< 1 Tarihi 5 >

1 ’Ya’yan Ruben maza ɗan farin Isra’ila (shi ne ɗan fari, amma sa’ad da ya ƙazantar da gadon auren mahaifinsa, sai aka ba wa’yancin ɗan farinsa wa’ya’yan Yusuf maza ɗan Isra’ila; don kada a lissafta shi a tarihin zuriya bisa ga matsayin haihuwarsa,
Voici les fils de Ruben, premier-né d’Israël (car c’est lui qui était son premier-né; mais lorsqu’il eut violé le lit nuptial de son père, son droit d’aînesse fut donné aux fils de Joseph, fils d’Israël; et Ruben ne fut plus réputé premier-né.
2 ko da yake Yahuda shi ne mafi ƙarfi cikin’yan’uwansa kuma mai mulki ya fito daga gare shi,’yancin zaman ɗan fari na Yusuf ne),
Quant à Juda, qui était le plus vaillant parmi ses frères, des princes ont germé de son tronc; mais le droit d’aînesse fut attribué à Joseph).
3 ’ya’yan Ruben ɗan farin Isra’ila maza su ne, Hanok, Fallu, Hezron da Karmi.
Voici donc les fils de Ruben, premier-né d’Israël: Enoch et Phallu, Esron et Carmi.
4 Zuriyar Yowel su ne, Shemahiya, Gog, Shimeyi,
Les fils de Joël: Samaïa, dont le fils, Gog, dont le fils, Séméi,
5 Mika, Reyahiya, Ba’al,
Dont le fils, Micha, dont le fils, Réia, dont le fils, Baal,
6 da Beyera, wanda Tiglat-Fileser sarkin Assuriya ya ɗauka zuwa zaman bauta. Beyera shi ne shugaban mutanen Ruben.
Dont le fils, Bééra, que Thelgathphalnasar, roi des Assyriens, emmena captif, et qui fut prince dans la tribu de Ruben.
7 Danginsu bisa ga iyalansu da aka jera bisa ga tarihin zuriyarsu su ne, Yehiyel shi ne sarki, akwai Zakariya,
Mais ses frères et toute sa parenté, quand ils furent dénombrés, avaient pour chefs Jéhiel et Zacharie.
8 da Bela ɗan Azaz. Azaz ɗan Shema daga dangin Yowel. Yowel ya yi zama a yankin Arower har zuwa Nebo da Ba’al-Meyon.
Or Bala, fils d’Azaz, fils de Samma, fils de Joël, habita lui-même à Aroër, jusqu’à Nébo et Béelméon.
9 Ta waje gabas sun zauna a ƙasar har zuwa bakin hamadan da ya nausa zuwa Kogin Yuferites, domin dabbobinsu sun ƙaru a Gileyad.
Il habita aussi contre le côté oriental jusqu’à l’entrée du désert et jusqu’au fleuve d’Euphrate; car ils possédaient un grand nombre de bestiaux dans la terre de Galaad.
10 A zamanin Shawulu zuriyar Ruben sun yi yaƙi da Hagirawa, suka ci su da yaƙi, suka zauna a wuraren zaman Hagirawan ko’ina a dukan yankin gabashin Gileyad.
Mais, dans les jours de Saül, ils combattirent contre les Agaréens, les tuèrent et habitèrent en leur place dans leurs tabernacles, dans toute la contrée qui regarde Galaad.
11 Mutanen Gad sun zauna kusa da mutanen Ruben a Bashan, har zuwa Saleka.
Quant aux enfants de Gad, ils habitèrent vis-à-vis d’eux dans la terre de Basan, jusqu’à Selcha.
12 Yowel shi ne babba, sai Shafan na biyu, sa’an nan Yanai da Shafat, su ne tushen Bashan.
Joël était à la tête, et Saphan, le second; mais Janaï et Saphat dans Basan.
13 Danginsu, bisa ga iyalai su ne, Mika’ilu, Meshullam, Sheba, Yorai, Yakan, Ziya da Eber, su bakwai ne duka.
Et leurs frères, selon les maisons de leur parenté, étaient Michaël, Mosollam, Sébé, Joraï, Jachan, Zié et Héber, sept en tout.
14 Waɗannan su ne’ya’yan Abihayil ɗan Huri, ɗan Yarowa, ɗan Gileyad, ɗan Mika’ilu, ɗan Yeshishai, ɗan Yado, ɗan Buz.
Ceux-ci furent fils d’Abihaïl, fils d’Huri, fils de Jara, fils de Galaad, fils de Michaël, fils de Jésési, fils de Jeddo, fils de Buz.
