< 1 Korintiyawa 10 >

1 Ba na so ku kasance da rashin sani,’yan’uwa, cewa dukan kakannin-kakanninmu sun yi tafiya a ƙarƙashin girgije, dukansu kuma suka bi ta tsakiyar teku.
he bhrAtaraH, asmatpitR^ipuruShAnadhi yUyaM yadaj nAtA na tiShThateti mama vA nChA, te sarvve meghAdhaHsthitA babhUvuH sarvve samudramadhyena vavrajuH,
2 An yi wa dukansu baftisma ga bin Musa a cikin girgije da kuma cikin teku.
sarvve mUsAmuddishya meghasamudrayo rmajjitA babhUvuH
3 Dukansu sun ci abincin ruhaniya guda
sarvva ekam AtmikaM bhakShyaM bubhujira ekam AtmikaM peyaM papushcha
4 suka kuma sha ruwan ruhaniyan nan guda; gama sun sha daga dutsen ruhaniya nan, wanda ya yi tafiya tare da su, wannan dutsen kuwa Kiristi ne.
yataste. anucharata AtmikAd achalAt labdhaM toyaM papuH so. achalaH khrIShTaeva|
5 Duk da haka, Allah bai ji daɗin yawancinsu ba; gawawwakinsu kuwa suka bazu ko’ina a cikin hamada.
tathA satyapi teShAM madhye. adhikeShu lokeShvIshvaro na santutoSheti hetoste prantare nipAtitAH|
6 To, waɗannan abubuwa misalai ne a gare mu, kada mu yi marmarin mugayen abubuwa, kamar yadda suka yi.
etasmin te. asmAkaM nidarshanasvarUpA babhUvuH; ataste yathA kutsitAbhilAShiNo babhUvurasmAbhistathA kutsitAbhilAShibhi rna bhavitavyaM|
7 Kada ku zama masu bautar gumaka, yadda waɗansunsu suka zama; kamar yadda yake a rubuce cewa, “Mutanen suka zauna don su ci su kuma sha, suka kuma tashi suka shiga rawa ta rashin kunya.”
likhitamAste, lokA bhoktuM pAtu nchopavivishustataH krIDitumutthitA itayanena prakAreNa teShAM kaishchid yadvad devapUjA kR^itA yuShmAbhistadvat na kriyatAM|
8 Kada fa mu yi fasikanci yadda waɗansunsu suka yi, har a rana guda mutane dubu ashirin da uku a cikinsu suka mutu.
aparaM teShAM kaishchid yadvad vyabhichAraH kR^itastena chaikasmin dine trayoviMshatisahasrANi lokA nipAtitAstadvad asmAbhi rvyabhichAro na karttavyaH|
9 Kada mu gwada Kiristi yadda waɗansunsu suka yi, har macizai suka kakkashe su.
teShAM kechid yadvat khrIShTaM parIkShitavantastasmAd bhuja Ngai rnaShTAshcha tadvad asmAbhiH khrIShTo na parIkShitavyaH|
10 Kada kuma ku yi gunaguni yadda waɗansunsu suka yi, har mala’ika mai hallakarwa ya hallaka su.
teShAM kechid yathA vAkkalahaM kR^itavantastatkAraNAt hantrA vinAshitAshcha yuShmAbhistadvad vAkkalaho na kriyatAM|
11 Waɗannnan abubuwa sun same su ne, domin su zama abubuwan koyi, aka kuma rubuta su domin a gargaɗe mu, mu da ƙarshen zamani ya zo mana. (aiōn g165)
tAn prati yAnyetAni jaghaTire tAnyasmAkaM nidarshanAni jagataH sheShayuge varttamAnAnAm asmAkaM shikShArthaM likhitAni cha babhUvuH| (aiōn g165)
12 Saboda haka in kana tsammani kana tsaye ne, to, ka yi hankali kada ka fāɗi!
ataeva yaH kashchid susthiraMmanyaH sa yanna patet tatra sAvadhAno bhavatu|
13 Ba jarrabar da ta taɓa samunku, wadda ba a saba yi wa mutum ba. Allah mai aminci ne; ba zai bari a jarrabce ku fiye da ƙarfinku ba. Amma in aka jarrabce ku, zai nuna muku mafita, domin ku iya cin nasara.
mAnuShikaparIkShAtiriktA kApi parIkShA yuShmAn nAkrAmat, Ishvarashcha vishvAsyaH so. atishaktyAM parIkShAyAM patanAt yuShmAn rakShiShyati, parIkShA cha yad yuShmAbhiH soDhuM shakyate tadarthaM tayA saha nistArasya panthAnaM nirUpayiShyati|
14 Saboda haka abokaina ƙaunatattu, ku guje wa bautar gumaka.
he priyabhrAtaraH, devapUjAto dUram apasarata|
15 Ina magana da ku a kan ku mutane ne fa masu azanci; ku duba da kanku ku ga abin da nake faɗa.
ahaM yuShmAn vij nAn matvA prabhAShe mayA yat kathyate tad yuShmAbhi rvivichyatAM|
16 Kwaf nan na godiya da muke yin godiya da shi, ashe ba tarayya ce a cikin jinin Kiristi ba? Wannan burodi kuma da muke karya mu ci, ashe, ba tarayya ne a cikin jikin Kiristi ba?
yad dhanyavAdapAtram asmAbhi rdhanyaM gadyate tat kiM khrIShTasya shoNitasya sahabhAgitvaM nahi? yashcha pUpo. asmAbhi rbhajyate sa kiM khrIShTasya vapuShaH sahabhAgitvaM nahi?
