< 1 Korintiyawa 11 >
1 Ku bi gurbina, kamar yadda ni nake bin gurbin Kiristi.
Be imitators of me, in so far as I in turn am an imitator of Christ.
2 Ina yabonku saboda kuna tunawa da ni a cikin kowane abu, kuna kuma riƙe da koyarwar, yadda na ba ku.
Now I commend you for remembering me in everything, and because you hold fast truths and practices precisely as I have taught them to you.
3 To, ina so ku gane cewa shugaban kowane namiji Kiristi ne, shugaban mace namiji ne, shugaban Kiristi kuma Allah ne.
I would have you know, however, that of every man, Christ is the Head, that of a woman her husband is the Head, and that God is Christ's Head.
4 Kowane namijin da ya yi addu’a ko annabci da kansa a rufe ya jawo kunya wa kansa.
A man who wears a veil when praying or prophesying dishonors his Head;
5 Duk macen da ta yi addu’a ko annabci da kanta a buɗe kuwa ta rena kanta, ya zama kamar an aske kanta ke nan.
but a woman who prays or prophesies with her head uncovered dishonors her Head, for it is exactly the same as if she had her hair cut short.
6 In mace ba ta so tă rufe kanta, to, sai tă aske gashinta; in kuwa abin kunya ne mace tă yanke ko tă aske gashinta, to, sai tă rufe kanta.
If a woman will not wear a veil, let her also cut off her hair. But since it is a dishonor to a woman to have her hair cut off or her head shaved, let her wear a veil.
7 Namiji kuwa bai kamata ya rufe kansa ba, da yake shi kamannin Allah ne, da kuma darajar Allah, amma mace dai, darajar namiji ne.
For a man ought not to have a veil on his head, since he is the image and glory of God; while woman is the glory of man.
8 Gama namiji bai fito daga mace ba, sai dai mace ce ta fito daga namiji.
Man does not take his origin from woman, but woman takes hers from man.
9 Ba a kuma halicci namiji don mace ba, sai dai mace don namiji.
For man was not created for woman's sake, but woman for man's.
10 Don haka, saboda wannan, da kuma saboda mala’iku, dole mace ta ɗaura wani abu a kanta.
That is why a woman ought to have on her head a symbol of subjection, because of the angels.
11 Duk da haka a cikin Ubangiji, mace ba a rabe take da namiji ba, namiji kuma ba a rabe yake da mace ba.
Yet, in the Lord, woman is not independent of man nor man independent of woman.
12 Kamar yadda mace ta fito daga namiji, haka kuma aka haifi namiji ta wurin mace. Sai dai kowane abu daga Allah yake.
For just as woman originates from man, so also man comes into existence through woman, but everything springs originally from God.
13 Ku kanku duba mana. Ya yi kyau mace tă yi addu’a ga Allah da kanta a buɗe?
Judge of this for your own selves: is it seemly for a woman to pray to God when she is unveiled?
14 Kai, yadda halitta take ma, ai, ta koya muku cewa in namiji yana da dogon gashi, abin kunya ne a gare shi,
Does not Nature itself teach you that if a man has long hair it is a dishonor to him,
15 amma in mace tana da dogon gashi, ai, daraja ce a gare ta. Gama an ba ta dogon gashi saboda rufe kanta ne.
but that if a woman has long hair it is her glory, because her hair was given her for a covering?
16 In akwai mai gardama da wannan, to, mu dai ba mu da wata al’ada, haka ma ikkilisiyoyin Allah.
But if any one is inclined to be contentious on the point, we have no such custom, nor have the Churches of God.
17 Game da umarnan nan dai, ban yaba muku ba, domin taruwarku ba ta kirki ba ce, ɓarna ce.
But while giving you these instructions, there is one thing I cannot praise--your meeting together, with bad rather than good results.
18 Da farko dai, na ji cewa sa’ad da kuka taru a matsayin ikkilisiya, akwai tsattsaguwa a tsakaninku, har na fara yarda da zancen.
for, in the first place, when you meet as a Church, there are divisions among you. This is what I am told, and I believe that there is some truth in it.
