< 1 Korintiyawa 10 >

1 Ba na so ku kasance da rashin sani,’yan’uwa, cewa dukan kakannin-kakanninmu sun yi tafiya a ƙarƙashin girgije, dukansu kuma suka bi ta tsakiyar teku.
Δεν θέλω δε να αγνοήτε, αδελφοί, ότι οι πατέρες ημών ήσαν πάντες υπό την νεφέλην, και πάντες διά της θαλάσσης διήλθον,
2 An yi wa dukansu baftisma ga bin Musa a cikin girgije da kuma cikin teku.
και πάντες εις τον Μωϋσήν εβαπτίσθησαν εν τη νεφέλη και εν τη θαλάσση,
3 Dukansu sun ci abincin ruhaniya guda
και πάντες την αυτήν πνευματικήν βρώσιν έφαγον,
4 suka kuma sha ruwan ruhaniyan nan guda; gama sun sha daga dutsen ruhaniya nan, wanda ya yi tafiya tare da su, wannan dutsen kuwa Kiristi ne.
και πάντες το αυτό πνευματικόν ποτόν έπιον· διότι έπινον από πνευματικής πέτρας ακολουθούσης, η δε πέτρα ήτο ο Χριστός·
5 Duk da haka, Allah bai ji daɗin yawancinsu ba; gawawwakinsu kuwa suka bazu ko’ina a cikin hamada.
αλλά δεν ευηρεστήθη ο Θεός εις τους πλειοτέρους εξ αυτών· διότι κατεστρώθησαν εν τη ερήμω.
6 To, waɗannan abubuwa misalai ne a gare mu, kada mu yi marmarin mugayen abubuwa, kamar yadda suka yi.
Ταύτα δε έγειναν παραδείγματα ημών, διά να μη ήμεθα ημείς επιθυμηταί κακών, καθώς και εκείνοι επεθύμησαν.
7 Kada ku zama masu bautar gumaka, yadda waɗansunsu suka zama; kamar yadda yake a rubuce cewa, “Mutanen suka zauna don su ci su kuma sha, suka kuma tashi suka shiga rawa ta rashin kunya.”
Μηδέ γίνεσθε ειδωλολάτραι, καθώς τινές εξ αυτών, ως είναι γεγραμμένον· Εκάθησεν ο λαός διά να φάγη και να πίη, και εσηκώθησαν να παίζωσι.
8 Kada fa mu yi fasikanci yadda waɗansunsu suka yi, har a rana guda mutane dubu ashirin da uku a cikinsu suka mutu.
Μηδέ ας πορνεύωμεν, καθώς τινές αυτών επόρνευσαν και έπεσον εν μιά ημέρα εικοσιτρείς χιλιάδες.
9 Kada mu gwada Kiristi yadda waɗansunsu suka yi, har macizai suka kakkashe su.
Μηδέ ας πειράζωμεν τον Χριστόν, καθώς και τινές αυτών επείρασαν και απωλέσθησαν υπό των όφεων.
10 Kada kuma ku yi gunaguni yadda waɗansunsu suka yi, har mala’ika mai hallakarwa ya hallaka su.
Μηδέ γογγύζετε, καθώς και τινές αυτών εγόγγυσαν, και απωλέσθησαν υπό του εξολοθρευτού.
11 Waɗannnan abubuwa sun same su ne, domin su zama abubuwan koyi, aka kuma rubuta su domin a gargaɗe mu, mu da ƙarshen zamani ya zo mana. (aiōn g165)
Ταύτα δε πάντα εγίνοντο εις εκείνους παραδείγματα, και εγράφησαν προς νουθεσίαν ημών, εις τους οποίους τα τέλη των αιώνων έφθασαν. (aiōn g165)
12 Saboda haka in kana tsammani kana tsaye ne, to, ka yi hankali kada ka fāɗi!
Ώστε ο νομίζων ότι ίσταται ας βλέπη μη πέση.
13 Ba jarrabar da ta taɓa samunku, wadda ba a saba yi wa mutum ba. Allah mai aminci ne; ba zai bari a jarrabce ku fiye da ƙarfinku ba. Amma in aka jarrabce ku, zai nuna muku mafita, domin ku iya cin nasara.
Πειρασμός δεν σας κατέλαβεν ειμή ανθρώπινος· πιστός όμως είναι ο Θεός, όστις δεν θέλει σας αφήσει να πειρασθήτε υπέρ την δύναμίν σας, αλλά μετά του πειρασμού θέλει κάμει και την έκβασιν, ώστε να δύνασθε να υποφέρητε.
14 Saboda haka abokaina ƙaunatattu, ku guje wa bautar gumaka.
Διά τούτο, αγαπητοί μου, φεύγετε από της ειδωλολατρείας.
15 Ina magana da ku a kan ku mutane ne fa masu azanci; ku duba da kanku ku ga abin da nake faɗa.
Λέγω ως προς φρονίμους· κρίνατε σεις τούτο το οποίον λέγω·
16 Kwaf nan na godiya da muke yin godiya da shi, ashe ba tarayya ce a cikin jinin Kiristi ba? Wannan burodi kuma da muke karya mu ci, ashe, ba tarayya ne a cikin jikin Kiristi ba?
Το ποτήριον της ευλογίας, το οποίον ευλογούμεν, δεν είναι κοινωνία του αίματος του Χριστού; Ο άρτος, τον οποίον κόπτομεν, δεν είναι κοινωνία του σώματος του Χριστού;
17 Da yake burodin nan ɗaya ne, ashe kuwa, mu da muke da yawa jiki ɗaya ne, gama dukanmu muna ci daga burodi nan guda.
διότι εις άρτος, εν σώμα είμεθα οι πολλοί· επειδή πάντες εκ του ενός άρτου μετέχομεν.
