< 1 Tarihi 9 >

1 Haka aka lissafta dukan Isra’ila a tarihin zuriyoyi a littafin sarakunan Isra’ila. Aka kwasa mutanen Yahuda zuwa zaman bauta a Babilon domin rashin aminci.
Tout Israël fut donc dénombré, et leur nombre total écrit dans le Livre des rois d’Israël et de Juda; et ils furent transportés à Babylone à cause de leur péché.
2 To, na farkon da aka sāke zaunar da su a mallakarsu a garuruwansu, su ne waɗansu Isra’ilawa, firistoci, Lawiyawa da kuma masu hidimar haikali.
Or ceux qui habitèrent les premiers dans leurs possessions et dans leurs villes furent Israël, les prêtres, les Lévites et les Nathinéens.
3 Waɗanda suke daga Yahuda, daga Benyamin, da kuma daga Efraim da Manasse waɗanda suka zauna a Urushalima su ne,
Il demeura à Jérusalem des enfants de Juda et des enfants de Benjamin, et même des enfants d’Ephraïm et de Manassé:
4 Uttai ɗan Ammihud, ɗan Omri, ɗan Imri, ɗan Bani, zuriyar Ferez ɗan Yahuda.
Othéi, fils d’Ammiud, fils d’Amri, fils d’Omraï, fils de Bonni, l’un des fils de Pharès, fils de Juda;
5 Na mutanen Shilo kuwa su ne, Asahiya ɗan fari da’ya’yansa maza.
Et de Siloni: Asaïa, le premier-né, et ses autres fils;
6 Na mutanen Zera su ne, Yewuyel. Mutane daga Yahuda sun kai 690.
Mais des fils de Zara: Jéhuel et leurs frères, au nombre de six cent quatre-vingt-dix;
7 Na Benyamin su ne, Sallu ɗan Meshullam, ɗan Hodawiya, ɗan Hassenuwa;
Et des fils de Benjamin: Salo, fils de Mosollam, fils d’Oduïa, fils d’Asana;
8 Ibnehiya ɗan Yeroham; Ela ɗan Uzzi, ɗan Mikri; da Meshullam ɗan Shefatiya, ɗan Reyuwel, ɗan Ibniya.
Et Jobania, fils de Jéroham, et Ela, fils d’Ozi. fils de Mochori; et Mosollam, fils de Saphatias, fils de Rahuel, fils de Jébanias,
9 Mutane daga Benyamin, kamar yadda aka lissafta zuriyarsu, sun kai 956. Dukan waɗannan mutane kawunan iyalansu ne.
Et leurs frères, selon leurs familles, au nombre de neuf cent cinquante-six. Tous ceux-là furent princes de familles, dans les maisons de leurs pères.
10 Na firistoci su ne, Yedahiya; Yehoyarib; Yakin;
Mais d’entre les prêtres, il y eut Jédaïa, Joïarib et Jachin;
11 Azariya ɗan Hilkiya, ɗan Meshullam, ɗan Zadok, ɗan Merahiyot, ɗan Ahitub, shugaban da yake lura da gidan Allah;
Azarias aussi, fils d’Helcias, fils de Mosollam, fils de Sadoc, fils de Maraïoth, fils d’Achitob, pontife de la maison de Dieu.
12 Adahiya ɗan Yeroham, ɗan Fashhur, ɗan Malkiya; da Ma’asai ɗan Adiyel, ɗan Yazera, ɗan Meshullam, ɗan Meshillemit, ɗan Immer.
De plus, Adaïas, fils de Jéroham, fils de Phassur, fils de Melchias; et Maasaï, fils d’Adiel, fils de Jezra, fils de Mosollam, fils de Mosollamith. fils d’Emmer;
13 Firistocin da suke kawunan iyalai, sun kai 1,760. Dukansu ƙwararru ne, masu hakkin hidima a cikin gidan Allah.
Ainsi que leurs frères, princes dans leurs familles, au nombre de mille sept cent soixante, d’une très grande force pour faire l’ouvrage du ministère dans la maison de Dieu.