19 Ba shakka dole a sami bambanci a tsakaninku don a nuna wa Allah ya amince da shi a cikinku.
For there must of necessity be differences of opinion among you, in order that it may be plainly seen who are the men of sterling worth among you.
20 Sa’ad da kuka taru, ba Cimar Ubangiji kuke ci ba,
When, however, you meet in one place, there is no eating the Supper of the Lord;
21 gama yayinda kuke ci, kowa yakan ci gaba ba tare da jiran wani ba. Wani yă zauna da yunwa, wani kuma yă bugu.
for it is his own supper of which each of you is in a hurry to partake, and one eats like a hungry man, while another has already drunk to excess.
22 Kai, ba ku da gidajen da za ku ci ku sha ne? Ko dai kun rena ikkilisiyar Allah ne, kuna kuma wulaƙanta waɗanda ba su da kome? Me zan ce muku? In yabe ku ne game da wannan? A’a, ko kaɗan!
Why, have you no homes in which to eat and drink? Or do you wish to show your contempt for the Church of God and make those who have no homes feel ashamed? What shall I say to you? Shall I praise you? In this matter I certainly do not praise you.
23 Gama abin da na karɓa daga wurin Ubangiji shi ne nake ba ku. Ubangiji Yesu, a daren da aka bashe shi, ya ɗauki burodi,
For it was from the Lord that I received the facts which, in turn, I handed on to you; how that the Lord Jesus, on the night He was to be betrayed, took some bread,
24 bayan ya yi godiya, sai ya kakkarya ya ce, “Wannan jikina ne, wanda yake dominku, ku yi wannan don tunawa da ni.”
and after giving thanks He broke it and said, "This is my body which is about to be broken for you. Do this in memory of me."
25 Haka kuma bayan cimar, ya ɗauki kwaf, yana cewa, “Wannan kwaf ne sabon alkawari a jinina; ku yi wannan, a duk sa’ad da kuke sha, don tunawa da ni.”
In the same way, when the meal was over, He also took the cup. "This cup," He said, "is the new Covenant of which my blood is the pledge. Do this, every time that you drink it, in memory of me."
26 Gama a duk sa’ad da kuke cin wannan burodi, kuke kuma sha daga wannan kwaf, kuna shelar mutuwar Ubangiji ne har yă dawo.
For every time that you eat this bread and drink from the cup, you are proclaiming the Lord's death--until He returns.
27 Saboda haka, duk wanda ya ci burodin ko ya sha daga kwaf na Ubangiji da rashin cancanta, ya yi laifin wulaƙanta jiki da jinin Ubangiji ke nan.
Whoever, therefore, in an unworthy manner, eats the bread or drinks from the cup of the Lord sins against the body and blood of the Lord.
28 Dole kowa yă bincike kansa kafin yă ci burodin yă kuma sha daga kwaf ɗin.
But let a man examine himself, and, having done that, then let him eat the bread and drink from the cup.
29 Gama duk wanda ya ci ya kuma sha ba tare da fahimtar jikin Ubangiji ba, ya ci ya kuma sha wa kansa hukunci ne.
For any one who eats and drinks, eats and drinks judgement to himself, if he fails to estimate the body aright.
30 Shi ya sa da yawa a cikinku ba su da ƙarfi, suna kuma da rashin lafiya, waɗansunku kuma sun riga sun yi barci.
That is why many among you are sickly and out of health, and why not a few die.
31 Amma in da za mu auna kanmu sosai, da ba za mu shiga irin hukuncin nan ba.
If, however, we estimated ourselves aright, we should not be judged.
32 Duk da haka sa’ad da Ubangiji ya hukunta mu, ana yin mana horo ne don kada a ƙarshe a hallaka mu tare da duniya.
But when we are judged by the Lord, chastisement follows, to save us from being condemned along with the world.
33 Saboda haka’yan’uwana, sa’ad da kuka taru don ci, ku jira juna.
Therefore, brethren, when you come together for this meal, wait for one another.
34 In wani yana jin yunwa, sai yă ci abinci a gida, saboda in kuka taru kada yă jawo hukunci. Sa’ad da na zo kuma zan ba da ƙarin umarnai.
If any one is hungry, let him eat at home; so that your coming together may not lead to judgement. The other matters I will deal with whenever I come.