< 1 Korintiyawa 10 >

1 Ba na so ku kasance da rashin sani,’yan’uwa, cewa dukan kakannin-kakanninmu sun yi tafiya a ƙarƙashin girgije, dukansu kuma suka bi ta tsakiyar teku.
For I would not have you ignorant, brethren, that all our fathers were under the cloud, and all passed through the sea,
2 An yi wa dukansu baftisma ga bin Musa a cikin girgije da kuma cikin teku.
and were all baptized to Moses in the cloud and in the sea,
3 Dukansu sun ci abincin ruhaniya guda
and all ate the same spiritual food,
4 suka kuma sha ruwan ruhaniyan nan guda; gama sun sha daga dutsen ruhaniya nan, wanda ya yi tafiya tare da su, wannan dutsen kuwa Kiristi ne.
and all drank the same spiritual drink; for they drank of the spiritual rock that accompanied them; and the rock was Christ;
5 Duk da haka, Allah bai ji daɗin yawancinsu ba; gawawwakinsu kuwa suka bazu ko’ina a cikin hamada.
but with most of them God was not well pleased; for they were laid low in the wilderness.
6 To, waɗannan abubuwa misalai ne a gare mu, kada mu yi marmarin mugayen abubuwa, kamar yadda suka yi.
Now these things were warnings for us, in order that we should not lust after evil things, as they lusted.
7 Kada ku zama masu bautar gumaka, yadda waɗansunsu suka zama; kamar yadda yake a rubuce cewa, “Mutanen suka zauna don su ci su kuma sha, suka kuma tashi suka shiga rawa ta rashin kunya.”
And do not ye become idolaters, as some of them did; as it is written: “The people sat down to eat and drink, and rose up to sport.”
8 Kada fa mu yi fasikanci yadda waɗansunsu suka yi, har a rana guda mutane dubu ashirin da uku a cikinsu suka mutu.
Nor let us commit fornication, as some of them did, and fell in one day three and twenty thousand.
9 Kada mu gwada Kiristi yadda waɗansunsu suka yi, har macizai suka kakkashe su.
Nor let us tempt Christ, as some of them tempted, and were destroyed by the serpents.
10 Kada kuma ku yi gunaguni yadda waɗansunsu suka yi, har mala’ika mai hallakarwa ya hallaka su.
And do not ye murmur, as some of them murmured, and perished by the Destroyer.
11 Waɗannnan abubuwa sun same su ne, domin su zama abubuwan koyi, aka kuma rubuta su domin a gargaɗe mu, mu da ƙarshen zamani ya zo mana. (aiōn g165)
Now these things happened to them as warnings, and were recorded for our admonition, to whom the ends of the ages have come. (aiōn g165)
12 Saboda haka in kana tsammani kana tsaye ne, to, ka yi hankali kada ka fāɗi!
Wherefore let him that thinketh he standeth, take heed lest he fall.
13 Ba jarrabar da ta taɓa samunku, wadda ba a saba yi wa mutum ba. Allah mai aminci ne; ba zai bari a jarrabce ku fiye da ƙarfinku ba. Amma in aka jarrabce ku, zai nuna muku mafita, domin ku iya cin nasara.
No temptation hath come upon you, but such as is common to man; but God is faithful, who will not suffer you to be tempted beyond what ye are able to endure, but will with the temptation furnish also the way to escape, that ye may be able to endure it.
14 Saboda haka abokaina ƙaunatattu, ku guje wa bautar gumaka.
Wherefore, my beloved, flee from idolatry.
15 Ina magana da ku a kan ku mutane ne fa masu azanci; ku duba da kanku ku ga abin da nake faɗa.
I speak as to wise men, judge ye what I say.
16 Kwaf nan na godiya da muke yin godiya da shi, ashe ba tarayya ce a cikin jinin Kiristi ba? Wannan burodi kuma da muke karya mu ci, ashe, ba tarayya ne a cikin jikin Kiristi ba?
The cup of blessing which we bless, is it not a partaking of the blood of Christ? the loaf which we break, is it not a partaking of the body of Christ?
17 Da yake burodin nan ɗaya ne, ashe kuwa, mu da muke da yawa jiki ɗaya ne, gama dukanmu muna ci daga burodi nan guda.
For we, the many, are one loaf, one body; for we all share in that one loaf.
