< 1 Korintiyawa 1 >

1 Bulus, wanda aka kira domin yă zama manzon Kiristi Yesu, bisa ga nufin Allah, da kuma ɗan’uwanmu Sostenes,
Paul, called to be an apostle of Jesus Christ by the will of God, and Sosthenes our brother,
2 Zuwa ga ikkilisiyar Allah da take a Korint, da waɗanda aka tsarkake cikin Kiristi Yesu, aka kuma kira domin su zama masu tsarki, tare da dukan waɗanda suke ko’ina da suke kiran sunan Ubangijinmu Yesu Kiristi, Ubangijinsu da kuma namu.
to the church of God in Corinth, to those who are sanctified in Christ Jesus and called to be saints, together with all who in every place call upon the name of our Lord Jesus Christ, both their Lord and ours:
3 Alheri da salama daga Allah Ubanmu, da Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
Grace to you and peace from God our Father and the Lord Jesus Christ.
4 Ina gode wa Allah kullum dominku, saboda alherinsa da aka ba ku a cikin Kiristi Yesu.
I always give thanks to my God for you because of the grace of God that has been given to you in Christ Jesus.
5 Gama a cikinsa kuka sami wadata ta kowace hanya, a cikin dukan maganarku, da kuma cikin dukan saninku
For you have been enriched in him in every way, in all speech and all knowledge,
6 gama shaidarmu game da Kiristi ta tabbata a cikinku.
just as the testimony of Christ was confirmed among you,
7 Saboda haka, ba ku rasa kowace baiwa ta ruhaniya ba, yayinda kuke jira da marmari, saboda bayyanuwar Ubangijinmu Yesu Kiristi.
so that you are not lacking in any gift as you eagerly await the revelation of our Lord Jesus Christ.
8 Zai ƙarfafa ku har zuwa ƙarshe, domin ku zama marasa aibi a ranar Ubangijinmu Yesu Kiristi.
He will strengthen you to the end, so that you will be blameless on the day of our Lord Jesus Christ.
9 Allah, wanda ya kira ku zuwa ga zumunci tare da Ɗansa Yesu Kiristi Ubangijinmu, shi mai aminci ne.
God is faithful, by whom you were called into the fellowship of his Son, Jesus Christ our Lord.
10 Ina roƙonku’yan’uwa, a cikin sunan Ubangijinmu Yesu Kiristi, dukanku ku yarda da juna, domin kada a sami tsattsaguwa a cikinku, domin kuma ku zama ɗaya, cikakku a cikin halinku da tunaninku.
Now I urge you, brothers, in the name of our Lord Jesus Christ, that you all agree in what you say and that there be no divisions among you, but that you be knit together in the same mind and in the same purpose.
11 ’Yan’uwana, waɗansu daga iyalin gidan Kulos sun gaya mini cewa, akwai faɗa a cikinku.
For it has been disclosed to me about you, my brothers, by those of Chloe's household, that there are quarrels among you.
12 Abin da nake nufi shi ne, ɗaya daga cikinku na cewa, “Ni ina bin Bulus,” wani na cewa, “Ni ina bin Afollos,” wani kuma, “Ni ina bin Kefas,” har wa yau wani kuma, “Ni ina bin Kiristi.”
What I mean is this: One of you says, “I follow Paul,” while another says, “I follow Apollos,” or, “I follow Cephas,” or, “I follow Christ.”
13 Kiristi a rabe ne? Bulus ne aka gicciye dominku? An yi muku baftisma a cikin sunan Bulus ne?
Has Christ been divided? Was Paul crucified for you, or were you baptized into the name of Paul?
14 Ina godiya domin ban yi wa wani baftisma a cikinku ba, sai dai Kirisbus da Gayus kaɗai.
I give thanks to God that I baptized none of you, except Crispus and Gaius,
15 Don haka, ba wanda na iya cewa an yi muku baftisma a cikin sunana.
so that no one may say that I baptized into my own name.
16 (I, na kuma yi wa iyalin gidan Istifanas baftisma, ban da wannan, ban tuna da wani da na yi masa baftisma ba.)
