< 1 Korintiyawa 11 >
1 Ku bi gurbina, kamar yadda ni nake bin gurbin Kiristi.
Become imitators of me, —even as, I also, [am] of Christ.
2 Ina yabonku saboda kuna tunawa da ni a cikin kowane abu, kuna kuma riƙe da koyarwar, yadda na ba ku.
Now I praise you, that, in all things, ye have me in remembrance, and, even as I delivered unto you the instructions, ye hold them fast.
3 To, ina so ku gane cewa shugaban kowane namiji Kiristi ne, shugaban mace namiji ne, shugaban Kiristi kuma Allah ne.
But I wish you to know—that, the head of every man, is, the Christ, and, the head of a woman, is, the man; and, the head of the Christ, is, God.
4 Kowane namijin da ya yi addu’a ko annabci da kansa a rufe ya jawo kunya wa kansa.
Every man, praying, or prophesying, having anything upon his head, putteth to shame his head;
5 Duk macen da ta yi addu’a ko annabci da kanta a buɗe kuwa ta rena kanta, ya zama kamar an aske kanta ke nan.
But, every woman, praying, or prophesying, with her head, unveiled, putteth to shame her head, —for it is, one and the same, with her having been shaven.
6 In mace ba ta so tă rufe kanta, to, sai tă aske gashinta; in kuwa abin kunya ne mace tă yanke ko tă aske gashinta, to, sai tă rufe kanta.
For, if a woman doth not veil herself, let her also be shorn; but, if it were a shame in a woman to be shorn or shaven, let her be veiled.
7 Namiji kuwa bai kamata ya rufe kansa ba, da yake shi kamannin Allah ne, da kuma darajar Allah, amma mace dai, darajar namiji ne.
For, a man, indeed, ought not to be veiling his head, being, the image and glory of God, —but, the woman, is the glory of man;
8 Gama namiji bai fito daga mace ba, sai dai mace ce ta fito daga namiji.
For, man, is not, of woman, but, woman, of man;
9 Ba a kuma halicci namiji don mace ba, sai dai mace don namiji.
For also man was not created, for the sake of the woman, but woman, for the sake of the man.
10 Don haka, saboda wannan, da kuma saboda mala’iku, dole mace ta ɗaura wani abu a kanta.
For this cause, ought the woman to have, permission, upon her head, because of the messengers.
11 Duk da haka a cikin Ubangiji, mace ba a rabe take da namiji ba, namiji kuma ba a rabe yake da mace ba.
Howbeit, neither is woman apart from man, nor man apart from woman—in the Lord;
12 Kamar yadda mace ta fito daga namiji, haka kuma aka haifi namiji ta wurin mace. Sai dai kowane abu daga Allah yake.
For, just as the woman is of the man, so, also the man, is through means of the woman; —but, all things, are of God.
13 Ku kanku duba mana. Ya yi kyau mace tă yi addu’a ga Allah da kanta a buɗe?
Among your own selves, judge ye, —Is it becoming for a woman, —unveiled, to be praying unto God?
14 Kai, yadda halitta take ma, ai, ta koya muku cewa in namiji yana da dogon gashi, abin kunya ne a gare shi,
Doth not, even nature herself, teach you—that, if, a man, have long hair, it is a dishonour to him;
15 amma in mace tana da dogon gashi, ai, daraja ce a gare ta. Gama an ba ta dogon gashi saboda rufe kanta ne.
But, if, a woman, have long hair, it is a glory to her, for, her long hair, instead of a veil, hath been given to her.
16 In akwai mai gardama da wannan, to, mu dai ba mu da wata al’ada, haka ma ikkilisiyoyin Allah.
But, if anyone thinketh to be contentious, we, have no such custom, —nor yet the assemblies of God.
17 Game da umarnan nan dai, ban yaba muku ba, domin taruwarku ba ta kirki ba ce, ɓarna ce.
But, in giving you the following charge, I praise you not, —in that, not for the better, but for the worse, ye come together.
18 Da farko dai, na ji cewa sa’ad da kuka taru a matsayin ikkilisiya, akwai tsattsaguwa a tsakaninku, har na fara yarda da zancen.
For, first of all, —when ye come together in assembly, I hear that divisions among you exist, —and, in part, I believe it;
19 Ba shakka dole a sami bambanci a tsakaninku don a nuna wa Allah ya amince da shi a cikinku.
For there must needs be, even parties among you, that, the approved, [themselves] may become manifest among you.