14 Na Lawiyawa su ne, Shemahiya ɗan Hasshub, ɗan Azrikam, ɗan Hashabiya, mutumin Merari;
Et d’entre les Lévites, il y eut Séméia, fils d’Hassub, fils d’Ezricam, fils d’Hasébia, l’un des fils de Mérari;
15 Bakbakkar, Heresh, Galal da Mattaniya ɗan Mika, ɗan Zikri, ɗan Asaf;
Bacbachar aussi, charpentier, Galal, et Mathania, fils de Micha, fils de Zéchri, fils d’Asaph;
16 Obadiya ɗan Shemahiya, ɗan Galal, ɗan Yedutun; da Berekiya ɗan Asa, ɗan Elkana, wanda ya zauna a ƙauyukan Netofawa.
Et Obdia, fils de Séméias, fils de Galal, fils d’Idithun; et Barachia, fils d’Asa, fils d’Elcana, qui habita dans les villages de Nétophati.
17 Matsaran ƙofofi su ne, Shallum, Akkub, Talmon, Ahiman da’yan’uwansu. Shallum ne babbansu
Quant aux portiers, c’étaient Sellum, Accub, Telmon et Ahimam; et leur frère Sellum était leur chef.
18 da aka ajiye a Ƙofar Sarki a gabas, har zuwa wannan lokaci. Waɗannan su ne matsaran ƙofofi na sansanin Lawiyawa.
Jusqu’à ce temps-là, à la porte du roi, vers l’orient, des fils de Lévi faisaient la garde tour à tour.
19 Shallum ɗan Kore, ɗan Ebiyasaf, ɗan Kora, da’yan’uwansa matsaran ƙofofi daga iyalin (mutanen Kohat) su suke da hakkin tsaron madogaran ƙofar Tenti kamar dai yadda kakanninsu suka kasance da hakkin tsaron mashigin mazaunin Ubangiji.
Or Sellum, fils de Coré, fils d’Abiasaph, fils de Coré, avec ses frères et la maison de son père, c’est-à-dire les Corites préposés aux ouvrages du ministère, étaient les gardiens des vestibules du tabernacle; et leurs familles gardaient tour à tour l’entrée du camp du Seigneur.
20 A dā Finehas ɗan Eleyazar ne yake lura da matsaran, kuma Ubangiji ya kasance tare da shi.
Or Phinéès, fils d’Eléazar, était leur chef devant le Seigneur.
21 Zakariya ɗan Meshelemiya shi ne mai tsaro a mashigin Tentin Sujada.
Et Zacharie, fils de Mosollamia, était portier à la porte du tabernacle de témoignage.
22 Duka-duka, waɗanda aka zaɓa don su zama matsaran madogaran ƙofa sun kai 212. Aka rubuta su zuriya-zuriya a ƙauyukansu. Dawuda da Sama’ila mai duba ne suka sa matsaran a wurarensu na aminci.
Tous ceux-là, choisis pour portiers aux différentes portes, étaient au nombre de deux cent douze, enregistrés dans leurs propres villages: David et Samuel, le Voyant, les établirent à cause de leur fidélité,
23 Su da zuriyarsu, su suke lura da tsaron ƙofofin gidan Ubangiji, gidan da ake kira Tenti.
Tant eux que leurs fils, pour veiller à leur tour aux portes de la maison du Seigneur et du tabernacle.
24 Matsaran suna a kusurwoyi huɗu, gabas, yamma, arewa da kudu.
Les portiers étaient vers les quatre vents, c’est-à-dire à l’orient, à l’occident, à l’aquilon et au midi.
25 ’Yan’uwansu a ƙauyukansu sukan zo lokaci, lokaci su yi ayyukansu kwana bakwai, bakwai.
Et leurs frères demeuraient dans leurs bourgades, et ils venaient en leurs sabbats depuis un temps jusqu’à un temps.
26 Amma manyan matsara huɗu, waɗanda suke Lawiyawa, an danƙa musu hakkin lura da ɗakuna da kuma wuraren ajiya a gidan Allah.
C’est à ces quatre Lévites que fut confié le nombre entier des portiers; et ils veillaient sur les chambres et sur les trésors de la maison du Seigneur.
27 Sukan kwana a kewayen gidan Allah, domin dole su tsare shi; kuma su suke lura da mabuɗi don buɗewa a kowace safiya.
Ils demeuraient même autour du temple du Seigneur, pendant leur garde, afin que, lorsque le temps était venu, ils ouvrissent eux-mêmes les portes le matin.
28 Waɗansunsu su ne suke lura da kayayyakin da ake amfani da su a hidimar haikali; sukan ƙirga su sa’ad da ake shigar da su da sa’ad da ake fitar da su.
À leur classe appartenaient aussi ceux qui étaient chargés des vases servant au culte; car c’était en certain nombre qu’étaient apportés les vases et qu’ils étaient remportés.
