< 1 Korintiyawa 11 >

1 Ku bi gurbina, kamar yadda ni nake bin gurbin Kiristi.
Be ye imitators of me, as I am of the Messiah.
2 Ina yabonku saboda kuna tunawa da ni a cikin kowane abu, kuna kuma riƙe da koyarwar, yadda na ba ku.
Moreover I commend you, my Brethren, that in all things ye are mindful of me, and that ye hold fast the precepts as I delivered them to you.
3 To, ina so ku gane cewa shugaban kowane namiji Kiristi ne, shugaban mace namiji ne, shugaban Kiristi kuma Allah ne.
And I would have you know, that the head of every man is the Messiah, and the head of the woman is the man, and the head of the Messiah is God.
4 Kowane namijin da ya yi addu’a ko annabci da kansa a rufe ya jawo kunya wa kansa.
Every man, who prayeth or prophesieth with his head covered, dishonoreth his head.
5 Duk macen da ta yi addu’a ko annabci da kanta a buɗe kuwa ta rena kanta, ya zama kamar an aske kanta ke nan.
And every woman, who prayeth or prophesieth with her head uncovered, dishonoreth her head; for she is on a level with her whose head is shaven.
6 In mace ba ta so tă rufe kanta, to, sai tă aske gashinta; in kuwa abin kunya ne mace tă yanke ko tă aske gashinta, to, sai tă rufe kanta.
For if a woman be not covered, let her also be shorn; but if it be shameful for a woman to be shorn or shaven, let her be covered.
7 Namiji kuwa bai kamata ya rufe kansa ba, da yake shi kamannin Allah ne, da kuma darajar Allah, amma mace dai, darajar namiji ne.
The man, indeed, ought not to cover his head, because he is the likeness and glory of God: but the woman is the glory of the man.
8 Gama namiji bai fito daga mace ba, sai dai mace ce ta fito daga namiji.
For the man was not from the woman, but the woman from the man.
9 Ba a kuma halicci namiji don mace ba, sai dai mace don namiji.
Neither was the man created for the woman's sake, but the woman for the man's sake.
10 Don haka, saboda wannan, da kuma saboda mala’iku, dole mace ta ɗaura wani abu a kanta.
For this cause ought the woman to have on her head the mark of authority, because of the angels.
11 Duk da haka a cikin Ubangiji, mace ba a rabe take da namiji ba, namiji kuma ba a rabe yake da mace ba.
Nevertheless, the man is not without the woman, nor the woman without the man, in our Lord.
12 Kamar yadda mace ta fito daga namiji, haka kuma aka haifi namiji ta wurin mace. Sai dai kowane abu daga Allah yake.
For as the woman was from the man, so the man is by the woman; and every thing is from God.
13 Ku kanku duba mana. Ya yi kyau mace tă yi addu’a ga Allah da kanta a buɗe?
Judge for yourselves, among yourselves; is it becoming, that a woman pray to God with her head uncovered?
14 Kai, yadda halitta take ma, ai, ta koya muku cewa in namiji yana da dogon gashi, abin kunya ne a gare shi,
Doth not nature teach you, that in a man, if his hair groweth long, it is a reproach to him?
15 amma in mace tana da dogon gashi, ai, daraja ce a gare ta. Gama an ba ta dogon gashi saboda rufe kanta ne.
But for a woman, if her hair is abundant, it is a glory to her; for her hair is given to her for a covering.
16 In akwai mai gardama da wannan, to, mu dai ba mu da wata al’ada, haka ma ikkilisiyoyin Allah.
But if any one is contentious about these things, we on our part have no such custom, nor hath the church of God.
17 Game da umarnan nan dai, ban yaba muku ba, domin taruwarku ba ta kirki ba ce, ɓarna ce.
This which I now enjoin, is not as praising you; for ye have not made progress, but have deteriorated.
18 Da farko dai, na ji cewa sa’ad da kuka taru a matsayin ikkilisiya, akwai tsattsaguwa a tsakaninku, har na fara yarda da zancen.
Because, first; when ye assemble in the church, there are, I hear, divisions among you; and I partly believe it.
