< 1 Tarihi 9 >

1 Haka aka lissafta dukan Isra’ila a tarihin zuriyoyi a littafin sarakunan Isra’ila. Aka kwasa mutanen Yahuda zuwa zaman bauta a Babilon domin rashin aminci.
And all Israel they had themselves enrolled and there they [are] written on [the] scroll of [the] kings of Israel and Judah they were taken into exile to Babylon in unfaithfulness their.
2 To, na farkon da aka sāke zaunar da su a mallakarsu a garuruwansu, su ne waɗansu Isra’ilawa, firistoci, Lawiyawa da kuma masu hidimar haikali.
And the inhabitants first who [were] in possession their in cities their [were] Israel the priests the Levites and the temple servants.
3 Waɗanda suke daga Yahuda, daga Benyamin, da kuma daga Efraim da Manasse waɗanda suka zauna a Urushalima su ne,
And in Jerusalem they dwelt some of [the] descendants of Judah and some of [the] descendants of Benjamin and some of [the] descendants of Ephraim and Manasseh.
4 Uttai ɗan Ammihud, ɗan Omri, ɗan Imri, ɗan Bani, zuriyar Ferez ɗan Yahuda.
Uthai [the] son of Ammihud [the] son of Omri [the] son of Imri [the] son of (Bani from *Q(K)*) [the] descendants of Perez [the] son of Judah.
5 Na mutanen Shilo kuwa su ne, Asahiya ɗan fari da’ya’yansa maza.
And of the Shilonite[s] Asaiah the firstborn and sons his.
6 Na mutanen Zera su ne, Yewuyel. Mutane daga Yahuda sun kai 690.
And of [the] descendants of Zerah Jeuel and relatives their six hundred and ninety.
7 Na Benyamin su ne, Sallu ɗan Meshullam, ɗan Hodawiya, ɗan Hassenuwa;
And of [the] descendants of Benjamin Sallu [the] son of Meshullam [the] son of Hodaviah [the] son of Senaah.
8 Ibnehiya ɗan Yeroham; Ela ɗan Uzzi, ɗan Mikri; da Meshullam ɗan Shefatiya, ɗan Reyuwel, ɗan Ibniya.
And Ibneiah [the] son of Jeroham and Elah [the] son of Uzzi [the] son of Mikri and Meshullam [the] son of Shephatiah [the] son of Reuel [the] son of Ibnijah.
9 Mutane daga Benyamin, kamar yadda aka lissafta zuriyarsu, sun kai 956. Dukan waɗannan mutane kawunan iyalansu ne.
And relatives their to generations their nine hundred and fifty and six all these men [were] chiefs of fathers to [the] house of ancestors their.
10 Na firistoci su ne, Yedahiya; Yehoyarib; Yakin;
And of the priests Jedaiah and Jehoiarib and Jakin.
11 Azariya ɗan Hilkiya, ɗan Meshullam, ɗan Zadok, ɗan Merahiyot, ɗan Ahitub, shugaban da yake lura da gidan Allah;
And Azariah [the] son of Hilkiah [the] son of Meshullam [the] son of Zadok [the] son of Meraioth [the] son of Ahitub [the] leader of [the] house of God.
12 Adahiya ɗan Yeroham, ɗan Fashhur, ɗan Malkiya; da Ma’asai ɗan Adiyel, ɗan Yazera, ɗan Meshullam, ɗan Meshillemit, ɗan Immer.
And Adaiah [the] son of Jeroham [the] son of Pashhur [the] son of Malkijah and Maasai [the] son of Adiel [the] son of Jahzerah [the] son of Meshullam [the] son of Meshillemith [the] son of Immer.
13 Firistocin da suke kawunan iyalai, sun kai 1,760. Dukansu ƙwararru ne, masu hakkin hidima a cikin gidan Allah.
And relatives their chiefs of [the] house of ancestors their one thousand and seven hundred and sixty mighty [men] of ability of [the] work of [the] service of [the] house of God.
14 Na Lawiyawa su ne, Shemahiya ɗan Hasshub, ɗan Azrikam, ɗan Hashabiya, mutumin Merari;
And of the Levites Shemaiah [the] son of Hasshub [the] son of Azrikam [the] son of Hashabiah of [the] descendants of Merari.