18 Ku dubi mutanen Isra’ila mana. Ashe, waɗanda suke cin hadayu, ba ɗaya suke da juna cikin cin hadayun da aka miƙa a bagade ba?
Look at Israel by natural descent. Have not those who eat of the sacrifices, communion with the altar?
19 To, me kuke tsammani nake nufi a nan? Hadayar da aka miƙa wa gunki ce wani abu, ko kuma gunkin ne wani abu?
What do I say then? That what is offered in sacrifice to idols is anything? Or that an idol is anything?
20 A’a, ina nufin akan miƙa hadayun da masu bautar gumaka suka wa aljanu ne, ba Allah ba. Ba na so ku zama ɗaya da aljanu.
Nay, but that what they sacrifice, they sacrifice to demons, and not to God; and I would not that ye should have communion with demons.
21 Ba zai yiwu ku sha daga kwaf na Ubangiji ku kuma sha daga kwaf na aljanu ba, ba ya yiwuwa ku ci a teburin Ubangiji, ku kuma ci a teburin aljanu.
Ye cannot drink the cup of the Lord, and the cup of demons; ye cannot be partakers of the Lord's table, and the table of demons.
22 Ashe, so muke mu tsokani Ubangiji ya yi kishi? Mun fi shi ƙarfi ne?
Shall we provoke the Lord to jealousy? Are we stronger than he?
23 “Ana da dama a yi kome” sai dai ba kome ba ne yake da amfani. “Ana da dama a yi kome” sai dai ba kome ba ne mai ginawa.
All things are lawful, but all things are not profitable; all things are lawful, but all things are not edifying.
24 Kada wani yă kula da kansa kawai, sai dai yă kula da waɗansu kuma.
Let no one seek his own pleasure, but the good of others.
25 Ku ci kowane abin da ake sayarwa a kasuwar nama ba sai kun tambaya ba don kada lamiri yă damu da inda abin ya fito,
Whatever is sold in the market that eat, without asking questions for the sake of conscience;
26 gama “Duniya da duk abin da yake cikinta na Ubangiji ne.”
for “the earth is the Lord's, and the fullness thereof.”
27 In wani marar bi ya gayyace ku cin abinci kuka kuwa yarda ku je, sai ku ci ko mene ne da aka sa a gabanku, ba tare da tambaya don kada lamiri yă damu da inda abin ya fito.
And if one who is an unbeliever inviteth you to a feast, and ye choose to go, eat whatever is set before you, without asking any questions for the sake of conscience.
28 Sai dai in wani ya ce muku, “Ai, wannan an miƙa ne wa gunki,” to, kada ku ci, saboda duban mutuncin wannan da ya gaya muku, don kuma lamiri yă kasance babu laifi
But if any one say to you, This hath been offered in sacrifice to an idol, do not eat of it, on account of him that showed you this, and from a regard to conscience;
29 ina nufin lamirin wancan mutum ne fa, ba naku ba. Don me lamirin wani zai shari’anta’yancina?
conscience I mean, not thine own, but that of the other. For why is my liberty to be judged by another conscience [[than my own]]?
30 In na ci abinci da godiya, don me za a zarge ni a kan abin da na ci da godiya ga Allah?
If I partake with thankfulness, why am I to be evil spoken of in a matter for which I give thanks?
31 Saboda haka, duk abin da kuke yi, ko ci ko sha, ku yi shi duka saboda ɗaukakar Allah.
Whether therefore ye eat or drink, or whatever ye do, do all to the glory of God.
32 Kada ku sa wani yă yi tuntuɓe, ko mutumin Yahuda ne, ko mutumin Al’ummai ko kuma ikkilisiyar Allah
Give no occasion of stumbling either to Jews or Greeks, or to the church of God;
33 kamar dai yadda nake ƙoƙarin faranta wa kowa rai, ta kowace hanya. Gama ba don kaina kaɗai nake yi ba, sai dai don amfanin mutane da yawa, don su sami ceto.
as I also strive to please all in all things, not seeking my own advantage, but that of the many; that they may be saved.

< 1 Korintiyawa 10 >