29 An sa waɗansu su lura da kayayyakin da kuma dukan waɗansu kayan wuri mai tsarki, da kuma gari da ruwan inabi, da mai, turare da kuma kayan yaji.
Parmi eux encore se trouvaient ceux qui, ayant la garde des ustensiles du sanctuaire, prenaient soin de la fleur de farine, du vin, de l’huile, de l’encens et des aromates.
30 Amma waɗansu firistoci ne suke harhaɗa kayan yajin.
Mais les fils des prêtres composaient les parfums à oindre avec les aromates.
31 Wani Balawe mai suna Mattitiya, ɗan farin Shallum mutumin Kora ne aka danƙa masa hakkin toya burodin miƙawa.
Et Mathathias le Lévite, le premier-né de Sellum, le Corite, était préposé pour ce qu’on faisait frire dans la poêle.
32 Waɗansu’yan’uwansu Kohatawa ne suke lura da shiryawa burodin da ake kaiwa a tebur a kowane Asabbaci.
Or c’est parmi les enfants de Caath, leurs frères, que se trouvaient ceux qui étaient chargés des pains de proposition, afin d’en préparer toujours de nouveaux à chaque sabbat.
33 Waɗanda suke mawaƙa, kawunan iyalan Lawiyawa, sukan zauna a ɗakunan haikali kuma ba sa yin waɗansu ayyuka domin su suke da hakkin aiki dare da rana.
Ce sont là les chefs des chantres parmi les familles des Lévites, qui demeuraient dans les chambres du temple, afin que, jour et nuit, sans interruption, ils remplissent leur ministère.
34 Dukan waɗannan su ne kawunan iyalan Lawiyawa, manya kamar yadda aka lissafta su a zuriyarsu, kuma suna zama a Urushalima.
Les chefs des Lévites, princes dans leurs familles, demeurèrent à Jérusalem.
35 Yehiyel mahaifin Gibeyon ya zauna a Gibeyon. Matarsa ita ce Ma’aka
Mais c’est à Gabaon que s’établirent Jéhiel, dont le nom de la femme était Maacha;
36 ɗansa na fari kuwa shi ne Abdon, sai Zur, Kish, Ba’al, Ner, Nadab,
Son fils premier-né, Abdon, elles autres, Sur, Cis, Baal, Ner et Nadab,
37 Gedor, Ahiyo, Zakariya da Miklot.
Gédor, Ahio, Zacharie et Macelloth.
38 Miklot shi ne mahaifin Shimeyam. Su ma sun zauna kusa da danginsu a Urushalima.
Or Macelloth engendra Samaan; ceux-là habitèrent vis-à-vis de leurs frères, à Jérusalem, avec leurs frères.
39 Ner shi mahaifin Kish, Kish mahaifin Shawulu, kuma Shawulu shi ne mahaifin Yonatan, Malki-Shuwa, Abinadab da Esh-Ba’al.
Mais Ner engendra Cis, et Cis engendra Saül, et Saül engendra Jonathan, et Melchisua, et Abinadab, et Esbaal.
40 Ɗan Yonatan shi ne, Merib-Ba’al wanda shi ne mahaifin Mika.
Et le fils de Jonathan fut Méribbaal; et Méribbaal engendra Micha.
41 ’Ya’yan Mika maza su ne, Fiton, Melek, Tareya da Ahaz.
Or les fils de Micha furent Phithon, Mélech, Tharaa et Ahaz.
42 Ahaz shi ne mahaifin Yada, Yada shi ne mahaifin Alemet, Azmawet da Zimri, Zimri kuwa shi ne mahaifin Moza.
Et Ahaz engendra Jara, et Jara engendra Alamath, Azmoth et Zamri; mais Zamri engendra Mosa.
43 Moza shi ne mahaifin Bineya; Refahiya, Eleyasa da kuma Azel.
Pour Mosa, il engendra Banaa, dont le fils Raphaïa engendra Elasa, de qui est né Asel.
44 Azel yana da’ya’ya maza shida, kuma ga sunayensu. Azrikam, Bokeru, Ishmayel, Sheyariya, Obadiya da Hanan. Waɗannan su ne’ya’yan Azel maza.
Or Asel eut six fils de ces noms: Ezricam, Bocru, Ismaël, Saria, Obdia, Hanan; ce sont là les fils d’Asel.

< 1 Tarihi 9 >