17 Da yake burodin nan ɗaya ne, ashe kuwa, mu da muke da yawa jiki ɗaya ne, gama dukanmu muna ci daga burodi nan guda.
vayaM bahavaH santo. apyekapUpasvarUpA ekavapuHsvarUpAshcha bhavAmaH, yato vayaM sarvva ekapUpasya sahabhAginaH|
18 Ku dubi mutanen Isra’ila mana. Ashe, waɗanda suke cin hadayu, ba ɗaya suke da juna cikin cin hadayun da aka miƙa a bagade ba?
yUyaM shArIrikam isrAyelIyavaMshaM nirIkShadhvaM| ye balInAM mAMsAni bhu njate te kiM yaj navedyAH sahabhAgino na bhavanti?
19 To, me kuke tsammani nake nufi a nan? Hadayar da aka miƙa wa gunki ce wani abu, ko kuma gunkin ne wani abu?
ityanena mayA kiM kathyate? devatA vAstavikI devatAyai balidAnaM vA vAstavikaM kiM bhavet?
20 A’a, ina nufin akan miƙa hadayun da masu bautar gumaka suka wa aljanu ne, ba Allah ba. Ba na so ku zama ɗaya da aljanu.
tannahi kintu bhinnajAtibhi rye balayo dIyante ta IshvarAya tannahi bhUtebhyaeva dIyante tasmAd yUyaM yad bhUtAnAM sahabhAgino bhavathetyahaM nAbhilaShAmi|
21 Ba zai yiwu ku sha daga kwaf na Ubangiji ku kuma sha daga kwaf na aljanu ba, ba ya yiwuwa ku ci a teburin Ubangiji, ku kuma ci a teburin aljanu.
prabhoH kaMsena bhUtAnAmapi kaMsena pAnaM yuShmAbhirasAdhyaM; yUyaM prabho rbhojyasya bhUtAnAmapi bhojyasya sahabhAgino bhavituM na shaknutha|
22 Ashe, so muke mu tsokani Ubangiji ya yi kishi? Mun fi shi ƙarfi ne?
vayaM kiM prabhuM sparddhiShyAmahe? vayaM kiM tasmAd balavantaH?
23 “Ana da dama a yi kome” sai dai ba kome ba ne yake da amfani. “Ana da dama a yi kome” sai dai ba kome ba ne mai ginawa.
mAM prati sarvvaM karmmApratiShiddhaM kintu na sarvvaM hitajanakaM sarvvam apratiShiddhaM kintu na sarvvaM niShThAjanakaM|
24 Kada wani yă kula da kansa kawai, sai dai yă kula da waɗansu kuma.
AtmahitaH kenApi na cheShTitavyaH kintu sarvvaiH parahitashcheShTitavyaH|
25 Ku ci kowane abin da ake sayarwa a kasuwar nama ba sai kun tambaya ba don kada lamiri yă damu da inda abin ya fito,
ApaNe yat krayyaM tad yuShmAbhiH saMvedasyArthaM kimapi na pR^iShTvA bhujyatAM
26 gama “Duniya da duk abin da yake cikinta na Ubangiji ne.”
yataH pR^ithivI tanmadhyastha ncha sarvvaM parameshvarasya|
27 In wani marar bi ya gayyace ku cin abinci kuka kuwa yarda ku je, sai ku ci ko mene ne da aka sa a gabanku, ba tare da tambaya don kada lamiri yă damu da inda abin ya fito.
aparam avishvAsilokAnAM kenachit nimantritA yUyaM yadi tatra jigamiShatha tarhi tena yad yad upasthApyate tad yuShmAbhiH saMvedasyArthaM kimapi na pR^iShTvA bhujyatAM|
28 Sai dai in wani ya ce muku, “Ai, wannan an miƙa ne wa gunki,” to, kada ku ci, saboda duban mutuncin wannan da ya gaya muku, don kuma lamiri yă kasance babu laifi
kintu tatra yadi kashchid yuShmAn vadet bhakShyametad devatAyAH prasAda iti tarhi tasya j nApayituranurodhAt saMvedasyArtha ncha tad yuShmAbhi rna bhoktavyaM| pR^ithivI tanmadhyastha ncha sarvvaM parameshvarasya,
29 ina nufin lamirin wancan mutum ne fa, ba naku ba. Don me lamirin wani zai shari’anta’yancina?
satyametat, kintu mayA yaH saMvedo nirddishyate sa tava nahi parasyaiva|
30 In na ci abinci da godiya, don me za a zarge ni a kan abin da na ci da godiya ga Allah?
anugrahapAtreNa mayA dhanyavAdaM kR^itvA yad bhujyate tatkAraNAd ahaM kuto nindiShye?
31 Saboda haka, duk abin da kuke yi, ko ci ko sha, ku yi shi duka saboda ɗaukakar Allah.
tasmAd bhojanaM pAnam anyadvA karmma kurvvadbhi ryuShmAbhiH sarvvameveshvarasya mahimnaH prakAshArthaM kriyatAM|
32 Kada ku sa wani yă yi tuntuɓe, ko mutumin Yahuda ne, ko mutumin Al’ummai ko kuma ikkilisiyar Allah
yihUdIyAnAM bhinnajAtIyAnAm Ishvarasya samAjasya vA vighnajanakai ryuShmAbhi rna bhavitavyaM|
33 kamar dai yadda nake ƙoƙarin faranta wa kowa rai, ta kowace hanya. Gama ba don kaina kaɗai nake yi ba, sai dai don amfanin mutane da yawa, don su sami ceto.
ahamapyAtmahitam acheShTamAno bahUnAM paritrANArthaM teShAM hitaM cheShTamAnaH sarvvaviShaye sarvveShAM tuShTikaro bhavAmItyanenAhaM yadvat khrIShTasyAnugAmI tadvad yUyaM mamAnugAmino bhavata|

< 1 Korintiyawa 10 >