18 Ku dubi mutanen Isra’ila mana. Ashe, waɗanda suke cin hadayu, ba ɗaya suke da juna cikin cin hadayun da aka miƙa a bagade ba?
Βλέπετε τον Ισραήλ κατά σάρκα· οι τρώγοντες τας θυσίας δεν είναι κοινωνοί του θυσιαστηρίου;
19 To, me kuke tsammani nake nufi a nan? Hadayar da aka miƙa wa gunki ce wani abu, ko kuma gunkin ne wani abu?
Τι λοιπόν λέγω; ότι το είδωλον είναι τι; ή ότι το ειδωλόθυτον είναι τι; ουχί·
20 A’a, ina nufin akan miƙa hadayun da masu bautar gumaka suka wa aljanu ne, ba Allah ba. Ba na so ku zama ɗaya da aljanu.
αλλ' ότι εκείνα, τα οποία θυσιάζουσι τα έθνη, εις τα δαιμόνια θυσιάζουσι και ουχί εις τον Θεόν· και δεν θέλω σεις να γίνησθε κοινωνοί των δαιμονίων.
21 Ba zai yiwu ku sha daga kwaf na Ubangiji ku kuma sha daga kwaf na aljanu ba, ba ya yiwuwa ku ci a teburin Ubangiji, ku kuma ci a teburin aljanu.
Δεν δύνασθε να πίνητε το ποτήριον του Κυρίου και το ποτήριον των δαιμονίων· δεν δύνασθε να ήσθε μέτοχοι της τραπέζης του Κυρίου και της τραπέζης των δαιμονίων.
22 Ashe, so muke mu tsokani Ubangiji ya yi kishi? Mun fi shi ƙarfi ne?
Η τον Κύριον θέλομεν να διεγείρωμεν εις ζηλοτυπίαν; μήπως είμεθα ισχυρότεροι αυτού;
23 “Ana da dama a yi kome” sai dai ba kome ba ne yake da amfani. “Ana da dama a yi kome” sai dai ba kome ba ne mai ginawa.
Πάντα είναι εις την εξουσίαν μου αλλά πάντα δεν συμφέρουσι· πάντα είναι εις την εξουσίαν μου, αλλά πάντα δεν οικοδομούσι.
24 Kada wani yă kula da kansa kawai, sai dai yă kula da waɗansu kuma.
Μηδείς ας ζητή το εαυτού συμφέρον, αλλ' έκαστος τα του άλλου.
25 Ku ci kowane abin da ake sayarwa a kasuwar nama ba sai kun tambaya ba don kada lamiri yă damu da inda abin ya fito,
Παν το πωλούμενον εν τω μακελλίω τρώγετε, μηδέν εξετάζοντες διά την συνείδησιν·
26 gama “Duniya da duk abin da yake cikinta na Ubangiji ne.”
διότι του Κυρίου είναι η γη και το πλήρωμα αυτής.
27 In wani marar bi ya gayyace ku cin abinci kuka kuwa yarda ku je, sai ku ci ko mene ne da aka sa a gabanku, ba tare da tambaya don kada lamiri yă damu da inda abin ya fito.
Και εάν τις των απίστων σας προσκαλή και θέλετε να υπάγητε, τρώγετε ό, τι βάλλεται έμπροσθέν σας, μηδέν εξετάζοντες διά την συνείδησιν.
28 Sai dai in wani ya ce muku, “Ai, wannan an miƙa ne wa gunki,” to, kada ku ci, saboda duban mutuncin wannan da ya gaya muku, don kuma lamiri yă kasance babu laifi
Εάν δε τις σας είπη, Τούτο είναι ειδωλόθυτον, μη τρώγετε δι' εκείνον τον φανερώσαντα και διά την συνείδησιν· διότι του Κυρίου είναι η γη και το πλήρωμα αυτής.
29 ina nufin lamirin wancan mutum ne fa, ba naku ba. Don me lamirin wani zai shari’anta’yancina?
Συνείδησιν δε λέγω ουχί την ιδικήν σου, αλλά την του άλλου. Επειδή διά τι η ελευθερία μου κρίνεται υπό άλλης συνειδήσεως;
30 In na ci abinci da godiya, don me za a zarge ni a kan abin da na ci da godiya ga Allah?
Και εάν εγώ μετ' ευχαριστίας μετέχω, διά τι βλασφημούμαι δι' εκείνο, διά το οποίον εγώ ευχαριστώ;
31 Saboda haka, duk abin da kuke yi, ko ci ko sha, ku yi shi duka saboda ɗaukakar Allah.
Είτε λοιπόν τρώγετε είτε πίνετε είτε πράττετέ τι, πάντα πράττετε εις δόξαν Θεού.
32 Kada ku sa wani yă yi tuntuɓe, ko mutumin Yahuda ne, ko mutumin Al’ummai ko kuma ikkilisiyar Allah
Μη γίνεσθε πρόσκομμα μήτε εις Ιουδαίους μήτε εις Έλληνας μήτε εις την εκκλησίαν του Θεού,
33 kamar dai yadda nake ƙoƙarin faranta wa kowa rai, ta kowace hanya. Gama ba don kaina kaɗai nake yi ba, sai dai don amfanin mutane da yawa, don su sami ceto.
καθώς και εγώ κατά πάντα αρέσκω εις πάντας, μη ζητών το ιδικόν μου συμφέρον, αλλά το των πολλών, διά να σωθώσι

< 1 Korintiyawa 10 >