20 Sa’ad da kuka taru, ba Cimar Ubangiji kuke ci ba,
When, therefore, ye come together into one place, it is not to eat, a supper unto the Lord;
21 gama yayinda kuke ci, kowa yakan ci gaba ba tare da jiran wani ba. Wani yă zauna da yunwa, wani kuma yă bugu.
For, each one, taketh beforehand, his own supper, in your eating, and, one, indeed, is hungry, whereas, another, is drinking to excess.
22 Kai, ba ku da gidajen da za ku ci ku sha ne? Ko dai kun rena ikkilisiyar Allah ne, kuna kuma wulaƙanta waɗanda ba su da kome? Me zan ce muku? In yabe ku ne game da wannan? A’a, ko kaɗan!
What! have ye not houses for your eating and drinking? or, the assembly of God, do ye despise, and, put to shame them who have nothing? What am I to say to you? Shall I praise you? In this, I praise you not.
23 Gama abin da na karɓa daga wurin Ubangiji shi ne nake ba ku. Ubangiji Yesu, a daren da aka bashe shi, ya ɗauki burodi,
For, I myself, received from the Lord—that which I also delivered unto you, —how that, the Lord Jesus, in the night in which he was being delivered up, took a loaf,
24 bayan ya yi godiya, sai ya kakkarya ya ce, “Wannan jikina ne, wanda yake dominku, ku yi wannan don tunawa da ni.”
And, giving thanks, brake it, and said—This, is my body, which is for you, —this, do ye, in remembrance of me;
25 Haka kuma bayan cimar, ya ɗauki kwaf, yana cewa, “Wannan kwaf ne sabon alkawari a jinina; ku yi wannan, a duk sa’ad da kuke sha, don tunawa da ni.”
In the same manner, the cup also, after they had taken supper, saying—This cup, is, the new covenant in my blood, this, do ye, as often soever as ye may be drinking it, in remembrance of me.
26 Gama a duk sa’ad da kuke cin wannan burodi, kuke kuma sha daga wannan kwaf, kuna shelar mutuwar Ubangiji ne har yă dawo.
For, as often as ye may be eating this loaf, and, the cup, may be drinking, The death of the Lord, do ye announce, until he come.
27 Saboda haka, duk wanda ya ci burodin ko ya sha daga kwaf na Ubangiji da rashin cancanta, ya yi laifin wulaƙanta jiki da jinin Ubangiji ke nan.
So that, whosoever may be eating the loaf, or drinking the cup of the Lord, in an unworthy manner, shall be responsible for the body and blood of the Lord.
28 Dole kowa yă bincike kansa kafin yă ci burodin yă kuma sha daga kwaf ɗin.
But let a man be proving himself, —and, so, of the loaf, let him eat, and, of the cup, let him drink;
29 Gama duk wanda ya ci ya kuma sha ba tare da fahimtar jikin Ubangiji ba, ya ci ya kuma sha wa kansa hukunci ne.
For, he that is eating and drinking, —judgment unto himself, doth eat and drink, —if he be not setting apart the body.
30 Shi ya sa da yawa a cikinku ba su da ƙarfi, suna kuma da rashin lafiya, waɗansunku kuma sun riga sun yi barci.
For this cause, many among you are weak and sickly; and, not a few, are falling asleep.
31 Amma in da za mu auna kanmu sosai, da ba za mu shiga irin hukuncin nan ba.
If, however, we had been setting, ourselves, apart, we had not, in that case, been coming under judgment;
32 Duk da haka sa’ad da Ubangiji ya hukunta mu, ana yin mana horo ne don kada a ƙarshe a hallaka mu tare da duniya.
But, being brought under judgment, by the Lord, are we being disciplined, lest, with the world, we should be condemned.
33 Saboda haka’yan’uwana, sa’ad da kuka taru don ci, ku jira juna.
So then, my brethren, —when ye come together for the eating, unto one another, be giving welcome: —
34 In wani yana jin yunwa, sai yă ci abinci a gida, saboda in kuka taru kada yă jawo hukunci. Sa’ad da na zo kuma zan ba da ƙarin umarnai.
If anyone be hungry, at home, let him eat, lest, unto judgment, ye be coming together. And, the remaining things, whensoever I come, I will set in order.