(I also baptized the household of Stephanas. Beyond that, I do not recall if I baptized anyone else.)
17 Gama Kiristi bai aike ni yin baftisma ba, sai dai wa’azin bishara ba da kalmomin hikimar mutum ba, domin kada gicciyen Kiristi ya rasa ikonsa.
For Christ did not send me to baptize, but to preach the gospel, and not with cleverness of speech, so that the cross of Christ would not be deprived of its power.
18 Gama saƙon gicciye wauta ne ga waɗanda suke hallaka, amma a gare mu, mu da ake ceto, ikon Allah ne.
For the message of the cross is foolishness to those who are perishing, but to us who are being saved it is the power of God.
19 Gama a rubuce yake cewa, “Zan rushe hikimar mai hikima, basirar mai azanci kuma zan rikita shi.”
For it is written, “I will destroy the wisdom of the wise, and the intelligence of the intelligent I will nullify.”
20 Ina mai hikima? Ina mai zurfin bincike? Ina masana na wannan zamani? Ashe, Allah bai wofinta hikimar duniya ba? (aiōn g165)
Where is the wise man? Where is the scribe? Where is the debater of this age? Has not God made the wisdom of this world foolish? (aiōn g165)
21 Gama tun da a cikin hikimar Allah, duniya a cikin hikimarta ba tă san shi ba, Allah ya ji daɗin ceton waɗanda suka ba da gaskiya ta wurin wautar wa’azin bishara.
For since, in the wisdom of God, the world through its wisdom did not know God, it pleased God through the foolishness of our proclamation to save those who believe.
22 Yahudawa suna so su ga alama, Hellenawa kuma suna neman hikima,
For Jews ask for a sign and Greeks seek wisdom,
23 amma mu, muna wa’azin Kiristi wanda aka gicciye ne, wanda ya zama dutsen tuntuɓe ga Yahudawa, wauta kuma ga Al’ummai,
but we preach Christ crucified, a stumbling block to Jews and foolishness to Greeks,
24 amma ga su waɗanda Allah ya kira, Yahudawa da Hellenawa, Kiristi ikon Allah ne, da kuma hikimar Allah.
but to those who are called, both Jews and Greeks, Christ is the power of God and the wisdom of God.
25 Gama wautar Allah ta fi hikimar mutum, kuma rashin ƙarfin Allah ya fi ƙarfin mutum.
For the foolishness of God is wiser than men, and the weakness of God is stronger than men.
26 ’Yan’uwa, ku tuna yadda kuke sa’ad da aka kira ku. Babu masu hikima da yawa a cikinku, bisa ga ganin mutum; babu masu iko da yawa, babu masu martaba da yawa bisa ga haihuwa.
Consider your calling, brothers, that not many of you were wise according to the flesh, not many were powerful, not many were of noble birth.
27 Amma Allah ya zaɓi abubuwa masu wautata duniya, don yă kunyata masu hikima. Allah ya zaɓi abubuwa marasa ƙarfi na duniya, domin ya ba wa masu ƙarfi kunya.
But God chose the foolish things of the world to shame the wise, and God chose the weak things of the world to shame the strong.
28 Ya zaɓi abubuwa marasa martaba na wannan duniya da kuma abubuwan da aka rena da abubuwan da ba a ɗauka a bakin kome ba, domin a wofinta abubuwan da ake ganinsu da daraja,
God chose what is lowly and despised in the world, things that are regarded as nothing, to nullify the things that are regarded as something,
29 domin kada wani ya yi taƙama a gabansa.
so that no flesh might boast before God.
30 Saboda Allah ne kuke cikin Kiristi Yesu, shi wanda ya zama hikima a gare mu daga Allah. Kiristi shi ne adalcinmu, da tsarkinmu, da kuma fansarmu.
It is because of him that you are in Christ Jesus, who has become for us wisdom from God, and in whom we have righteousness, sanctification, and redemption.
31 Saboda haka, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Duk wanda yake taƙama, ya yi taƙama a cikin Ubangiji.”
Therefore, as it is written, “Let him who boasts, boast in the Lord.”

< 1 Korintiyawa 1 >