15 Ahi ɗan Abiyel, ɗan Guni, shi ne kan iyalinsu.
Leurs frères furent encore les fils d’Abdiel, fils de Guni, chacun chef de maison dans ses familles.
16 Mutanen Gad sun zauna a Bashan da ƙauyukan da suke kurkusa da shi, da kuma a dukan makiyayan Sharon har zuwa iyaka inda suka kai.
Et ils habitèrent en Galaad, dans Basan, et ses bourgades, et dans tous les faubourgs de Saron, jusqu’aux limites.
17 Dukan waɗannan sun shiga tarihin zuriya a lokacin mulkin Yotam sarkin Yahuda da Yerobowam sarkin Isra’ila.
Tous ceux-ci furent dénombrés dans les jours de Joathan, roi de Juda, et dans les jours de Jéroboam, roi d’Israël.
18 Mutanen Ruben, mutanen Gad da rabin kabilar Manasse sun kasance da mutane 44,760 shiryayyu don aikin soja, jarumawan da za su iya riƙe garkuwa da takobi, waɗanda suke iya yin amfani da baka, waɗanda kuma aka horar don yaƙi.
Les enfants de Ruben, de Gad, et de la demi-tribu de Manassé, furent des gens de guerre, portant des boucliers et des glaives, tendant l’arc, et formés aux combats, au nombre de quarante-quatre mille sept cent soixante, marchant à la bataille.
19 Suka yi yaƙi da Hagirawa, Yetur, Nafish da Nodab.
Ils combattirent contre les Agaréens; mais les Ituréens, Naphis et Nodab
20 Aka taimake su a yaƙin, Allah kuma ya ba da Hagirawa da dukan abokansu gare su, domin sun yi kuka gare shi a lokacin yaƙin. Ya amsa addu’o’insu, domin sun dogara gare shi.
Leur donnèrent du secours. Et les Agaréens furent livrés entre leurs mains, ainsi que tous ceux qui avaient été avec eux, parce qu’ils invoquèrent Dieu, lorsqu’ils combattaient; et il les exauça, parce qu’ils avaient cru en lui.
21 Suka ƙwace dabbobin Hagirawa, raƙuma dubu hamsin, tumaki dubu ɗari biyu da hamsin da kuma jakuna dubu biyu. Suka kuma kame mutane dubu ɗari ɗaya,
Et ils prirent tout ce que possédaient ces peuples: cinquante mille chameaux, deux cent cinquante mille brebis, deux mille ânes, et cent mille âmes d’hommes.
22 waɗansu suka mutu, domin yaƙin na Allah ne. Suka zauna a ƙasar har lokacin da aka kai su zaman bauta.
De plus, beaucoup de blessés succombèrent: car c’était la guerre du Seigneur. Et ils habitèrent là en leur place jusqu’à la transmigration.
23 Mutanen rabin kabilar Manasse sun yi yawa; suka zauna a ƙasar daga Bashan har zuwa Ba’al-Hermon, wato, zuwa Senir (Dutsen Hermon).
Les enfants de la demi-tribu de Manassé aussi possédèrent le pays depuis les confins de Basan jusqu’à Baal, Hermon et Sanir, et la montagne d’Hermon, parce que leur nombre était grand.
24 Waɗannan su ne kawunan iyalansu. Efer, Ishi, Eliyel, Azriyel, Irmiya, Hodawiya da Yadiyel. Su jarumawa ne, sanannu, su ne kuma kawunan iyalansu.
Et voici les princes de la maison de leur parenté: Epher, Jési, Eliel, Ezriel, Jérémie, Odoïa, et Jédiel, hommes très braves, et puissants, et princes renommés dans leurs familles.
25 Amma ba su yi aminci da Allahn kakanninsu ba, suka kuma yi karuwanci ga waɗansu allolin mutanen ƙasar, waɗanda Allah ya hallaka a gabansu.
Cependant ils abandonnèrent le Dieu de leurs pères, et forniquèrent, en allant après les dieux des peuples de ce pays que Dieu avait détruits devant eux.
26 Saboda haka Allah na Isra’ila ya zuga ruhun Ful sarkin Assuriya (wato, Tiglat-Fileser sarkin Assuriya), wanda ya kwashe mutanen Ruben, mutanen Gad da rabin kabilar Manasse zuwa zaman bauta. Ya kwashe su zuwa Hala, Habor, Hara da kuma kogin Gozan, inda suke har wa yau.
Mais le Dieu d’Israël suscita l’esprit de Phul, roi des Assyriens, et l’esprit de Thelgathphalnasar, roi d’Assur; et il transféra Ruben, Gad et la demi-tribu de Manassé, et les emmena à Lahéla, à Habor, à Ara, et sur le fleuve de Gozan, jusqu’à ce jour.

< 1 Tarihi 5 >