou qui prophétise, la tête couverte, déshonore son chef.
5 Duk macen da ta yi addu’a ko annabci da kanta a buɗe kuwa ta rena kanta, ya zama kamar an aske kanta ke nan.
Mais toute femme qui prie ou qui prophétise sans avoir la tête couverte, déshonore son chef; car c'est la même chose que si elle était rasée.
6 In mace ba ta so tă rufe kanta, to, sai tă aske gashinta; in kuwa abin kunya ne mace tă yanke ko tă aske gashinta, to, sai tă rufe kanta.
Que si la femme n'est point couverte, qu'elle se coupe aussi les cheveux. Mais s'il est honteux pour une femme d'avoir les cheveux coupés, ou d'être rasée, qu'elle soit couverte.
7 Namiji kuwa bai kamata ya rufe kansa ba, da yake shi kamannin Allah ne, da kuma darajar Allah, amma mace dai, darajar namiji ne.
Pour ce qui est de l'homme, il ne doit pas se couvrir la tête, puisqu'il est l'image et la gloire de Dieu; mais la femme est la gloire de l'homme.
8 Gama namiji bai fito daga mace ba, sai dai mace ce ta fito daga namiji.
En effet, l'homme n'a pas été pris de la femme, mais la femme a été prise de l'homme;
9 Ba a kuma halicci namiji don mace ba, sai dai mace don namiji.
Et l'homme n'a pas été créé pour la femme, mais la femme a été créée pour l'homme.
10 Don haka, saboda wannan, da kuma saboda mala’iku, dole mace ta ɗaura wani abu a kanta.
C'est pourquoi la femme, à cause des anges, doit avoir sur sa tête une marque de l'autorité sous laquelle elle est.
11 Duk da haka a cikin Ubangiji, mace ba a rabe take da namiji ba, namiji kuma ba a rabe yake da mace ba.
Toutefois, l'homme n'est point sans la femme, ni la femme sans l'homme, dans le Seigneur.
12 Kamar yadda mace ta fito daga namiji, haka kuma aka haifi namiji ta wurin mace. Sai dai kowane abu daga Allah yake.
Car comme la femme a été prise de l'homme, aussi l'homme naît de la femme; et tout vient de Dieu.
13 Ku kanku duba mana. Ya yi kyau mace tă yi addu’a ga Allah da kanta a buɗe?
Jugez-en vous-mêmes; est-il bienséant qu'une femme prie Dieu sans avoir la tête couverte?
14 Kai, yadda halitta take ma, ai, ta koya muku cewa in namiji yana da dogon gashi, abin kunya ne a gare shi,
La nature elle-même ne vous apprend-elle pas qu'il est honteux à l'homme de porter de longs cheveux;
15 amma in mace tana da dogon gashi, ai, daraja ce a gare ta. Gama an ba ta dogon gashi saboda rufe kanta ne.
Mais que si la femme porte de longs cheveux, c'est un honneur pour elle, parce que la chevelure lui est donnée pour voile?
16 In akwai mai gardama da wannan, to, mu dai ba mu da wata al’ada, haka ma ikkilisiyoyin Allah.
Que si quelqu'un se plaît à contester, nous n'avons pas cette coutume, ni les Églises de Dieu non plus.
17 Game da umarnan nan dai, ban yaba muku ba, domin taruwarku ba ta kirki ba ce, ɓarna ce.
Or, en ce que je vais vous dire, je ne vous loue point: c'est que vous vous assemblez, non pour devenir meilleurs, mais pour empirer.
18 Da farko dai, na ji cewa sa’ad da kuka taru a matsayin ikkilisiya, akwai tsattsaguwa a tsakaninku, har na fara yarda da zancen.
Car, premièrement, j'apprends que lorsque vous vous assemblez dans l'Église, il y a des divisions parmi vous, et j'en crois une partie,
19 Ba shakka dole a sami bambanci a tsakaninku don a nuna wa Allah ya amince da shi a cikinku.
Car il faut qu'il y ait des schismes parmi vous, afin que ceux d'entre vous qui sont approuvés, soient manifestés.
20 Sa’ad da kuka taru, ba Cimar Ubangiji kuke ci ba,
Lors donc que vous vous assemblez dans un même lieu, ce n'est pas pour manger la Cène du Seigneur;
21 gama yayinda kuke ci, kowa yakan ci gaba ba tare da jiran wani ba. Wani yă zauna da yunwa, wani kuma yă bugu.