19 Ba shakka dole a sami bambanci a tsakaninku don a nuna wa Allah ya amince da shi a cikinku.
For there are to be contentions among you, that the approved among you may be known.
20 Sa’ad da kuka taru, ba Cimar Ubangiji kuke ci ba,
When therefore ye come together, ye eat and drink, not as is becoming on the day of our Lord.
21 gama yayinda kuke ci, kowa yakan ci gaba ba tare da jiran wani ba. Wani yă zauna da yunwa, wani kuma yă bugu.
But, one and another proceedeth to eat his own supper; and one is hungry, and another is drunken.
22 Kai, ba ku da gidajen da za ku ci ku sha ne? Ko dai kun rena ikkilisiyar Allah ne, kuna kuma wulaƙanta waɗanda ba su da kome? Me zan ce muku? In yabe ku ne game da wannan? A’a, ko kaɗan!
What! have ye no houses in which ye can eat and drink? Or, despise ye the church of God, and shame them who have nothing? What shall I say to you? Shall I praise you? In this I praise you not.
23 Gama abin da na karɓa daga wurin Ubangiji shi ne nake ba ku. Ubangiji Yesu, a daren da aka bashe shi, ya ɗauki burodi,
For I have received from our Lord, that which I imparted to you; that our Lord Jesus, on the night he was betrayed, took bread,
24 bayan ya yi godiya, sai ya kakkarya ya ce, “Wannan jikina ne, wanda yake dominku, ku yi wannan don tunawa da ni.”
and blessed, and brake it, and said: " Take, eat; this is my body, which is broken for your sakes: thus do ye, in remembrance of me."
25 Haka kuma bayan cimar, ya ɗauki kwaf, yana cewa, “Wannan kwaf ne sabon alkawari a jinina; ku yi wannan, a duk sa’ad da kuke sha, don tunawa da ni.”
So, after they had supped, he gave also the cup, and said: " This cup is the new testament in my blood: thus do ye, as often as ye drink it, in remembrance of me."
26 Gama a duk sa’ad da kuke cin wannan burodi, kuke kuma sha daga wannan kwaf, kuna shelar mutuwar Ubangiji ne har yă dawo.
For as often as ye eat this bread, and drink this cup, ye commemorate the death of our Lord, until his advent.
27 Saboda haka, duk wanda ya ci burodin ko ya sha daga kwaf na Ubangiji da rashin cancanta, ya yi laifin wulaƙanta jiki da jinin Ubangiji ke nan.
He therefore, who eateth of the bread of the Lord, and drinketh of his cup, and is not worthy of it, is guilty of the blood of the Lord, and of his body.
28 Dole kowa yă bincike kansa kafin yă ci burodin yă kuma sha daga kwaf ɗin.
For this reason, a man should examine himself, and then eat of this bread, and drink of this cup:
29 Gama duk wanda ya ci ya kuma sha ba tare da fahimtar jikin Ubangiji ba, ya ci ya kuma sha wa kansa hukunci ne.
for, whoever eateth and drinketh of it, while he is unworthy, eateth and drinketh condemnation on himself, by not discerning the body of the Lord.
30 Shi ya sa da yawa a cikinku ba su da ƙarfi, suna kuma da rashin lafiya, waɗansunku kuma sun riga sun yi barci.
For this cause, many among you are diseased and sickly, and many sleep.
31 Amma in da za mu auna kanmu sosai, da ba za mu shiga irin hukuncin nan ba.
For if we would judge ourselves, we should not be judged.
32 Duk da haka sa’ad da Ubangiji ya hukunta mu, ana yin mana horo ne don kada a ƙarshe a hallaka mu tare da duniya.
But when we are judged by our Lord, we are really chastised, that we may not be condemned with the world.
33 Saboda haka’yan’uwana, sa’ad da kuka taru don ci, ku jira juna.
Wherefore, my Brethren, when ye assemble to eat, wait ye one for another.
34 In wani yana jin yunwa, sai yă ci abinci a gida, saboda in kuka taru kada yă jawo hukunci. Sa’ad da na zo kuma zan ba da ƙarin umarnai.
And let him who is hungry, eat at home; that ye may assemble, not for condemnation. And as to other things, I will give you directions when I come.

< 1 Korintiyawa 11 >