15 Bakbakkar, Heresh, Galal da Mattaniya ɗan Mika, ɗan Zikri, ɗan Asaf;
And Bakbakkar Heresh and Galal and Mattaniah [the] son of Mica [the] son of Zikri [the] son of Asaph.
16 Obadiya ɗan Shemahiya, ɗan Galal, ɗan Yedutun; da Berekiya ɗan Asa, ɗan Elkana, wanda ya zauna a ƙauyukan Netofawa.
And Obadiah [the] son of Shemaiah [the] son of Galal [the] son of Jeduthun and Berekiah [the] son of Asa [the] son of Elkanah who dwelt in [the] villages of [the] Netophathite[s].
17 Matsaran ƙofofi su ne, Shallum, Akkub, Talmon, Ahiman da’yan’uwansu. Shallum ne babbansu
And the gatekeepers Shallum and Akkub and Talmon and Ahiman and brother their Shallum [was] the chief.
18 da aka ajiye a Ƙofar Sarki a gabas, har zuwa wannan lokaci. Waɗannan su ne matsaran ƙofofi na sansanin Lawiyawa.
And until now in [the] gate of the king east-ward they [were] the gatekeepers of [the] camps of [the] descendants of Levi.
19 Shallum ɗan Kore, ɗan Ebiyasaf, ɗan Kora, da’yan’uwansa matsaran ƙofofi daga iyalin (mutanen Kohat) su suke da hakkin tsaron madogaran ƙofar Tenti kamar dai yadda kakanninsu suka kasance da hakkin tsaron mashigin mazaunin Ubangiji.
And Shallum [the] son of Kore [the] son of Ebiasaph [the] son of Korah and relatives his of [the] house of father his the Korahites [were] over [the] work of the service [the] keepers of the thresholds of the tent and ancestors their [had been] over [the] camp of Yahweh [the] keepers of the entrance.
20 A dā Finehas ɗan Eleyazar ne yake lura da matsaran, kuma Ubangiji ya kasance tare da shi.
And Phinehas [the] son of Eleazar a leader he had been over them before Yahweh - [was] with him.
21 Zakariya ɗan Meshelemiya shi ne mai tsaro a mashigin Tentin Sujada.
Zechariah [the] son of Meshelemiah [was] a gatekeeper of [the] entrance of [the] tent of meeting.
22 Duka-duka, waɗanda aka zaɓa don su zama matsaran madogaran ƙofa sun kai 212. Aka rubuta su zuriya-zuriya a ƙauyukansu. Dawuda da Sama’ila mai duba ne suka sa matsaran a wurarensu na aminci.
All of them who had been chosen to gatekeepers at the thresholds [were] two hundred and two [plus] ten they [was] in villages their recording genealogy they them he had appointed David and Samuel the seer in faithfulness their.
23 Su da zuriyarsu, su suke lura da tsaron ƙofofin gidan Ubangiji, gidan da ake kira Tenti.
And they and descendants their [were] over the gates of [the] house of Yahweh of [the] house of the tent to guards.
24 Matsaran suna a kusurwoyi huɗu, gabas, yamma, arewa da kudu.
To four sides they were the gatekeepers [the] east west-ward north-ward and south-ward.
25 ’Yan’uwansu a ƙauyukansu sukan zo lokaci, lokaci su yi ayyukansu kwana bakwai, bakwai.
And relatives their in villages their [were] to come for [the] seven the days from time to time with these.
26 Amma manyan matsara huɗu, waɗanda suke Lawiyawa, an danƙa musu hakkin lura da ɗakuna da kuma wuraren ajiya a gidan Allah.
For in faithfulness they [the] four [the] mighty [ones] of the gatekeepers they [were] the Levites and they were over the store-rooms and over the treasuries of [the] house of God.
27 Sukan kwana a kewayen gidan Allah, domin dole su tsare shi; kuma su suke lura da mabuɗi don buɗewa a kowace safiya.
And around [the] house of God they spent [the] night for [was] on them a duty and they [were] over the key and to the morning to the morning.
28 Waɗansunsu su ne suke lura da kayayyakin da ake amfani da su a hidimar haikali; sukan ƙirga su sa’ad da ake shigar da su da sa’ad da ake fitar da su.