Car au repas, chacun se hâte de prendre son souper particulier; en sorte que l'un a faim, et l'autre est repu.
22 Kai, ba ku da gidajen da za ku ci ku sha ne? Ko dai kun rena ikkilisiyar Allah ne, kuna kuma wulaƙanta waɗanda ba su da kome? Me zan ce muku? In yabe ku ne game da wannan? A’a, ko kaɗan!
N'avez-vous pas des maisons pour manger et pour boire? Ou méprisez-vous l'Église de Dieu, et faites-vous honte à ceux qui n'ont rien? Que vous dirai-je? Vous louerai-je? Je ne vous loue point de cela.
23 Gama abin da na karɓa daga wurin Ubangiji shi ne nake ba ku. Ubangiji Yesu, a daren da aka bashe shi, ya ɗauki burodi,
Car pour moi, j'ai reçu du Seigneur ce que je vous ai aussi enseigné; c'est que le Seigneur Jésus, la nuit qu'il fut livré, prit du pain;
24 bayan ya yi godiya, sai ya kakkarya ya ce, “Wannan jikina ne, wanda yake dominku, ku yi wannan don tunawa da ni.”
Et ayant rendu grâces, il le rompit, et dit: Prenez, mangez; ceci est mon corps, qui est rompu pour vous; faites ceci en mémoire de moi.
25 Haka kuma bayan cimar, ya ɗauki kwaf, yana cewa, “Wannan kwaf ne sabon alkawari a jinina; ku yi wannan, a duk sa’ad da kuke sha, don tunawa da ni.”
De même aussi, après avoir soupé, il prit la coupe, et dit: Cette coupe est la nouvelle alliance en mon sang; faites ceci en mémoire de moi, toutes les fois que vous en boirez.
26 Gama a duk sa’ad da kuke cin wannan burodi, kuke kuma sha daga wannan kwaf, kuna shelar mutuwar Ubangiji ne har yă dawo.
Car toutes les fois que vous mangez de ce pain, et que vous buvez de cette coupe, vous annoncez la mort du Seigneur, jusqu'à ce qu'il vienne.
27 Saboda haka, duk wanda ya ci burodin ko ya sha daga kwaf na Ubangiji da rashin cancanta, ya yi laifin wulaƙanta jiki da jinin Ubangiji ke nan.
C'est pourquoi, quiconque mangera de ce pain, ou boira de la coupe du Seigneur indignement, sera coupable envers le corps et le sang du Seigneur.
28 Dole kowa yă bincike kansa kafin yă ci burodin yă kuma sha daga kwaf ɗin.
Que chacun donc s'éprouve soi-même, et qu'ainsi il mange de ce pain et boive de cette coupe;
29 Gama duk wanda ya ci ya kuma sha ba tare da fahimtar jikin Ubangiji ba, ya ci ya kuma sha wa kansa hukunci ne.
Car celui qui en mange et qui en boit indignement, mange et boit sa condamnation, ne discernant point le corps du Seigneur.
30 Shi ya sa da yawa a cikinku ba su da ƙarfi, suna kuma da rashin lafiya, waɗansunku kuma sun riga sun yi barci.
C'est pour cela qu'il y a parmi vous beaucoup d'infirmes et de malades, et qu'un grand nombre sont morts.
31 Amma in da za mu auna kanmu sosai, da ba za mu shiga irin hukuncin nan ba.
Car si nous nous jugions nous-mêmes, nous ne serions point jugés.
32 Duk da haka sa’ad da Ubangiji ya hukunta mu, ana yin mana horo ne don kada a ƙarshe a hallaka mu tare da duniya.
Mais quand nous sommes jugés, nous sommes châtiés par le Seigneur, afin que nous ne soyons point condamnés avec le monde.
33 Saboda haka’yan’uwana, sa’ad da kuka taru don ci, ku jira juna.
C'est pourquoi, mes frères, quand vous vous assemblez pour manger, attendez-vous les uns les autres.
34 In wani yana jin yunwa, sai yă ci abinci a gida, saboda in kuka taru kada yă jawo hukunci. Sa’ad da na zo kuma zan ba da ƙarin umarnai.
Et si quelqu'un a faim, qu'il mange dans sa maison, afin que vous ne vous assembliez point pour votre condamnation. Quant aux autres choses, je les réglerai quand je serai arrivé.