And some of them [were] over [the] articles of the service for by number they brought them and by number they took out them.
29 An sa waɗansu su lura da kayayyakin da kuma dukan waɗansu kayan wuri mai tsarki, da kuma gari da ruwan inabi, da mai, turare da kuma kayan yaji.
And some of them [were] appointed over the articles and over all [the] articles of the holy place and over the fine flour and the wine and the oil and the frankincense and the spices.
30 Amma waɗansu firistoci ne suke harhaɗa kayan yajin.
And some of [the] sons of the priests [were those who] mixed the mixture of the spices.
31 Wani Balawe mai suna Mattitiya, ɗan farin Shallum mutumin Kora ne aka danƙa masa hakkin toya burodin miƙawa.
And Mattithiah one of the Levites he [was] the firstborn of Shallum the Korahite in faithfulness [was] over [the] work of the flat cakes.
32 Waɗansu’yan’uwansu Kohatawa ne suke lura da shiryawa burodin da ake kaiwa a tebur a kowane Asabbaci.
And some of [the] sons of the Kohathite[s] some of relatives their [were] over [the] bread of the row to prepare [it] sabbath sabbath.
33 Waɗanda suke mawaƙa, kawunan iyalan Lawiyawa, sukan zauna a ɗakunan haikali kuma ba sa yin waɗansu ayyuka domin su suke da hakkin aiki dare da rana.
And these the singers [the] chiefs of fathers of the Levites [were] in the rooms (set free *Q(K)*) for by day and night [was] on them in the work.
34 Dukan waɗannan su ne kawunan iyalan Lawiyawa, manya kamar yadda aka lissafta su a zuriyarsu, kuma suna zama a Urushalima.
These [were] [the] chiefs of the fathers of the Levites to generations their chiefs these they dwelt in Jerusalem.
35 Yehiyel mahaifin Gibeyon ya zauna a Gibeyon. Matarsa ita ce Ma’aka
And in Gibeon they dwelt [the] father of Gibeon (Jeiel *Q(K)*) and [the] name of wife his [was] Maacah.
36 ɗansa na fari kuwa shi ne Abdon, sai Zur, Kish, Ba’al, Ner, Nadab,
And son his the firstborn [was] Abdon and Zur and Kish and Baal and Ner and Nadab.
37 Gedor, Ahiyo, Zakariya da Miklot.
And Gedor and Ahio and Zechariah and Mikloth.
38 Miklot shi ne mahaifin Shimeyam. Su ma sun zauna kusa da danginsu a Urushalima.
And Mikloth he fathered Shimeam and also they before relatives their they dwelt in Jerusalem with relatives their.
39 Ner shi mahaifin Kish, Kish mahaifin Shawulu, kuma Shawulu shi ne mahaifin Yonatan, Malki-Shuwa, Abinadab da Esh-Ba’al.
And Ner he fathered Kish and Kish he fathered Saul and Saul he fathered Jonathan and Malki-Shua and Abinadab and Eshbaal.
40 Ɗan Yonatan shi ne, Merib-Ba’al wanda shi ne mahaifin Mika.
And [the] son of Jonathan [was] Merib-baal and Meri-baal he fathered Micah.
41 ’Ya’yan Mika maza su ne, Fiton, Melek, Tareya da Ahaz.
And [the] sons of Micah Pithon and Melech and Tahrea. (And Ahaz. *X*)
42 Ahaz shi ne mahaifin Yada, Yada shi ne mahaifin Alemet, Azmawet da Zimri, Zimri kuwa shi ne mahaifin Moza.
And Ahaz he fathered Jarah and Jarah he fathered Alemeth and Azmaveth and Zimri and Zimri he fathered Moza.
43 Moza shi ne mahaifin Bineya; Refahiya, Eleyasa da kuma Azel.
And Moza he fathered Binea and Rephaiah son his Eleasah son his Azel son his.
44 Azel yana da’ya’ya maza shida, kuma ga sunayensu. Azrikam, Bokeru, Ishmayel, Sheyariya, Obadiya da Hanan. Waɗannan su ne’ya’yan Azel maza.
And [belonged] to Azel six sons and these [are] names their Azrikam - Bocheru and Ishmael and Sheariah and Obadiah and Hanan these [were] [the] sons of Azel.

< 1 Tarihi 9 >